< Ézéchiel 23 >

1 La parole de Yahvé me fut adressée de nouveau, en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils d'homme, il y avait deux femmes, filles d'une même mère.
“Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
3 Elles se sont prostituées en Égypte. Elles se sont prostituées dans leur jeunesse. On y caressait leurs seins, on y caressait leurs mamelons de jeunesse.
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4 Elles s`appelaient Ohola, l`aînée, et Oholiba, sa sœur. Elles sont devenues miennes, et elles ont engendré des fils et des filles. Quant à leurs noms, Samarie est Oholah, et Jérusalem Oholibah.
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
5 « Oholah jouait les prostituées quand elle était à moi. Elle s'est prostituée à ses amants, aux Assyriens ses voisins,
“Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
6 qui étaient vêtus de bleu, gouverneurs et chefs, tous des jeunes gens désirables, des cavaliers montés sur des chevaux.
waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
7 Elle s'est prostituée à eux, tous les meilleurs hommes de l'Assyrie. Elle se souillait avec les idoles de ceux qu'elle convoitait.
Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
8 Elle n'a pas quitté sa prostitution depuis sa sortie d'Égypte, car dans sa jeunesse ils couchaient avec elle. Ils ont caressé ses mamelons de jeunesse et ils ont déversé sur elle leur prostitution.
Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
9 C'est pourquoi je l'ai livrée entre les mains de ses amants, entre les mains des Assyriens dont elle s'était entichée.
“Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
10 Ils ont découvert sa nudité. Ils ont pris ses fils et ses filles, et ils l'ont tuée par l'épée. Elle devint un sujet de discorde parmi les femmes, car on exerçait sur elle des jugements.
Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
11 « Sa sœur Oholiba vit cela, mais elle était plus corrompue qu'elle dans ses convoitises, et dans sa prostitution qui était plus dépravée que celle de sa sœur.
“Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
12 Elle convoitait les Assyriens, gouverneurs et chefs, ses voisins, vêtus de la façon la plus splendide, des cavaliers montés sur des chevaux, tous des jeunes gens désirables.
Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
13 J'ai vu qu'elle était souillée. Elles ont toutes deux pris le même chemin.
Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
14 « Elle augmenta sa prostitution, car elle vit des hommes représentés sur la muraille, des images de Chaldéens peints en rouge,
“Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
15 vêtus de ceintures à la taille, avec des turbans flottants sur la tête, tous ressemblant à des princes, à l'image des Babyloniens en Chaldée, leur pays natal.
da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
16 Dès qu'elle les vit, elle les convoita et leur envoya des messagers en Chaldée.
Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
17 Les Babyloniens vinrent à elle dans le lit d'amour, et ils la souillèrent par leur prostitution. Elle fut souillée par eux, et son âme fut éloignée d'eux.
Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
18 Alors elle découvrit sa prostitution et découvrit sa nudité. Alors mon âme s'est détachée d'elle, comme mon âme s'est détachée de sa sœur.
Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
19 Mais elle multiplia ses prostitutions, se souvenant des jours de sa jeunesse où elle s'était prostituée au pays d'Égypte.
Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
20 Elle a convoité leurs amants, dont la chair est comme la chair des ânes, et dont le produit est comme le produit des chevaux.
A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
21 C'est ainsi que tu t'es souvenue de la débauche de ta jeunesse, du caressement de tes mamelons par les Égyptiens, à cause de tes seins juvéniles.
Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
22 C'est pourquoi, Oholiba, le Seigneur Yahvé dit: « Voici que je vais soulever contre toi tes amants, ceux dont ton âme est séparée, et je les ferai venir contre toi de toutes parts:
“Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
23 les Babyloniens et tous les Chaldéens, Pékod, Shoa, Koa, et tous les Assyriens avec eux, tous des jeunes gens désirables, des gouverneurs et des chefs, des princes et des hommes de renom, tous montés sur des chevaux.
Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
24 Ils viendront contre toi avec des armes, des chars et des chariots, et avec une multitude de peuples. Ils se dresseront contre toi avec un bouclier et un casque tout autour. Je leur confierai le jugement, et ils te jugeront selon leurs jugements.
Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
25 J'exercerai ma jalousie contre toi, et ils te traiteront avec fureur. Ils t'enlèveront ton nez et tes oreilles. Ton reste tombera par l'épée. Ils prendront tes fils et tes filles, et le reste de ton corps sera dévoré par le feu.
Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
26 Ils te dépouilleront de tes vêtements et emporteront tes beaux bijoux.
Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
27 Ainsi, je ferai cesser ton impudicité et j'éloignerai ta prostitution du pays d'Égypte, afin que tu ne lèves pas les yeux vers eux et que tu ne te souviennes plus de l'Égypte.''
Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
28 Car le Seigneur Yahvé dit: « Voici que je te livre entre les mains de ceux que tu hais, entre les mains de ceux dont ton âme est séparée.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
29 Ils te traiteront avec haine, ils enlèveront tout ton travail, et ils te laisseront nu et dénudé. On découvrira la nudité de ta prostitution, ton impudicité et ta prostitution.
Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
30 Ces choses te seront faites parce que tu t'es prostituée après les nations, et que tu t'es souillée par leurs idoles.
sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
31 Tu as marché dans la voie de ta sœur; c'est pourquoi je remettrai sa coupe entre tes mains ».
Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
32 « Le Seigneur Yahvé dit: Tu boiras dans la coupe de ta sœur, qui est profond et large. On vous ridiculisera et on vous tournera en dérision. Il contient beaucoup.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
33 Vous serez remplis d'ivresse et de chagrin, avec la coupe de l'étonnement et de la désolation, avec la coupe de ta sœur Samarie.
Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
34 Vous le boirez même et le viderez. Vous en rongerez les morceaux brisés, et déchirera vos seins; car je l'ai dit, dit le Seigneur Yahvé.
Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
35 « C'est pourquoi le Seigneur Yahvé dit: « Parce que tu m'as oublié et que tu m'as rejeté derrière ton dos, toi aussi tu portes ton impudicité et ta prostitution. »"
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
36 Yahvé me dit encore: « Fils d'homme, vas-tu juger Oholah et Oholibah? Alors, déclare-leur leurs abominations.
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
37 Car ils ont commis l'adultère, et le sang est dans leurs mains. Ils ont commis l'adultère avec leurs idoles. Ils ont aussi fait passer par le feu leurs fils, qu'ils m'ont enfantés, pour qu'ils soient dévorés.
gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
38 Et voici ce qu'ils m'ont fait: ils ont souillé mon sanctuaire le jour même, et ils ont profané mes sabbats.
Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
39 Car, après avoir immolé leurs enfants à leurs idoles, ils sont venus le même jour dans mon sanctuaire pour le profaner; et voici, ils ont fait cela au milieu de ma maison.
A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
40 « De plus, vous, les sœurs, vous avez fait venir des hommes qui viennent de loin, à qui on a envoyé un messager, et voici qu'ils sont venus; pour eux, vous vous êtes lavées, vous avez peint vos yeux, vous vous êtes parées d'ornements,
“Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
41 et vous vous êtes assises sur un lit majestueux, avec une table préparée devant elle, sur laquelle vous avez mis mon encens et mon huile.
Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
42 « La voix d'une multitude à l'aise était avec elle. Avec des hommes du peuple, on amenait des ivrognes du désert; on leur mettait des bracelets aux mains, et de belles couronnes sur la tête.
“Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
43 Je dis alors, à propos de celle qui avait vieilli dans l'adultère: « Maintenant, ils vont se prostituer avec elle, et elle avec eux ».
Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
44 Ils entrèrent chez elle, comme on entre chez une prostituée. Et ils sont allés vers Ohola et vers Oholiba, les femmes impudiques.
Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
45 Les hommes justes les jugeront avec le jugement des adultères et avec le jugement des femmes qui versent le sang, parce qu'elles sont adultères et que le sang est dans leurs mains.
Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
46 Car le Seigneur Yahvé dit: « Je ferai monter contre eux une foule, je les ferai battre en retraite et je les dépouillerai.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
47 La troupe les lapidera et les expédiera avec leurs épées. Ils tueront leurs fils et leurs filles, et brûleront leurs maisons par le feu.
Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
48 "'Je ferai ainsi disparaître la débauche du pays, afin que toutes les femmes apprennent à ne pas être débauchées comme vous.
“Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
49 On fera retomber sur toi ta débauche, et tu porteras les péchés de tes idoles. Alors vous saurez que je suis le Seigneur Yahvé. »
Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 23 >