< Exode 23 >

1 « Tu ne répandras pas de fausses nouvelles. Ne joins pas ta main au méchant pour être un témoin malveillant.
“Kada ku baza rahoton ƙarya. Kada kuma ku haɗa baki da mugayen mutane har da ku zama munafukai ta wurin ba da shaidar ƙarya.
2 « Tu ne suivras pas une foule pour faire le mal. Tu ne témoigneras pas au tribunal pour te ranger du côté d'une multitude afin de pervertir la justice.
“Kada ku yi abin da ba daidai ba, don galibin mutane suna yin haka. Sa’ad da kuke ba da shaida a gaban shari’a, kada ku ba da shaidar ƙarya a kauce wa gaskiya don ku faranta wa taron jama’a rai.
3 Tu ne favoriseras pas un pauvre dans sa cause.
Kada ku yi wa matalauci sonkai a gaban shari’a.
4 « Si tu rencontres le bœuf de ton ennemi ou son âne qui s'égare, tu le ramèneras à lui.
“In ka ga saniyar abokin gābanka, ko jakinsa ya ɓace, ka yi ƙoƙari ka mai da shi wurinsa.
5 Si tu vois l'âne de celui qui te hait tomber sous son fardeau, ne le laisse pas. Tu l'aideras à le porter.
In ka ga jakin wani maƙiyinka ya fāɗi a ƙarƙashin kayan da ya ɗauka, kada ka bar shi can, ka yi ƙoƙari ka taimake shi.
6 « Tu ne refuseras pas la justice à tes pauvres gens dans leurs procès.
“Kada ku kāsa yin adalci ga matalauci a wurin shari’a.
7 « Éloigne-toi d'une fausse accusation, et ne tue pas l'innocent et le juste, car je ne justifierai pas les méchants.
Ku yi nesa da ƙage. Kada ku kashe marar laifi tare da mai adalci, gama ba zan bar mugun yă tafi haka kawai ba.
8 « Tu ne prendras pas de pot-de-vin, car le pot-de-vin aveugle les voyants et pervertit les paroles des justes.
“Kada ka karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta waɗanda suke gani, yakan kuma karkatar da maganar masu adalci.
9 « Tu n'opprimeras pas l'étranger, car tu connais le cœur de l'étranger, puisque vous étiez étrangers au pays d'Égypte.
“Kada ka zalunci baƙo, ku kanku kun san halin baƙunci, gama dā ku baƙi ne a Masar.
10 « Pendant six ans, tu ensemenceras ta terre et tu en recueilleras le produit,
“Shekara shida za ku nome gonakinku ku girbe amfanin gonar,
11 mais la septième année, tu la laisseras en repos et en jachère, afin que les pauvres de ton peuple puissent manger; et ce qu'ils laisseront, les animaux des champs le mangeront. De même, tu traiteras ta vigne et ton oliveraie de la même manière.
amma a shekara ta bakwai za ku bar ƙasa tă huta. Sa’an nan matalautan da suke cikinku za su sami abinci daga cikinta, namun jeji kuma za su ci abin da aka bari. Ku yi haka da gonakinku na inabi, da na itatuwan zaitun.
12 « Six jours tu feras ton travail, et le septième jour tu te reposeras, afin que ton bœuf et ton âne se reposent, et que le fils de ton serviteur et l'étranger se rafraîchissent.
“Kwana shida za ku yi aikinku, amma a rana ta bakwai, kada ku yi aiki, saboda saniyarku da jakinku su huta, haka kuma bawan da aka haifa a gidanku, da kuma baƙon da yake a cikinku yă wartsake.
13 « Prends garde de faire tout ce que je t'ai dit; n'invoque pas le nom d'autres dieux et ne les fais pas entendre de ta bouche.
“Ku mai da hankali, ku yi biyayya da duk abin da na faɗa muku. Kada ku kira sunaye waɗansu alloli; kada a ji su a bakinku.
14 « Vous célébrerez une fête en mon honneur trois fois par an.
“Sau uku a shekara za ku yi mini biki.
15 Vous observerez la fête des pains sans levain. Pendant sept jours, vous mangerez des pains sans levain, comme je vous l'ai ordonné, au moment fixé dans le mois d'Abib (car c'est pendant ce mois que vous êtes sortis d'Égypte), et personne ne se présentera devant moi à vide.
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti, kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, kamar yadda na umarce ku. Ku yi wannan a lokacin da aka ayana a watan Abib, gama a watan ne kuka fito daga Masar. “Kada wani yă zo a gabana hannu wofi.
16 Et la fête de la moisson, des prémices de vos travaux, que vous avez semés dans les champs; et la fête de la récolte, à la fin de l'année, quand vous rassemblez vos travaux des champs.
“Ku yi Bikin Girbi da nunan fari na amfanin shuke-shuken gonarku. “Ku yi Bikin Tattarawa a ƙarshen shekara, sa’ad da kuka tattara amfani daga gonarku.
17 Trois fois par an, tous vos mâles se présenteront devant le Seigneur Yahvé.
“Sau uku a shekara, maza duka za su bayyana a gaban Ubangiji Mai Iko Duka.
18 « Tu n'offriras pas le sang de mon sacrifice avec du pain levé. La graisse de mon festin ne restera pas toute la nuit jusqu'au matin.
“Kada ku miƙa mini hadayar jini tare da wani abu mai yisti. “Ba za a bar kitsen bikin hadayata yă kwana ba.
19 Tu apporteras les premiers fruits de ton sol dans la maison de l'Éternel, ton Dieu. « Tu ne feras pas bouillir un chevreau dans le lait de sa mère.
“Dole ne ku kawo mafi kyau daga nunan fari na gonakinku a gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madarar mahaifiyarsa.
20 « Voici, j'envoie un ange devant toi, pour te garder en chemin et te faire entrer dans le lieu que j'ai préparé.
“Ga shi, zan aika mala’ika a gabanku, yă tsare ku a tafiyarku, yă kuma kawo ku wurin da na shirya.
21 Prends garde à lui, et écoute sa voix. Ne le provoque pas, car il ne pardonnera pas ta désobéissance, car mon nom est en lui.
Ku saurare shi, ku kuma kasa kunne ga abin da yake faɗa. Kada ku yi masa tawaye; ba zai gafarta tawayenku ba, gama shi wakilina ne.
22 Mais si vous écoutez vraiment sa voix, et si vous faites tout ce que je dis, alors je serai l'ennemi de vos ennemis, et l'adversaire de vos adversaires.
In kun kasa kunne sosai ga abin da yake faɗi, kuka kuma yi abin da na faɗa, zan zama magabci ga abokan gābanku, zan kuma yi hamayya da abokan hamayyanku.
23 Car mon ange marchera devant toi, et te conduira vers l'Amoréen, le Héthien, le Phérézien, le Cananéen, le Hévien et le Jébusien, et je les exterminerai.
Mala’ikana zai sha gabanku, yă kawo ku cikin ƙasar Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Kan’aniyawa, da Hiwiyawa, da kuma Yebusiyawa, zan kuma kawar da su.
24 Tu ne te prosterneras pas devant leurs dieux, tu ne les serviras pas et tu ne suivras pas leurs pratiques, mais tu les écraseras et tu détruiras leurs piliers.
Kada ku durƙusa wa allolinsu, ko ku yi musu sujada, ko kuma ku bi al’adunsu. Za ku hallaka dukan allolinsu, ku kuma farfasa keɓaɓɓun duwatsunsu.
25 Tu serviras Yahvé ton Dieu, il bénira ton pain et ton eau, et j'éloignerai la maladie du milieu de toi.
Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, albarkansa kuwa za tă kasance a kan abincinku da ruwan shanku. Zan ɗauke cuta daga cikinku.
26 Personne ne fera de fausse couche ni ne sera stérile dans votre pays. J'accomplirai le nombre de vos jours.
A ƙasarku, mace ba za tă yi ɓari ba, ba kuma za a sami marar haihuwa ba. Zan ba ku tsawon rai.
27 J'enverrai ma terreur devant toi, je confondrai tous les peuples que tu rencontreras, et je ferai en sorte que tous tes ennemis te tournent le dos.
“Zan aiki razanata a gabanku, in kuma sa ruɗami a cikin kowace al’ummar da za ku sadu da ita. Zan sa duk abokan gābanku su juye da baya, su gudu.
28 J'enverrai devant toi le frelon qui chassera devant toi l'Hivvite, le Cananéen et le Héthien.
Zan aiki rina a gabanku, su kori Hiwiyawa, Kan’aniyawa da kuma Hittiyawa.
29 Je ne les chasserai pas devant toi en une seule année, de peur que le pays ne devienne désert et que les animaux des champs ne se multiplient contre toi.
Amma ba a shekara guda zan kore muku su ba, don kada ƙasar tă zama kufai har namun jeji su fi ƙarfinku.
30 Je les chasserai peu à peu de devant toi, jusqu'à ce que tu aies augmenté et que tu aies hérité du pays.
Da kaɗan da kaɗan zan kore muku su, har yawanku yă kai yadda za ku mallaki ƙasar.
31 Je fixerai tes limites depuis la mer Rouge jusqu'à la mer des Philistins, et depuis le désert jusqu'au fleuve; car je livrerai entre tes mains les habitants du pays, et tu les chasseras devant toi.
“Zan kafa iyakokinku daga Jan Teku zuwa Bahar Rum, daga hamada kuma zuwa Kogi. Zan ba da mazaunan ƙasar a hannunku, za ku kuwa kore su daga gabanku.
32 Tu ne feras aucune alliance avec eux, ni avec leurs dieux.
Kada ku ƙulla yarjejjeniya da su, ko da allolinsu.
33 Ils n'habiteront pas dans ton pays, de peur qu'ils ne te fassent pécher contre moi, car si tu sers leurs dieux, ce sera un piège pour toi. »
Kada ku bari su zauna a cikin ƙasarku, in har kuka bar su, za su ɓata ku da zunubinsu na bautar allolinsu, har zai yă zama muku tarko.”

< Exode 23 >