< Ézéchiel 15 >

1 La parole de Yahvé me fut adressée, en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 « Fils d'homme, qu'est-ce que le cep de vigne plus que tout autre arbre, le sarment qui est parmi les arbres de la forêt?
“Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
3 En prendra-t-on du bois pour en faire quelque chose? En prendra-t-on une épingle pour y suspendre quelque objet?
An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
4 Voici, il est jeté au feu pour servir de combustible; le feu en a dévoré les deux extrémités, et le milieu en est brûlé. Est-il utile à quelque œuvre?
Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
5 Voici, quand il était entier, il n'était propre à aucun ouvrage. Combien moins encore, quand le feu l'aura dévoré et qu'il aura été brûlé, sera-t-il encore propre à quelque œuvre? ".
In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
6 C'est pourquoi le Seigneur Yahvé dit: « Comme le bois de vigne parmi les arbres de la forêt, que j'ai donné au feu pour combustible, ainsi je donnerai aux habitants de Jérusalem.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
7 Je tournerai ma face contre eux. Ils sortiront du feu, mais le feu les dévorera encore. Et vous saurez que je suis Yahvé, quand je tournerai ma face contre eux.
Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
8 Je dévasterai le pays, parce qu'ils ont été infidèles, dit le Seigneur Yahvé.
Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 15 >