< Ézéchiel 43 >

1 Ensuite, il me conduisit à la porte, à la porte qui regarde l'orient.
Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
2 Et voici, la gloire du Dieu d'Israël vint du côté de l'orient. Sa voix était comme le bruit de grandes eaux, et la terre était illuminée par sa gloire.
sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
3 C'était comme l'aspect de la vision que j'ai eue, selon la vision que j'ai eue lorsque je suis venu pour détruire la ville; les visions étaient semblables à celle que j'ai eue près du fleuve Kebar; et je suis tombé sur ma face.
Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
4 La gloire de Yahvé entra dans la maison par le chemin de la porte qui donne sur l'orient.
Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
5 L'Esprit m'enleva et me fit entrer dans le parvis intérieur; et voici, la gloire de Yahvé remplissait la maison.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
6 J'entendis quelqu'un me parler hors de la maison, et un homme se tenait près de moi.
Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
7 Il me dit: « Fils d'homme, voici le lieu de mon trône et le lieu de la plante de mes pieds, où j'habiterai pour toujours au milieu des enfants d'Israël. La maison d'Israël ne souillera plus mon saint nom, ni eux ni leurs rois, par leurs prostitutions et par les cadavres de leurs rois sur leurs hauts lieux,
Ya ce, “Ɗan mutum, wannan shi ne kursiyina da wurin tafin ƙafafuna. A nan ne zan zauna a cikin Isra’ilawa har abada. Gidan Isra’ila ba zai ƙara ɓata sunana mai tsarki ba, ko su ko sarakunansu, ta wurin karuwanci da gumakan da ba su da rai, sarakunansu a masujadan kan tudu.
8 en plaçant leur seuil près de mon seuil et leur poteau près de mon poteau. Il y avait un mur entre moi et eux, et ils ont souillé mon saint nom par les abominations qu'ils ont commises. C'est pourquoi je les ai consumés dans ma colère.
Sa’ad da suka sa madogarar ƙofarsu kusa da madogarar ƙofata, da katanga kawai a tsakanina da su, sun ɓata sunana mai tsarki ta wurin ayyukansu masu banƙyama. Saboda haka na hallaka su cikin fushina.
9 Maintenant, qu'ils fassent disparaître leur prostitution et les cadavres de leurs rois loin de moi. Alors j'habiterai au milieu d'eux pour toujours.
Yanzu bari su kawar da karuwancinsu da gumakansu waɗanda ba su da rai na sarakunansu daga gabana, zan kuwa zauna a cikinsu har abada.
10 « Toi, fils de l'homme, montre la maison à la maison d'Israël, afin qu'ils aient honte de leurs iniquités; et qu'ils mesurent le modèle.
“Ɗan mutum, ka bayyana haikalin ga mutanen Isra’ila, don su ji kunya saboda zunubansu. Bari su yi la’akari da fasalin,
11 S'ils ont honte de tout ce qu'ils ont fait, fais-leur connaître la forme de la maison, son mode, ses sorties, ses entrées, sa structure, toutes ses ordonnances, toutes ses formes et toutes ses lois, et écris-le à leurs yeux, afin qu'ils en gardent toute la forme, et toutes ses ordonnances, et qu'ils les mettent en pratique.
kuma in suka ji kunyar abubuwan da suka aikata, sai ka sanar musu fasalin haikalin da shirye-shiryensa, ƙofofinsa na shiga da fita, dukan fasalinsa da dukan ƙa’idodinsa da dokokinsa. Ka rubuta waɗannan a gabansu saboda su yi aminci da fasalinsa su kuma kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
12 « Voici la loi de la maison. Au sommet de la montagne, toute la limite qui l'entoure sera très sainte. Voici la loi de la maison.
“Wannan ita ce dokar haikalin. Dukan filin da yake kewaye a kan dutsen, zai zama wuri mafi tsarki. Dokar haikalin ke nan.
13 « Voici les mesures de l'autel, par coudées (la coudée est une coudée et la largeur d'une main): le fond sera d'une coudée, la largeur d'une coudée, et la bordure qui l'entoure d'un empan; ce sera la base de l'autel.
“Waɗannan su ne aune-aunen bagade a tsawon kamu, wannan kamu shi ne kamun tafin hannu. Zurfin magudanar ruwansa kamu ɗaya ne fāɗinsa kuma kamu ɗaya, tare da da’ira kamun tafi ɗaya kewaye da gefensa. Wannan kuma shi ne tsayin bagaden.
14 De la base sur le sol au rebord inférieur, il y aura deux coudées, et la largeur sera d'une coudée; du rebord inférieur au rebord supérieur, il y aura quatre coudées, et la largeur sera d'une coudée.
Daga lambatun da yake a ƙasa har zuwa ƙaramin mahaɗin da yake ƙasa wanda ya kewaye bagade, tsayinsa kamu biyu ne, fāɗinsa kuma kamu guda. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗin wanda ya kewaye bagade, zai zama kamu huɗu, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya.
15 L'autel supérieur aura quatre coudées; depuis le foyer de l'autel et vers le haut, il y aura quatre cornes.
Murhun bagaden kamu huɗu ne, akwai ƙahoni guda huɗu sun miƙe sama daga murhun.
16 Le foyer de l'autel aura douze coudées de long sur douze de large, et sera carré sur ses quatre côtés.
Murhun bagaden murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha biyu, fāɗinsa kuma kamu goma sha biyu.
17 La corniche aura quatorze coudées de long sur quatorze de large dans ses quatre côtés; la bordure qui l'entourera sera d'une demi-coudée; son fond aura une coudée de large; et ses marches seront tournées vers l'orient. »
Gefen bisa ma murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha huɗu fāɗinsa kuma kamu goma huɗu, da da’ira da yake da fāɗin rabin kamu da magudanan ruwa kamu guda kewaye. Matakan bagaden suna fuskantar gabas.”
18 Il me dit: « Fils d'homme, le Seigneur Yahvé dit: 'Voici les règles à observer pour l'autel, le jour où on le construit, pour y offrir des holocaustes et y répandre du sang.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa waɗannan su ne za su zama ƙa’idodi don yin hadaya ta ƙonawa da yayyafawar jini a kan bagaden sa’ad da aka gina shi.
19 Tu donneras aux prêtres lévitiques de la descendance de Tsadok, qui sont près de moi, pour me servir, dit le Seigneur Yahvé, un jeune taureau en sacrifice pour le péché.
Za ka ba da ɗan bijimi a matsayin hadaya ta ƙonawa ga firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, na iyalin Zadok, waɗanda suke zuwa kusa don hidima a gabana, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 Tu prendras de son sang et tu en mettras sur ses quatre cornes, sur les quatre coins de la corniche et sur la bordure tout autour. Tu le purifieras et tu en feras l'expiation de cette manière.
Za ka ɗibi jininsa ka zuba shi a ƙahoni huɗu na bagaden a gefen bisa da kuma kewaye da da’irar, ta haka za ka tsarkake bagaden ka kuma yi kafara dominsa.
21 Tu prendras aussi le taureau du sacrifice pour le péché, et tu le brûleras dans le lieu réservé de la maison, en dehors du sanctuaire.
Za ka ɗauki bijimi na hadaya don zunubi ka ƙone shi a sashen da aka shirya na haikalin a wani wuri waje da wuri mai tsarki.
22 « Le second jour, tu offriras un bouc sans défaut en sacrifice pour le péché; on purifiera l'autel, comme on l'a purifié avec le taureau.
“A rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin hadaya don zunubi, za a kuma tsarkake bagaden yadda aka yi da bijimin.
23 Lorsque tu auras achevé de le purifier, tu offriras un jeune taureau sans défaut et un bélier du troupeau sans défaut.
Sa’ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa ɗan bijimi da kuma rago daga cikin garke, dukansu marasa lahani.
24 Tu les feras approcher de l'Éternel, et les prêtres jetteront du sel sur eux; ils les offriront en holocauste à l'Éternel.
Za ka miƙa su a gaban Ubangiji, firistoci kuma za su barbaɗe gishiri a kansu su kuma miƙa su kamar hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
25 « Pendant sept jours, vous préparerez chaque jour un bouc pour le sacrifice pour le péché. On préparera aussi un jeune taureau et un bélier du troupeau, sans défaut.
“Kwana bakwai za ka tanada bunsuru kullum domin hadaya don zunubi; za ka kuma tanada ɗan bijimi da rago daga garke, dukansu marasa lahani.
26 Pendant sept jours, on fera l'expiation sur l'autel et on le purifiera. Ils le consacreront ainsi.
Kwana bakwai za su yi kafara saboda bagaden su kuma tsarkake shi; ta haka za su keɓe shi.
27 Lorsqu'ils auront accompli ces jours, le huitième jour et les suivants, les prêtres offriront vos holocaustes sur l'autel et vos sacrifices de prospérité. Alors je vous accepterai, dit le Seigneur Yahvé. »
A ƙarshen waɗannan kwanaki, daga rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kan bagade. Sa’an nan zan karɓe ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 43 >