< Ézéchiel 16 >
1 La parole de Yahvé me fut adressée, en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils d'homme, fais connaître à Jérusalem ses abominations;
“Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
3 et dis: « Le Seigneur Yahvé dit à Jérusalem: « Ton origine et ta naissance sont du pays des Cananéens. Ton père était un Amoréen, et ta mère était une Héthienne.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
4 Quant à ta naissance, le jour où tu es née, ton nombril n'a pas été coupé. On ne t'a pas lavée dans l'eau pour te purifier. On ne t'a pas salé du tout, ni enveloppé dans des couvertures.
A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
5 Aucun œil n'a eu pitié de toi, pour te faire l'une de ces choses, pour avoir pitié de toi; mais on t'a jeté en plein champ, parce que tu étais en horreur le jour où tu es né.
Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
6 « Quand j'ai passé près de toi et que je t'ai vu te vautrer dans ton sang, je t'ai dit: « Si tu es dans ton sang, vis.
“‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
7 Je t'ai fait multiplier comme les plantes des champs, tu as grandi et tu es devenue grande, et tu as atteint une grande beauté. Tes seins se sont formés, et tes cheveux ont poussé; pourtant tu étais nue et dénudée.
Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
8 "''Quand je passais devant toi et que je te regardais, voici que ton temps était le temps de l'amour; j'ai étendu sur toi mon vêtement et j'ai couvert ta nudité. Oui, je me suis engagé envers toi et j'ai conclu une alliance avec toi, dit le Seigneur Yahvé, et tu es devenu mien.
“‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 "''Puis je t'ai lavé avec de l'eau. Oui, j'ai lavé à fond ton sang, et je t'ai oint d'huile.
“‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
10 Je t'ai aussi revêtu d'un ouvrage brodé et je t'ai mis des sandales de cuir. Je t'ai habillé de lin fin et je t'ai couvert de soie.
Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
11 Je t'ai paré d'ornements, j'ai mis des bracelets à tes mains, et j'ai mis une chaîne à ton cou.
Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
12 J'ai mis un anneau à ton nez, des boucles d'oreille à tes oreilles, et une belle couronne sur ta tête.
na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
13 Tu étais ainsi paré d'or et d'argent. Tes vêtements étaient de lin fin, de soie et de broderie. Tu mangeais de la farine fine, du miel et de l'huile. Tu étais d'une grande beauté, et tu as prospéré jusqu'à devenir une famille royale.
Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
14 Ta renommée s'est répandue parmi les nations à cause de ta beauté, car elle était parfaite, grâce à la majesté dont je t'avais revêtue, dit le Seigneur Yahvé.
Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 "''Mais tu t'es confiée à ta beauté, tu t'es prostituée à cause de ta renommée, et tu as déversé ta prostitution sur tous les passants. C'était à lui.
“‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
16 Tu as pris une partie de tes vêtements, tu t'es fait des hauts lieux ornés de couleurs variées, et tu t'es prostituée dessus. Cela ne doit pas arriver, et cela n'arrivera pas.
Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
17 Vous avez aussi pris vos beaux bijoux, de mon or et de mon argent, que je vous avais donnés, et vous vous êtes fait des images d'hommes, et vous vous êtes prostitués avec elles.
Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
18 Tu as pris tes vêtements brodés, tu les as couverts, et tu as mis devant eux mon huile et mon encens.
Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
19 Et le pain que je t'ai donné, la fleur de farine, l'huile et le miel, dont je t'ai nourri, tu l'as mis devant eux comme un parfum agréable, et il en a été ainsi, dit le Seigneur Yahvé.
Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 "« Tu as pris tes fils et tes filles, que tu m'avais enfantés, et tu les as sacrifiés pour qu'ils soient dévorés. Votre prostitution a-t-elle été peu de chose,
“‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
21 pour que vous fassiez mourir mes enfants et que vous les livriez, en les faisant passer par le feu pour eux?
Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
22 Dans toutes tes abominations et tes prostitutions, tu ne t'es pas souvenu des jours de ta jeunesse, quand tu étais nu et dénudé, et que tu te vautrais dans ton sang.
Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
23 "« Il est arrivé, après toutes vos méchancetés, malheur à vous, dit le Seigneur Yahvé,
“‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
24 que vous vous êtes bâti une voûte, et que vous vous êtes fait une place élevée dans toutes les rues.
kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
25 Tu t'es bâti une place élevée à la tête de chaque chemin, et tu as fait de ta beauté une abomination; tu as ouvert tes pieds à tous les passants, et tu as multiplié tes prostitutions.
A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
26 Tu t'es aussi livrée à l'impudicité avec les Égyptiens, tes voisins, grands par la chair, et tu as multiplié tes prostitutions, pour m'irriter.
Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
27 Voici donc que j'ai étendu ma main sur toi, que j'ai diminué ta part, et que je t'ai livrée à la volonté de celles qui te haïssent, les filles des Philistins, qui ont honte de ton impudicité.
Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
28 Tu t'es aussi prostituée avec les Assyriens, parce que tu étais insatiable; oui, tu t'es prostituée avec eux, et pourtant tu n'étais pas satisfaite.
Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
29 Tu as en outre multiplié tes prostitutions jusqu'au pays des marchands, jusqu'en Chaldée; et pourtant tu n'as pas été satisfaite de cela.
Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
30 "« Que ton cœur est faible, dit le Seigneur Yahvé, puisque tu fais toutes ces choses, qui sont l'œuvre d'une prostituée impudente,
“‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
31 en ce que tu bâtis ta voûte à la tête de chaque chemin, et que tu fais ta place élevée dans chaque rue, et que tu n'as pas été comme une prostituée, en ce que tu méprises le salaire.
Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
32 "« Femme adultère, qui prend des étrangers au lieu de son mari!
“‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
33 Les gens font des cadeaux à toutes les prostituées; mais toi, tu fais des cadeaux à tous tes amants, et tu les corromps, afin qu'ils viennent de tous côtés pour te prostituer.
Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
34 Tu es différente des autres femmes dans ta prostitution, en ce que personne ne te suit pour se prostituer; et comme tu donnes un salaire, et qu'on ne te donne pas de salaire, tu es donc différente. »''
Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
35 C'est pourquoi, prostituée, écoute la parole de Yahvé:
“‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
36 Le Seigneur Yahvé dit: Parce que ta souillure s'est répandue et que ta nudité a été découverte par tes prostitutions avec tes amants, à cause de toutes les idoles de tes abominations et du sang de tes enfants que tu leur as donné,
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
37 voici, je rassemblerai tous tes amants avec lesquels tu as pris plaisir, tous ceux que tu as aimés et tous ceux que tu as haïs. Je les rassemblerai même contre toi de toutes parts, et je leur découvrirai ta nudité, afin qu'ils voient toute ta nudité.
saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
38 Je te jugerai comme on juge les femmes qui rompent le mariage et versent le sang, et je ferai retomber sur toi le sang de la colère et de la jalousie.
Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
39 Je te livrerai aussi entre leurs mains; ils jetteront tes voûtes et briseront tes hauts lieux. Ils te dépouilleront de tes vêtements et prendront tes beaux bijoux. Ils te laisseront nu et dénudé.
Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
40 Ils amèneront contre toi une troupe, ils te lapideront, ils te transperceront de leurs épées.
Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
41 Ils brûleront vos maisons par le feu, et ils exerceront sur vous des jugements en présence de nombreuses femmes. Je te ferai cesser de te prostituer, et tu ne donneras plus de salaire.
Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
42 Je ferai en sorte que ma colère contre toi s'apaise, et que ma jalousie s'éloigne de toi. Je me tairai, et je ne me mettrai plus en colère.
Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
43 "« Parce que tu ne t'es pas souvenu des jours de ta jeunesse, mais que tu t'es déchaîné contre moi en toutes ces choses, voici que je fais retomber ta voie sur ta tête, dit le Seigneur Yahvé: « et tu ne commettras plus cette infamie avec toutes tes abominations.
“‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
44 « Voici, tous ceux qui se servent de proverbes se serviront de ce proverbe contre toi, en disant: « Telle est la mère, telle est la fille ».
“‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
45 Tu es la fille de ta mère, qui a en horreur son mari et ses enfants, et tu es la sœur de tes sœurs, qui ont en horreur leurs maris et leurs enfants. Ta mère était une Hittite, et ton père un Amoréen.
Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
46 Ta sœur aînée est Samarie, qui habite à ta gauche, elle et ses filles; et ta sœur cadette, qui habite à ta droite, est Sodome avec ses filles.
Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
47 Tu n'as pas marché dans leurs voies, tu n'as pas commis leurs abominations; mais bientôt tu t'es corrompue plus qu'eux dans toutes tes voies.
Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
48 Je suis vivant, dit le Seigneur Yahvé, Sodome, ta sœur, n'a pas fait, elle et ses filles, ce que tu as fait, toi et tes filles.
Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
49 "''Voici ce qu'était l'iniquité de ta sœur Sodome: l'orgueil, l'abondance du pain et l'aisance prospère étaient chez elle et chez ses filles. Elle n'a pas non plus fortifié la main des pauvres et des nécessiteux.
“‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
50 Ils se sont montrés arrogants et ont commis des abominations devant moi. C'est pourquoi je les ai fait disparaître quand je l'ai vu.
Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
51 Samarie n'a pas commis la moitié de tes péchés; mais toi, tu as multiplié tes abominations plus qu'elles, et tu as justifié tes sœurs par toutes les abominations que tu as commises.
Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
52 Tu portes toi-même ta propre honte, en ce que tu as jugé tes sœurs; par les péchés que tu as commis plus abominablement qu'elles, elles sont plus justes que toi. Oui, toi aussi, sois confondue, et porte ta honte, en ce que tu as justifié tes sœurs.
Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
53 "« Je renverserai leur captivité, la captivité de Sodome et de ses filles, la captivité de Samarie et de ses filles, et la captivité de vos captifs au milieu d'eux;
“‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
54 afin que vous portiez votre propre honte, et que vous ayez honte de tout ce que vous avez fait, puisque vous leur êtes une consolation.
domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
55 Tes sœurs, Sodome et ses filles, retourneront dans leur ancien domaine; Samarie et ses filles retourneront dans leur ancien domaine; et toi et tes filles, vous retournerez dans votre ancien domaine.
’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
56 Car ta sœur Sodome n'a pas été mentionnée par ta bouche au jour de ton orgueil,
Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
57 avant que ta méchanceté ne soit découverte, comme au temps de l'opprobre des filles de Syrie, et de toutes celles qui l'entourent, les filles des Philistins, qui te méprisent tout autour.
kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
58 Tu as porté tes débauches et tes abominations, dit Yahvé.
Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
59 "'Car le Seigneur Yahvé dit: « Je vous traiterai aussi comme vous avez fait, vous qui avez méprisé le serment en rompant l'alliance.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
60 Mais je me souviendrai de mon alliance avec toi aux jours de ta jeunesse, et j'établirai avec toi une alliance éternelle.
Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
61 Alors tu te souviendras de tes voies et tu auras honte quand tu recevras tes sœurs, tes aînées et tes cadettes; et je te les donnerai pour filles, mais non par ton alliance.
Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
62 J'établirai mon alliance avec vous. Alors vous saurez que je suis Yahvé;
Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
63 afin que vous vous souveniez et que vous soyez confus, et que vous n'ouvriez plus la bouche à cause de votre honte, quand je vous aurai pardonné tout ce que vous avez fait, dit le Seigneur Yahvé.'"
Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”