< Ézéchiel 17 >

1 La parole de Yahvé me fut adressée, en ces mots:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils d'homme, raconte une énigme, et dis une parabole à la maison d'Israël.
“Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
3 Tu diras: « Le Seigneur Yahvé dit: Un grand aigle aux grandes ailes et aux longues plumes, plein de plumes de diverses couleurs, vint au Liban et prit la cime du cèdre.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
4 Il coupa le plus haut de ses jeunes rameaux, et le transporta dans un pays de trafic. Il le planta dans une ville de marchands.
ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
5 "''Il prit aussi une partie de la semence du pays et la planta dans une terre fertile. Il la plaça près de nombreuses eaux. Il la plaça comme un saule.
“‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
6 Il grandit et devint une vigne étalée, de petite taille, dont les branches étaient tournées vers lui, et dont les racines étaient sous lui. Elle devint donc une vigne, produisit des branches et poussa des rameaux.
ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
7 "''Il y avait aussi un autre grand aigle, avec de grandes ailes et beaucoup de plumes. Voici, cette vigne a plié ses racines vers lui, et elle a poussé ses rameaux vers lui, depuis le sol où elle était plantée, afin qu'il l'arrose.
“‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
8 Elle était plantée dans un bon sol, près de beaucoup d'eaux, afin qu'elle produise des branches et qu'elle porte du fruit, pour être une bonne vigne. »''
An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
9 Dis: « Le Seigneur Yahvé dit: « Prospère-t-il? N'arrachera-t-il pas ses racines et ne coupera-t-il pas ses fruits, pour qu'il se dessèche, pour que toutes ses feuilles fraîches et printanières se flétrissent? Ce n'est pas par un bras fort ou par un grand nombre de personnes qu'elle pourra être relevée de ses racines.
“Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
10 Oui, voici, étant plantée, prospérera-t-elle? Ne se desséchera-t-elle pas quand le vent d'orient la touchera? Elle se flétrira dans le sol où elle a poussé. »'"
Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
11 La parole de Yahvé me fut adressée en ces termes:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
12 « Dis maintenant à la maison rebelle: « Ne savez-vous pas ce que signifient ces choses? ». Dis-leur: Voici, le roi de Babylone est venu à Jérusalem, il a pris son roi et ses chefs, et les a emmenés avec lui à Babylone.
“Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
13 Il prit l'un des descendants royaux, et fit alliance avec lui. Il le fit aussi jurer, et il enleva les puissants du pays,
Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
14 afin d'abaisser le royaume, de l'empêcher de se relever, et de le faire subsister en respectant son alliance.
don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
15 Mais il s'est rebellé contre lui en envoyant ses ambassadeurs en Égypte, pour qu'ils lui donnent des chevaux et un peuple nombreux. Prospérera-t-il? Celui qui fait de telles choses échappera-t-il? Viendra-t-il à bout de l'alliance, et échappera-t-il quand même?
Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
16 « Je suis vivant, dit le Seigneur Yahvé, dans le lieu où habite le roi qui l'a fait roi, dont il a méprisé le serment et rompu l'alliance, il mourra avec lui au milieu de Babylone.
“‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
17 Pharaon, avec sa puissante armée et sa grande troupe, ne l'aidera pas dans la guerre, quand on élèvera des monticules et qu'on construira des forts pour exterminer de nombreuses personnes.
Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
18 Car il a méprisé le serment en rompant l'alliance; et voici, il avait donné sa main, et pourtant il a fait toutes ces choses. Il ne s'échappera pas.
Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
19 C'est pourquoi le Seigneur Yahvé dit: 'Je suis vivant! Je ferai retomber sur sa tête mon serment qu'il a méprisé et mon alliance qu'il a rompue.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
20 J'étendrai mon filet sur lui, et il sera pris dans mon piège. Je l'emmènerai à Babylone, et là j'entrerai en jugement avec lui pour la faute qu'il a commise envers moi.
Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
21 Tous ses fugitifs, dans toutes ses bandes, tomberont par l'épée, et ceux qui resteront seront dispersés à tout vent. Alors vous saurez que c'est moi, Yahvé, qui l'ai dit ».
Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
22 « Le Seigneur Yahvé dit: 'Je prendrai aussi une partie de la cime du cèdre et je la planterai. J'arracherai de la cime de ses jeunes rameaux un rameau tendre, et je le planterai sur une montagne élevée et haute.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
23 Je le planterai sur la montagne élevée d'Israël; il produira des rameaux, il portera du fruit, et il sera un bon cèdre. Des oiseaux de toute espèce habiteront à l'ombre de ses branches.
A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
24 Tous les arbres des champs sauront que moi, Yahvé, j'ai fait tomber le grand arbre, j'ai élevé le petit arbre, j'ai desséché l'arbre vert, et j'ai fait prospérer l'arbre sec. "'Moi, Yahvé, j'ai parlé et je l'ai fait.'"
Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”

< Ézéchiel 17 >