< Ézéchiel 39 >

1 Toi, fils de l'homme, prophétise contre Gog, et dis: « Le Seigneur Yahvé dit: « Voici, j'en veux à toi, Gog, prince de Rosh, de Méschec et de Tubal.
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
2 Je te tournerai, je te conduirai, je te ferai monter des extrémités du nord, et je t'amènerai sur les montagnes d'Israël.
Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
3 Je frapperai ton arc de ta main gauche, et je ferai tomber tes flèches de ta main droite.
Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
4 Tu tomberas sur les montagnes d'Israël, toi, toutes tes hordes, et les peuples qui sont avec toi. Je vous livrerai aux oiseaux de toute espèce et aux bêtes des champs pour qu'ils vous dévorent.
A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
5 Vous tomberez en plein champ, car j'ai parlé, dit le Seigneur Yahvé.
Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
6 J'enverrai un feu sur Magog et sur ceux qui habitent en sécurité dans les îles. Alors ils sauront que je suis Yahvé.
Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
7 "''Je ferai connaître mon saint nom parmi mon peuple d'Israël. Je ne permettrai plus que mon saint nom soit profané. Alors les nations sauront que je suis Yahvé, le Saint en Israël.
“‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
8 Voici, cela vient, et cela s'accomplira, dit le Seigneur Yahvé. « C'est le jour dont j'ai parlé.
Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
9 "« Les habitants des villes d'Israël sortiront, feront du feu avec les armes et les brûleront, tant les boucliers que les cuirasses, les arcs et les flèches, les massues et les lances, et ils en feront du feu pendant sept ans;
“‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
10 de sorte qu'ils ne prendront pas de bois dans les champs et n'en abattront pas dans les forêts, car ils feront du feu avec les armes. Ils pilleront ceux qui les ont pillés, et ils dépouilleront ceux qui les ont dépouillés, dit le Seigneur Yahvé.
Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
11 "''En ce jour-là, je donnerai à Gog un lieu de sépulture en Israël, la vallée de ceux qui passent, à l'est de la mer, et elle arrêtera ceux qui passent. On y enterrera Gog et toute sa multitude, et on l'appellera 'la vallée de Hamon Gog'.
“‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
12 "''La maison d'Israël les enterrera pendant sept mois, afin de purifier le pays.
“‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
13 Oui, tout le peuple du pays les enterrera, et ils deviendront célèbres au jour où je serai glorifié, dit le Seigneur Yahvé.
Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
14 "''Ils mettront à part des hommes continuellement employés qui passeront dans le pays. Ceux qui passeront iront avec ceux qui enterrent ceux qui restent à la surface du pays, pour le purifier. Au bout de sept mois, ils feront des recherches.
“‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
15 Ceux qui fouilleront le pays passeront; et si quelqu'un voit un os d'homme, il dressera un signe à côté, jusqu'à ce que les fossoyeurs l'aient enterré dans la vallée de Hamon Gog.
Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
16 Hamonah sera aussi le nom d'une ville. C'est ainsi qu'ils purifieront le pays. »''
Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
17 « Toi, fils de l'homme, le Seigneur Yahvé dit: « Parle aux oiseaux de toute espèce et à tous les animaux des champs: « Assemblez-vous et venez, rassemblez-vous de tous côtés à mon sacrifice que je vous offre, un grand sacrifice sur les montagnes d'Israël, pour manger de la viande et boire du sang.
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
18 Vous mangerez la chair des puissants, et vous boirez le sang des princes de la terre, des béliers, des agneaux, des boucs, des taureaux, tous gras de Basan.
Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
19 Vous mangerez de la graisse jusqu'à ce que vous soyez rassasiés, et vous boirez du sang jusqu'à ce que vous soyez ivres, de mon sacrifice que j'ai offert pour vous.
A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
20 Vous serez rassasiés à ma table de chevaux et de chars, de vaillants hommes, et de tous les hommes de guerre, dit le Seigneur Yahvé.''
A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 « Je mettrai ma gloire parmi les nations. Alors toutes les nations verront le jugement que j'ai exercé, et la main que j'ai mise sur elles.
“Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
22 Et la maison d'Israël saura que je suis Yahvé, son Dieu, dès ce jour et à l'avenir.
Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
23 Les nations sauront que la maison d'Israël est allée en captivité à cause de son iniquité, parce qu'elle m'a offensé et que je lui ai caché ma face; je l'ai livrée aux mains de ses adversaires et elle est tombée par l'épée.
Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
24 Je les ai traités selon leur impureté et selon leurs transgressions. J'ai caché ma face devant eux.
Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
25 C'est pourquoi le Seigneur Yahvé dit: « Maintenant, je renverrai les captifs de Jacob et j'aurai pitié de toute la maison d'Israël. Je serai jaloux de mon saint nom.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
26 Ils oublieront leur honte et toutes les fautes qu'ils ont commises à mon égard, quand ils habiteront en sécurité dans leur pays. Personne ne les effraiera
Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
27 quand je les aurai ramenés des peuples, rassemblés des terres de leurs ennemis, et que je me serai montré saint au milieu d'eux aux yeux de nombreuses nations.
Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
28 Ils sauront que je suis l'Éternel, leur Dieu, parce que je les ai emmenés en captivité parmi les nations et que je les ai rassemblés dans leur pays. Alors je ne laisserai plus aucun d'eux en captivité.
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
29 Je ne leur cacherai plus ma face, car j'ai répandu mon Esprit sur la maison d'Israël, dit le Seigneur Yahvé. »
Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 39 >