< Exode 15 >

1 Alors Moïse et les enfants d'Israël chantèrent ce cantique à Yahvé, et dirent, « Je chanterai à Yahvé, car il a triomphé glorieusement. Il a jeté le cheval et son cavalier dans la mer.
Sa’an nan Musa da Isra’ilawa suka rera wannan waƙa ga Ubangiji suka ce, “Zan rera waƙa ga Ubangiji gama an ɗaukaka shi ƙwarai. Doki da mahayinsa ya jefa su cikin teku.
2 Yah est ma force et mon chant. Il est devenu mon salut. C'est mon Dieu, et je le louerai; le Dieu de mon père, et je l'exalterai.
“Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, ya zama cetona. Shi Allahna ne, zan yabe shi. Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.
3 Yahvé est un homme de guerre. Yahvé est son nom.
Ubangiji mai yaƙi ne Ubangiji ne sunansa.
4 Il a jeté dans la mer les chars de Pharaon et son armée. Ses capitaines choisis sont coulés dans la Mer Rouge.
Karusan Fir’auna da sojojinsa ya jefa cikin teku. Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya.
5 Les profondeurs les recouvrent. Ils sont descendus dans les profondeurs comme une pierre.
Zurfafan ruwaye sun rufe su; suka nutse cikin zurfi kamar dutse.
6 Ta droite, Yahvé, est glorieuse en puissance. Ta main droite, Yahvé, met l'ennemi en pièces.
Hannun damanka, ya Ubangiji, Mai kwarjini ne da iko, hannun damanka, ya Ubangiji, ya farfashe magabci.
7 Dans la grandeur de ton excellence, tu renverses ceux qui s'élèvent contre toi. Tu envoies ta colère. Elle les consume comme du chaume.
“A cikin girman kwarjininka ka kā da waɗanda sun yi gāba da kai. Ka aiki fushinka mai zafi ya cinye su kamar tattaka.
8 Par le souffle de tes narines, les eaux se sont amoncelées. Les inondations se sont redressées comme un tas. Les profondeurs étaient figées au cœur de la mer.
Da hucin numfashin hancinka ruwaye suka tattaru. Ruwaye masu kwararowa, suka tsaya kamar bango; ruwaye na zurfafa suka daskare a tsakiyar teku.
9 L'ennemi dit: « Je poursuivrai. Je les rattraperai. Je partagerai le butin. Mon désir sera satisfait sur eux. Je tirerai mon épée. Ma main les détruira.
Magabci ya yi fahariya, cewa ‘Zan fafare su, in ci musu. Zan raba ganima; abin da na so ya samu. Zan ja takobina hannuna kuwa zai hallaka su.’
10 Tu as soufflé avec ton vent. La mer les a recouverts. Ils ont coulé comme du plomb dans les eaux puissantes.
Amma ka hura numfashinka sai teku ya rufe su. Suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye.
11 Qui est comme toi, Yahvé, parmi les dieux? qui est comme toi, glorieux dans la sainteté, redoutant les louanges, faisant des merveilles?
Wane ne cikin alloli, ya yi kamar ka, ya Ubangiji? Wane ne kamar ka, mai ɗaukaka cikin tsarki, mai banrazana cikin ɗaukaka, mai aikata al’ajabai?
12 Tu as étendu ta main droite. La terre les a avalés.
“Ka miƙa hannunka na dama, ƙasa ta haɗiye abokan gābanka.
13 « Toi, dans ta bonté, tu as conduit le peuple que tu as racheté. Tu les as guidés dans ta force jusqu'à ta demeure sainte.
A cikin ƙaunarka marar iyaka, za ka bishe mutanen da ka fansa. A cikin ƙarfinka, za ka bishe su zuwa mazauninka mai tsarki.
14 Les peuples ont entendu. Ils tremblent. Les habitants de Philadelphie ont été frappés par les douleurs.
Al’ummai za su ji, su yi rawar jiki tsoro zai kama mutanen Filistiya.
15 Alors les chefs d'Edom furent consternés. Le tremblement s'empare des hommes puissants de Moab. Tous les habitants de Canaan ont fondu.
Sarakunan Edom za su tsorata, shugabannin Mowab za su yi rawar jiki, mutanen Kan’ana za su narke.
16 La terreur et l'effroi s'abattent sur eux. Par la grandeur de ton bras, ils sont immobiles comme une pierre, jusqu'à ce que ton peuple passe, Yahvé, jusqu'au passage des personnes que vous avez achetées.
Razana da tsoro za su fāɗo a kansu. Da ikon hannunka za su tsaya cik kamar dutse, har sai mutanen da ka kawo sun wuce, ya Ubangiji.
17 Tu les feras entrer et tu les planteras dans la montagne de ton héritage, le lieu, Yahvé, que tu t'es fait pour y habiter: le sanctuaire, Seigneur, que tes mains ont établi.
Za ka kawo su, ka dasa su a kan dutsen nan naka inda, ya Ubangiji, ka shirya domin mazauninka, wuri mai tsarkin da hannuwanka suka kafa, ya Ubangiji.
18 Yahvé régnera pour toujours et à jamais. »
“Ubangiji zai yi mulki har abada abadin.”
19 Car les chevaux de Pharaon, avec ses chars et ses cavaliers, entrèrent dans la mer, et Yahvé ramena sur eux les eaux de la mer; mais les enfants d'Israël marchèrent à sec au milieu de la mer.
Sa’ad da dawakai, kekunan yaƙi da mahayan dawakan Fir’auna suka shiga cikin teku, Ubangiji ya mayar da ruwan teku a kansu, amma Isra’ilawa suka wuce a cikin teku a busasshiyar ƙasa.
20 Miriam, la prophétesse, sœur d'Aaron, prit un tambourin dans sa main; et toutes les femmes sortirent après elle avec des tambourins et en dansant.
Sa’an nan Miriyam annabiya,’yar’uwar Haruna ta ɗauki ganga a hannunta, dukan mata kuwa suka bi ta, da ganguna suna rawa.
21 Miriam leur répondit, « Chantez à Yahvé, car il a triomphé avec gloire. Il a jeté le cheval et son cavalier dans la mer. »
Miriyam ta yi musu waƙa. “Ku rera ga Ubangiji gama ya ci gawurtacciyar nasara. Doki da mahayi, ya jefa cikin teku.”
22 Moïse fit partir Israël de la mer Rouge, et ils entrèrent dans le désert de Schur. Ils marchèrent trois jours dans le désert, et ne trouvèrent point d'eau.
Sai Musa ya jagoranci Isra’ila daga jan teku zuwa hamadar Shur. Kwana uku suka yi tafiya cikin hamada ba su sami ruwa ba.
23 Lorsqu'ils arrivèrent à Mara, ils ne purent boire des eaux de Mara, car elles étaient amères. C'est pourquoi on l'appela Mara.
Da suka zo Mara, ba su iya shan ruwan ba saboda yana da ɗaci (shi ya sa ake kira wurin Mara).
24 Le peuple murmura contre Moïse, en disant: « Que boirons-nous? »
Sai mutanen suka yi gunaguni a kan Musa, suna cewa, “Me za mu sha?”
25 Moïse cria à Yahvé. Yahvé lui montra un arbre, qu'il jeta dans les eaux, et les eaux devinrent douces. Là, il établit pour eux une loi et une ordonnance, et là, il les mit à l'épreuve.
Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya nuna masa wani itace. Sai ya jefa shi cikin ruwan, sai ruwan ya zama mai daɗi. A can Ubangiji ya yi musu doka da farilla, a can kuma ya gwada su.
26 Il dit: « Si vous écoutez attentivement la voix de l'Éternel, votre Dieu, si vous faites ce qui est juste à ses yeux, si vous êtes attentifs à ses commandements et si vous observez toutes ses lois, je ne vous infligerai aucune des maladies que j'ai infligées aux Égyptiens, car je suis l'Éternel qui vous guérit. »
Ya ce, “In kun kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku kuka yi abin da yake daidai a idanunsa, in kun mai da hankali ga umarnansa, kuka kiyaye dukan farillansa, ba zan kawo muku wani ciwon da na kawo a kan Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.”
27 Ils arrivèrent à Elim, où il y avait douze sources d'eau et soixante-dix palmiers. Ils campèrent là, près des eaux.
Sai suka zo Elim inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu da itatuwan dabino saba’in, suka sauka a can, kusa da ruwa.

< Exode 15 >