< Ézéchiel 37 >
1 La main de l'Éternel fut sur moi; il me fit sortir par l'Esprit de l'Éternel, et me déposa au milieu de la vallée, qui était pleine d'ossements.
Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
2 Il me fit passer devant eux tout autour; et voici, il y en avait beaucoup dans la vallée ouverte, et voici, ils étaient très secs.
Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
3 Il me dit: « Fils d'homme, ces os peuvent-ils vivre? » J'ai répondu: « Seigneur Yahvé, tu le sais. »
Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
4 Il me dit encore: « Prophétise sur ces os, et dis-leur: Ossements desséchés, écoutez la parole de Yahvé.
Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
5 Le Seigneur Yahvé dit à ces os: « Voici, je vais faire entrer en vous un souffle, et vous vivrez.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
6 Je mettrai sur vous des nerfs, je ferai remonter sur vous de la chair, je vous couvrirai de peau, je ferai entrer en vous un souffle, et vous vivrez. Alors vous saurez que je suis Yahvé. »'"
Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
7 Je prophétisai donc comme on me l'avait ordonné. Comme je prophétisais, il y eut un bruit, et voici qu'il y eut un tremblement de terre. Et les os se rapprochèrent les uns des autres, l'un de l'autre.
Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
8 Je regardai, et voici, il y avait sur eux des nerfs, de la chair qui montait, et de la peau qui les recouvrait; mais il n'y avait en eux aucun souffle.
Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
9 Et il me dit: « Prophétise au vent, prophétise, fils de l'homme, et dis au vent: « Le Seigneur Yahvé dit: « Venez des quatre vents, soufflez, soufflez sur ces morts, et qu'ils vivent »".
Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
10 Et je prophétisai comme il me l'avait ordonné, et le souffle entra en eux, et ils vécurent, et se tinrent sur leurs pieds, une armée extrêmement grande.
Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
11 Il me dit alors: « Fils d'homme, ces os, c'est toute la maison d'Israël. Voici qu'ils disent: 'Nos os sont desséchés, et notre espoir est perdu. Nous sommes complètement isolés.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
12 C'est pourquoi prophétise et dis-leur: « Le Seigneur Yahvé dit: « Voici que j'ouvre vos tombeaux, je vous fais sortir de vos tombeaux, mon peuple, et je vous fais entrer dans le pays d'Israël.
Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
13 Vous saurez que je suis l'Éternel, quand j'aurai ouvert vos tombeaux et que je vous aurai fait sortir de vos tombeaux, mon peuple.
Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
14 Je mettrai mon Esprit en vous, et vous vivrez. Alors je vous placerai dans votre pays, et vous saurez que moi, Yahvé, j'ai parlé et que j'ai agi, dit Yahvé'".
Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
15 La parole de Yahvé me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 « Toi, fils de l'homme, prends un bâton et écris dessus: « Pour Juda et pour les enfants d'Israël, ses compagnons ». Prends ensuite un autre bâton, et écris dessus: « Pour Joseph, le bâton d'Ephraïm, et pour toute la maison d'Israël, ses compagnons ».
“Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
17 Puis tu les joindras l'un à l'autre en un seul bâton, pour qu'ils ne fassent qu'un dans ta main.
Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
18 « Quand les enfants de ton peuple te diront: « Ne veux-tu pas nous montrer ce que tu entends par là? »
“In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
19 dis-leur: « Le Seigneur Yahvé dit: « Voici, je prendrai le bâton de Joseph, qui est dans la main d'Ephraïm, et les tribus d'Israël qui lui sont associées; je les mettrai avec lui, avec le bâton de Juda, et j'en ferai un seul bâton, et ils ne feront qu'un dans ma main.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
20 Les bâtons sur lesquels vous écrivez seront dans votre main, sous leurs yeux. »
Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
21 Dis-leur: « Le Seigneur Yahvé dit: « Voici que je vais prendre les enfants d'Israël du milieu des nations où ils sont allés, je les rassemblerai de tous côtés et je les ramènerai dans leur pays.
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
22 Je ferai d'eux une seule nation dans le pays, sur les montagnes d'Israël. Un seul roi sera leur roi à tous. Ils ne seront plus deux nations. Ils ne seront plus du tout divisés en deux royaumes.
Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
23 Ils ne se souilleront plus par leurs idoles, ni par leurs abominations, ni par aucune de leurs transgressions; mais je les délivrerai de toutes les demeures où ils ont péché, et je les purifierai. Ils seront mon peuple, et je serai leur Dieu.
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
24 "''Mon serviteur David sera leur roi. Ils auront tous un seul berger. Ils marcheront dans mes ordonnances, observeront mes lois et les mettront en pratique.
“‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
25 Ils habiteront dans le pays que j'ai donné à mon serviteur Jacob et dans lequel vos pères ont vécu. Ils y habiteront, eux, leurs enfants et les enfants de leurs enfants, pour toujours. David, mon serviteur, sera leur prince pour toujours.
Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
26 Je conclurai avec eux une alliance de paix. Ce sera une alliance éternelle avec eux. Je les placerai, je les multiplierai, et je placerai mon sanctuaire au milieu d'eux pour toujours.
Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
27 Ma tente sera aussi avec eux. Je serai leur Dieu, et ils seront mon peuple.
Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
28 Les nations sauront que je suis Yahvé qui sanctifie Israël, lorsque mon sanctuaire sera au milieu d'eux pour toujours. »''"
Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”