< Exode 24 >

1 Il dit à Moïse: « Monte vers Yahvé, toi, Aaron, Nadab et Abihu, et soixante-dix des anciens d'Israël; et tu te prosterneras à distance.
Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku hauro zuwa wurina, kai da Haruna, Nadab da Abihu, da kuma dattawa saba’in a cikin Isra’ila. Za ku yi sujada da ɗan nisa,
2 Moïse seul s'approchera de Yahvé, mais eux ne s'approcheront pas. Le peuple ne montera pas avec lui. »
sai Musa kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama’a su hau tare da shi.”
3 Moïse vint raconter au peuple toutes les paroles de Yahvé et toutes les ordonnances; et tout le peuple répondit d'une seule voix: « Nous ferons tout ce que Yahvé a dit. »
Sa’ad da Musa ya tafi ya faɗa wa mutanen duk kalmomin Ubangiji da dokokinsa, sai suka amsa da murya ɗaya suna cewa, “Duk abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi.”
4 Moïse écrivit toutes les paroles de Yahvé, puis il se leva de bon matin et construisit un autel au pied de la montagne, avec douze piliers pour les douze tribus d'Israël.
Sai Musa ya rubuta duk abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tashi kashegari da sassafe ya gina bagade kusa da dutsen, ya aza al’amudai goma sha biyu bisa ga kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
5 Il envoya des jeunes gens parmi les enfants d'Israël, qui offrirent des holocaustes et sacrifièrent des animaux en sacrifice de prospérité à Yahvé.
Sai ya aiki samarin Isra’ilawa, suka miƙa hadaya ta ƙonawa, suka kuma miƙa ƙananan bijimai don hadaya ta salama ga Ubangiji.
6 Moïse prit la moitié du sang et la mit dans des bassins, et il aspergea l'autel avec la moitié du sang.
Musa ya ɗauki rabin jinin ya zuba a cikin kwanoni, rabin kuma ya yayyafa a kan bagaden.
7 Il prit le livre de l'alliance et le lut à l'oreille du peuple, qui dit: « Nous ferons tout ce que l'Éternel a dit, et nous obéirons. »
Sa’an nan ya ɗauki Littafin Alkawari ya karanta wa mutane. Suka amsa suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa; za mu yi biyayya.”
8 Moïse prit le sang, en fit l'aspersion sur le peuple et dit: « Regardez, c'est le sang de l'alliance que Yahvé a conclue avec vous au sujet de toutes ces paroles. »
Musa ya kuma ɗauki jinin, ya yayyafa a kan mutanen ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, bisa ga dukan waɗannan kalmomi.”
9 Alors montèrent Moïse, Aaron, Nadab, Abihu et soixante-dix des anciens d'Israël.
Musa da Haruna, Nadab da Abihu, da dattawa saba’in, Allah na Isra’ila suka haura
10 Ils virent le Dieu d'Israël. Sous ses pieds, il y avait comme un ouvrage pavé de pierre de saphir, comme les cieux pour la clarté.
suka kuma ga Allah na Isra’ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa akwai wani abu wanda aka yi da saffaya, mai haske kuma kamar sararin sama kansa.
11 Il ne mit pas la main sur les nobles des enfants d'Israël. Ils voyaient Dieu, et ils mangeaient et buvaient.
Amma Allah bai yi wa shugabannin Isra’ila wani abu ba; suka ga Allah, suka ci suka kuma sha.
12 Yahvé dit à Moïse: « Monte vers moi sur la montagne et reste là; je te donnerai les tables de pierre contenant la loi et les commandements que j'ai écrits, afin que tu les enseignes. »
Ubangiji ya ce wa Musa, “Hauro wurina a kan dutse, ka tsaya a nan, zan ba ka allunan dutsen, da doka da umarnan da na rubuta don koyonsu.”
13 Moïse se leva avec Josué, son serviteur, et Moïse monta sur la montagne de Dieu.
Sa’an nan Musa ya fita tare da Yoshuwa mataimakinsa, ya kuwa hau kan dutsen Allah.
14 Il dit aux anciens: « Attendez-nous ici, jusqu'à ce que nous revenions vers vous. Voici qu'Aaron et Hur sont avec vous. Quiconque a un différend peut s'adresser à eux. »
Ya ce wa dattawan, “Ku jira mu a nan, sai mun dawo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai yă je wurinsu.”
15 Moïse monta sur la montagne, et la nuée couvrit la montagne.
Da Musa ya hau dutsen, sai girgije ya rufe dutsen,
16 La gloire de Yahvé se posa sur la montagne du Sinaï, et la nuée la couvrit pendant six jours. Le septième jour, il appela Moïse du milieu de la nuée.
sai ɗaukakar Ubangiji ta sauka a kan Dutsen Sinai, kwana shida girgije ya rufe dutsen, a rana ta bakwai, sai Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.
17 L'aspect de la gloire de Yahvé était comme un feu dévorant au sommet de la montagne, aux yeux des enfants d'Israël.
Ga Isra’ilawa dai, ɗaukakar Ubangiji ta yi kamar wuta mai ci a kan dutse.
18 Moïse entra au milieu de la nuée et monta sur la montagne; et Moïse resta sur la montagne quarante jours et quarante nuits.
Sa’an nan Musa ya shiga girgijen ya hau kan dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba’in da dare arba’in.

< Exode 24 >