< Ézéchiel 10 >

1 Alors je regardai, et voici, dans l'espace qui était au-dessus de la tête des chérubins, il y avait au-dessus d'eux comme une pierre de saphir, comme l'apparence d'un trône.
Na duba, sai na ga kamannin kursiyin saffaya a kan sararin da yake a bisa kawunan kerubobi.
2 Il parla à l'homme vêtu de lin, et dit: « Va entre les roues tournantes, jusque sous le chérubin, remplis tes deux mains de charbons ardents d'entre les chérubins, et répands-les sur la ville. » Il est entré pendant que je regardais.
Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da yake saye da lilin, “Ka shiga cikin da’irorin da suke ƙarƙashin kerubobi. Ka cika hannuwanka da garwashin wuta wanda yake tsakanin kerubobin ka kuma watsar da su a kan birnin.” Yayinda nake dubawa, sai ya shiga.
3 Or les chérubins se tenaient à droite de la maison quand l'homme entra, et la nuée remplissait le parvis intérieur.
Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na haikali sa’ad da mutumin ya shiga, sai girgije ya cika filin da yake can ciki.
4 La gloire de Yahvé monta du chérubin et se tint au-dessus du seuil de la maison; la maison fut remplie de la nuée, et le parvis fut rempli de l'éclat de la gloire de Yahvé.
Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa kerubobi ya tafi zuwa madogarar ƙofar haikali. Girgijen ya cika haikali, filin kuwa ya cika da hasken ɗaukakar Ubangiji.
5 Le bruit des ailes des chérubins se faisait entendre jusqu'au parvis extérieur, comme la voix du Dieu tout-puissant quand il parle.
Sai aka ji ƙarar fikafikan kerubobin har a filin waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa’ad da ya yi magana.
6 Lorsqu'il donna cet ordre à l'homme vêtu de lin: « Prends du feu entre les roues tournantes, entre les chérubins », il entra et se tint près d'une roue.
Sa’ad da Ubangiji ya umarci mutumin da yake saye da lilin cewa, “Ka ɗibi wuta daga cikin tsakanin da’irorin, daga tsakanin kerubobin,” sai mutumin ya shiga ya tsaya kusa da da’irar.
7 Le chérubin étendit sa main d'entre les chérubins vers le feu qui était entre les chérubins; il en prit une partie, et la mit dans les mains de l'homme vêtu de lin, qui la prit et sortit.
Sa’an nan ɗaya daga cikin kerubobin ya miƙa hannu zuwa wurin wutar da take tsakaninsu. Ya ɗebo wutar daga ciki ya zuba a hannuwan mutumin da yake saye da lilin, shi kuwa ya karɓa ya fita.
8 La forme d'une main d'homme apparaissait ici dans les chérubins sous leurs ailes.
(A ƙarƙashin fikafikan kerubobin ana iya ganin abin da ya yi kamar hannuwan mutum.)
9 Je regardai, et voici, il y avait quatre roues à côté des chérubins, une roue à côté d'un chérubin, et une autre roue à côté d'un autre chérubin. L'aspect des roues était semblable à une pierre de béryl.
Na duba, sai na ga kusa da kerubobin akwai da’irori huɗu, kowanne kusa da kerub guda; da’irorin suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja.
10 Elles avaient toutes les quatre la même apparence, comme une roue dans une roue.
Game da kamanninsu kuwa, huɗu a cikinsu sun yi kama da juna; kowanne ya yi kamar da da’ira a cikin da’ira.
11 Quand elles allaient, elles allaient dans leurs quatre directions. Ils ne se tournaient pas en marchant, mais ils suivaient la tête jusqu'à l'endroit où elle se trouvait. Ils ne se tournaient pas en marchant.
Yayinda suke tafiya, sukan tafi kowane gefe huɗun da kerubobin suka nufa; da’irorin ba sa juyawa yayinda kerubobin suke tafiya. Kerubobin suka tafi kowane gefen da kan ya nufa, ba tare da juyawa ba sa’ad da suke tafiya.
12 Tout leur corps, y compris leur dos, leurs mains, leurs ailes et les roues, était rempli d'yeux tout autour, même les roues qu'ils avaient tous les quatre.
Jikunansu gaba ɗaya, har da bayansu, hannuwansu da fikafikansu, sun cika gaba ɗaya da idanu, kamar yadda suke a da’irori huɗun.
13 Quant aux roues, elles étaient appelées, à ce que j'ai entendu, « les roues tournantes ».
Na ji ana kiran da’irorin “da’irorin guguwa.”
14 Chacune d'elles avait quatre faces. La première face était celle d'un chérubin. La deuxième face était la face d'un homme. La troisième face était la face d'un lion. La quatrième était la face d'un aigle.
Kowane daga kerubobin yana da fuskoki huɗu. Fuska ɗaya na kerub ne, na biyun fuskar mutum ne, na ukun fuskar zaki ne, na huɗun kuwa fuskar gaggafa ce.
15 Les chérubins se sont levés. C'est l'être vivant que j'ai vu près du fleuve Kebar.
Sai kerubobin suka tashi sama. Waɗannan ne halittu masu ran da na gani kusa da Kogin Kebar.
16 Quand les chérubins allaient, les roues allaient à côté d'eux; et quand les chérubins levaient leurs ailes pour s'élever de la terre, les roues ne tournaient pas non plus d'à côté d'eux.
Sa’ad da kerubobin suka motsa, sai da’irorin da suke kusa da su su motsa; kuma sa’ad da kerubobin suka buɗe fikafikansu don su tashi daga ƙasa, da’irorin ba sa barin wurarensu.
17 Quand ils se tenaient debout, ils se tenaient debout. Quand ils s'élevaient, ceux-ci s'élevaient avec eux, car l'esprit de l'être vivant était en eux.
Sa’ad da kerubobin suka tsaya cik, su ma sukan tsaya cik; kuma sa’ad da kerubobin suka tashi, sai su ma su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun yana a cikinsu.
18 La gloire de Yahvé sortit du seuil de la maison et se tint au-dessus des chérubins.
Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa madogarar ƙofar haikali ya kuma tsaya a bisa kerubobi.
19 Les chérubins levèrent leurs ailes et s'élevèrent de terre à mes yeux quand ils sortirent, avec les roues à côté d'eux. Ils se tinrent à l'entrée de la porte orientale de la maison de Yahvé, et la gloire du Dieu d'Israël était au-dessus d'eux, en haut.
Yayinda nake duba, kerubobin suka buɗe fikafikansu suka kuma tashi daga ƙasa, yayinda suka tafi kuwa, da’irorin suka tafi tare da su. Suka tsaya a mashigin ƙofar gabas na gidan Ubangiji, ɗaukakar Allah na Isra’ila kuwa yana a kansu.
20 Voici l'être vivant que j'ai vu sous le Dieu d'Israël, près du fleuve Kebar; et j'ai su que c'étaient des chérubins.
Waɗannan ne rayayyun halittun da na gani a ƙarƙashin Allah na Isra’ila kusa da Kogin Kebar, na kuma gane cewa su kerubobi ne.
21 Chacun avait quatre faces, et chacun avait quatre ailes. La forme des mains d'un homme était sous leurs ailes.
Kowanne yana da fuskoki huɗu da fikafikai huɗu, a ƙarƙashin kuwa akwai wani abin da ya yi kamar hannuwan mutum.
22 Quant à la ressemblance de leurs visages, ce sont les visages que j'ai vus près du fleuve du Kebar, leur aspect et eux-mêmes. Ils allaient tous droit devant eux.
Fuskokinsu suna da kamanni ɗaya da waɗanda na gani kusa da Kogin Kebar. Kowanne ya tafi kai tsaye sosai.

< Ézéchiel 10 >