< Exode 16 >

1 Ils partirent d'Elim, et toute l'assemblée des enfants d'Israël arriva au désert de Sin, qui est entre Elim et Sinaï, le quinzième jour du second mois après leur sortie du pays d'Égypte.
Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
2 Toute l'assemblée des enfants d'Israël murmura contre Moïse et Aaron dans le désert;
A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
3 et les enfants d'Israël leur dirent: « Nous aurions voulu mourir par la main de Yahvé dans le pays d'Égypte, quand nous étions assis près des marmites à viande, quand nous mangions du pain à satiété, car vous nous avez fait sortir dans ce désert pour tuer toute cette assemblée par la faim. »
Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
4 Yahvé dit à Moïse: « Voici, je ferai pleuvoir pour vous du pain du ciel, et le peuple sortira et ramassera chaque jour une portion d'un jour, afin de l'éprouver pour savoir s'il marchera ou non dans ma loi.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
5 Le sixième jour, ils prépareront ce qu'ils auront apporté, et ce sera le double de ce qu'ils auront ramassé chaque jour. »
A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
6 Moïse et Aaron dirent à tous les enfants d'Israël: « Le soir, vous saurez que Yahvé vous a fait sortir du pays d'Égypte.
Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
7 Au matin, vous verrez la gloire de l'Éternel, car il a entendu vos murmures contre l'Éternel. Qui sommes-nous, pour que vous murmuriez contre nous? »
Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
8 Moïse dit: « Maintenant, Yahvé vous donnera de la viande à manger le soir, et le matin du pain pour vous rassasier, parce que Yahvé entend les murmures que vous murmurez contre lui. Et nous, qui sommes-nous? Vos murmures ne sont pas contre nous, mais contre Yahvé. »
Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
9 Moïse dit à Aaron: « Dis à toute l'assemblée des enfants d'Israël: « Approchez-vous de l'Éternel, car il a entendu vos murmures ».
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
10 Comme Aaron parlait à toute l'assemblée des enfants d'Israël, ils regardèrent vers le désert, et voici que la gloire de Yahvé apparut dans la nuée.
Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
11 Yahvé parla à Moïse et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa,
12 « J'ai entendu les murmures des enfants d'Israël. Parle-leur en disant: « Le soir, vous mangerez de la viande, et le matin, vous serez rassasiés de pain. Alors vous saurez que je suis Yahvé votre Dieu ».
“Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
13 Le soir, les cailles montèrent et couvrirent le camp; et le matin, la rosée s'étendit autour du camp.
Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
14 Lorsque la rosée qui s'était déposée eut disparu, voici qu'il y avait à la surface du désert une petite chose ronde, aussi petite que le givre sur le sol.
Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
15 Lorsque les enfants d'Israël la virent, ils se dirent les uns aux autres: « Qu'est-ce que c'est? » Car ils ne savaient pas ce que c'était. Moïse leur dit: « C'est le pain que l'Éternel vous donne à manger.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
16 Voici ce que l'Éternel a ordonné: « Recueillez-en chacun selon ce qu'il mange: un omer par tête, selon le nombre de vos personnes, vous en prendrez chacun pour ceux qui sont dans sa tente. »
Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
17 Les enfants d'Israël firent ainsi; les uns en recueillirent davantage, les autres moins.
Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
18 Quand ils mesurèrent avec un omer, celui qui avait beaucoup ramassé ne manqua de rien, et celui qui avait peu ramassé ne manqua de rien. Chacun ramassait selon ce qu'il mangeait.
Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
19 Moïse leur dit: « Que personne n'en laisse jusqu'au matin. »
Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
20 Mais ils n'écoutèrent pas Moïse, et quelques-uns d'entre eux en laissèrent jusqu'au matin, de sorte qu'il y eut des vers et que le produit devint fétide; Moïse fut irrité contre eux.
Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
21 Ils le ramassèrent matin par matin, chacun selon sa consommation. Lorsque le soleil se mit à chauffer, elle fondit.
Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
22 Le sixième jour, ils ramassèrent deux fois plus de pain, deux omers pour chacun. Tous les chefs de l'assemblée vinrent en parler à Moïse.
A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
23 Celui-ci leur dit: « Voici ce qu'a dit l'Éternel: Demain est un repos solennel, un sabbat consacré à l'Éternel. Faites cuire ce que vous voulez faire cuire, faites bouillir ce que vous voulez faire bouillir, et tout ce qui restera vous sera réservé pour être gardé jusqu'au matin.
Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
24 Ils le conservèrent jusqu'au matin, comme Moïse l'avait ordonné, et il ne devint pas infecte, et il n'y avait pas de vers dedans.
Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
25 Moïse dit: « Mangez-en aujourd'hui, car aujourd'hui est un jour de sabbat pour l'Éternel. Aujourd'hui, vous ne la trouverez pas dans les champs.
Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
26 Pendant six jours, vous le ramasserez, mais le septième jour est le sabbat. Il n'y en aura point. »
Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
27 Le septième jour, une partie du peuple sortit pour ramasser, mais ils ne trouvèrent rien.
Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
28 Yahvé dit à Moïse: « Jusques à quand refuserez-vous d'observer mes commandements et mes lois?
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
29 Voici, parce que Yahvé vous a donné le sabbat, il vous donne le sixième jour le pain de deux jours. Que chacun reste à sa place. Que personne ne sorte de sa place le septième jour. »
Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
30 Le peuple se reposa donc le septième jour.
Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
31 La maison d'Israël l'appela « Manne ». Elle était semblable à de la graine de coriandre, de couleur blanche, et son goût était semblable à celui des galettes au miel.
Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
32 Moïse dit: « Voici ce que Yahvé a ordonné: qu'on en garde un omer plein pour vos descendants, afin qu'ils voient le pain dont je vous ai nourris dans le désert, quand je vous ai fait sortir du pays d'Égypte ».
Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
33 Moïse dit à Aaron: « Prends un pot, mets-y un omer plein de manne et dépose-le devant l'Éternel, pour qu'il soit conservé par vos générations. »
Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
34 Comme l'Éternel l'avait ordonné à Moïse, Aaron la déposa devant le Témoignage, pour qu'elle soit conservée.
Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
35 Les enfants d'Israël mangèrent la manne pendant quarante ans, jusqu'à leur arrivée dans un pays habité. Ils mangèrent la manne jusqu'à ce qu'ils arrivent aux frontières du pays de Canaan.
Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
36 Or, un omer, c'est le dixième d'un épha.
(Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)

< Exode 16 >