< Exode 22 >

1 « Si un homme vole un bœuf ou une brebis, et le tue ou le vend, il paiera cinq bœufs pour un bœuf, et quatre brebis pour une brebis.
“In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
2 Si le voleur est trouvé en train d'entrer par effraction, et qu'il soit frappé de telle sorte qu'il meure, il ne sera pas coupable d'effusion de sang pour lui.
“In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
3 Si le soleil s'est levé sur lui, il est coupable d'effusion de sang. Il devra le restituer. S'il n'a rien, il sera vendu pour son vol.
amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
4 Si le bien volé est trouvé vivant entre ses mains, qu'il s'agisse d'un bœuf, d'un âne ou d'un mouton, il paiera le double.
In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
5 « Si un homme fait paître un champ ou une vigne en laissant son animal en liberté, et que celui-ci paisse dans le champ d'un autre homme, il devra le restituer sur le meilleur de son champ et sur le meilleur de sa vigne.
“In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
6 « Si un feu éclate et s'accroche à des épines, de sorte que les chocs du grain, le grain sur pied ou le champ soient consumés, celui qui a allumé le feu devra le restituer.
“In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
7 « Si un homme livre à son prochain de l'argent ou des objets à garder, et qu'on les vole dans la maison de cet homme, si le voleur est trouvé, il paiera le double.
“In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
8 Si le voleur n'est pas trouvé, le maître de la maison s'approchera de Dieu, pour savoir s'il a mis la main sur les biens de son prochain.
Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
9 Pour toute affaire de dépouillement, qu'il s'agisse d'un bœuf, d'un âne, d'un mouton, d'un vêtement, ou de toute autre chose perdue, au sujet de laquelle quelqu'un dit: « Ceci est à moi », la cause des deux parties sera portée devant Dieu. Celui que Dieu condamne devra payer le double à son prochain.
A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
10 « Si un homme livre à son prochain un âne, un bœuf, un mouton, ou tout autre animal à garder, et qu'il meure, soit blessé, soit chassé, sans que personne ne le voie,
“In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
11 le serment de Yahvé sera entre eux deux: il n'a pas mis la main sur le bien de son prochain; son propriétaire l'acceptera, et il ne le restituera pas.
rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
12 Mais s'il lui est volé, celui qui a volé devra le restituer à son propriétaire.
Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
13 S'il est déchiré en morceaux, qu'il l'apporte comme preuve. Il ne restituera pas ce qui a été déchiré.
In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
14 Si un homme emprunte un objet à son prochain, et que cet objet se blesse ou meurt sans que son propriétaire soit avec lui, il devra le restituer.
“In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
15 Si son propriétaire est avec elle, il ne la restituera pas. Si c'est un objet loué, il est venu pour son bail.
Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
16 Si un homme séduit une vierge qui n'est pas promise au mariage et couche avec elle, il paiera une dot pour qu'elle devienne sa femme.
“Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
17 Si son père refuse catégoriquement de la lui donner, il paiera une somme d'argent correspondant à la dot des vierges.
In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
18 « Tu ne permettras pas à une sorcière de vivre.
“Kada ku bar maiya da rai.
19 « Celui qui aura des rapports sexuels avec un animal sera puni de mort.
“Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
20 « Celui qui sacrifie à un dieu quelconque, sauf à Yahvé seul, sera anéanti.
“Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
21 « Tu ne feras pas tort à un étranger et tu ne l'opprimeras pas, car vous étiez des étrangers dans le pays d'Égypte.
“Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
22 « Vous ne profiterez d'aucune veuve ni d'aucun orphelin.
“Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
23 Si tu en profites, et qu'ils crient vers moi, j'entendrai leur cri;
In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
24 ma colère s'enflammera, et je vous tuerai par l'épée; vos femmes seront veuves, et vos enfants orphelins.
Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
25 « Si tu prêtes de l'argent à un pauvre de mon peuple qui est avec toi, tu ne seras pas pour lui un créancier. Tu ne lui demanderas pas d'intérêt.
“In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
26 Si tu prends en gage le vêtement de ton prochain, tu le lui rendras avant le coucher du soleil,
In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
27 car c'est sa seule couverture, c'est son vêtement pour sa peau. Dans quoi dormira-t-il? S'il crie vers moi, j'entendrai, car je suis miséricordieux.
domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
28 « Tu ne blasphémeras pas Dieu et tu ne maudiras pas un chef de ton peuple.
“Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
29 « Tu ne tarderas pas à offrir de ta récolte et de l'écoulement de tes presses. « Vous me donnerez le premier-né de vos fils.
“Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
30 Tu feras de même avec ton bétail et avec tes brebis. Il restera sept jours avec sa mère, puis le huitième jour, vous me le donnerez.
Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
31 « Vous serez pour moi des hommes saints, c'est pourquoi vous ne mangerez pas de viande déchirée par les animaux dans les champs. Vous la jetterez aux chiens.
“Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.

< Exode 22 >