< Exode 13 >

1 Yahvé parla à Moïse, et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 « Sanctifie-moi tout premier-né, tout ce qui ouvre le ventre des enfants d'Israël, tant des hommes que des animaux. Il est à moi. »
“Keɓe mini kowane ɗan fari. Ɗan fari wanda ya fara buɗe mahaifa a cikin Isra’ilawa nawa ne, ko na mutum ko na dabba.”
3 Moïse dit au peuple: « Souvenez-vous de ce jour où vous êtes sortis d'Égypte, de la maison de servitude, car c'est par la force de sa main que Yahvé vous a fait sortir de ce lieu. On ne mangera pas de pain levé.
Sai Musa ya ce wa mutane, “Ku tuna da wannan rana, ranar da kuka fito daga Masar, daga ƙasar bauta, gama Ubangiji ya fito da ku da hannu mai iko. Kada ku ci wani abin da yake da yisti.
4 Aujourd'hui, vous sortez au mois d'Abib.
A wannan rana kuka fita, wato, a watan Abib.
5 Lorsque Yahvé vous fera entrer dans le pays des Cananéens, des Héthiens, des Amoréens, des Héviens et des Jébusiens, qu'il a juré à vos pères de vous donner, un pays où coulent le lait et le miel, vous célébrerez cet office pendant ce mois.
Sa’ad da Ubangiji ya kawo ku cikin ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasar da ya rantse wa kakanninku cewa zai ba ku, ƙasar da take zub da madara da zuma, za ku kiyaye wannan biki a wannan wata.
6 Pendant sept jours, vous mangerez des pains sans levain, et le septième jour, vous ferez une fête en l'honneur de l'Éternel.
Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, a kan rana ta bakwai kuma za ku yi biki ga Ubangiji.
7 On mangera des pains sans levain pendant les sept jours; on ne verra pas avec vous de pain levé. On ne verra pas de levure avec vous, dans tout votre territoire.
Ku ci burodi marar yisti cikin kwana bakwai; kada a sami wani abu mai yisti a cikinku, ko a sami yisti a ko’ina a wurinku.
8 En ce jour-là, tu diras à ton fils: « C'est à cause de ce que Yahvé a fait pour moi, quand je suis sorti d'Égypte ».
A ranan nan kowa zai faɗa wa ɗanka, ‘Ina yin haka saboda abin da Ubangiji ya yi mini, sa’ad da na fita daga Masar.’
9 Ce sera pour toi un signe sur ta main et un souvenir entre tes yeux, afin que la loi de l'Éternel soit dans ta bouche; car c'est d'une main forte que l'Éternel t'a fait sortir d'Égypte.
Wannan abin tunawa zai zama muku alama a hannunku, da kuma a goshinku cewa dokar Ubangiji tana a bakinku. Gama Ubangiji ya fitar da ku daga Masar da hannu mai iko.
10 Tu observeras donc cette ordonnance en son temps, d'année en année.
Dole ku kiyaye wannan farilla kowace shekara a lokacinta.
11 « Lorsque Yahvé vous fera entrer dans le pays des Cananéens, comme il l'a juré à vous et à vos pères, et qu'il vous le donnera,
“Bayan Ubangiji ya kawo ku cikin ƙasar Kan’aniyawa, ya kuma ba da ita yadda ya alkawarta muku da rantsuwa, ku da kakanninku,
12 vous réserverez à Yahvé tout ce qui ouvre le ventre et tout premier-né d'un animal que vous avez. Les mâles appartiendront à Yahvé.
sai ku miƙa kowane ɗan fari ga Ubangiji. Duk ɗan farin dabbobinku na Ubangiji ne.
13 Tout premier-né d'un âne, tu le rachèteras avec un agneau; si tu ne le rachètes pas, tu lui briseras le cou; et tu rachèteras tous les premiers-nés de l'homme parmi tes fils.
Amma a fanshi kowane ɗan farin jakinku da ɗan rago. In kuwa ba za ku fanshe shi ba, sai ku karye wuyansa. Sai ku fanshe kowane ɗan farin daga cikin’ya’yanku.
14 Lorsque ton fils te demandera un jour: « Qu'est-ce que cela? », tu lui diras: « C'est par la force de sa main que Yahvé nous a fait sortir d'Égypte, de la maison de servitude.
“A kwanaki masu zuwa, in ɗanka ya tambaye ka, ‘Mene ne manufar wannan?’ Ka faɗa masa cewa, ‘Da hannu mai iko Ubangiji ya fito da mu daga Masar, daga ƙasar bauta.
15 Lorsque Pharaon s'est obstiné à ne pas nous laisser partir, Yahvé a tué tous les premiers-nés du pays d'Égypte, aussi bien les premiers-nés des hommes que ceux du bétail. C'est pourquoi je sacrifie à Yahvé tout ce qui ouvre les entrailles, c'est-à-dire les mâles; mais je rachète tous les premiers-nés de mes fils'.
Sa’ad da Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai yarda ya sallame mu ba, sai Ubangiji ya kashe dukan’ya’yan farin ƙasar Masar, na mutum da na dabba, gaba ɗaya. Domin haka nake yin hadaya ga Ubangiji da’ya’yan fari, maza, da suka fara buɗe mahaifa, amma nakan fanshi dukan’ya’yan farina maza.’
16 Ce sera un signe sur ta main et des symboles entre tes yeux, car c'est par la force de la main que Yahvé nous a fait sortir d'Égypte. »
Za tă kuma zama alama a hannunku da kuma shaida a goshinku cewa Ubangiji ya fito da mu daga Masar da hannunsa mai iko.”
17 Lorsque Pharaon eut laissé partir le peuple, Dieu ne le conduisit pas par le chemin du pays des Philistins, qui était pourtant tout proche, car Dieu dit: « De peur que le peuple ne change d'avis en voyant la guerre, et qu'il ne retourne en Égypte »;
Sa’ad da Fir’auna ya bar mutane su tafi, Allah bai bi da su a hanyar da ta bi ta iyakar Filistiyawa ba, ko da yake wannan hanya ce ta fi kusa. Gama Allah ya ce, “In suka fuskanci yaƙi, wataƙila su canja ra’ayinsu su koma Masar.”
18 mais Dieu conduisit le peuple par le chemin du désert, près de la mer Rouge; et les enfants d'Israël montèrent armés hors du pays d'Égypte.
Saboda haka Allah ya kewaye da mutanen ta hamada zuwa Jan Teku. Isra’ilawa kuwa suka fita daga Masar da shirin yaƙi.
19 Moïse prit avec lui les ossements de Joseph, car il avait fait jurer les enfants d'Israël en disant: « Dieu vous visitera et vous emporterez avec vous mes ossements loin d'ici. »
Musa ya ɗauki ƙasusuwan Yusuf tare da shi, gama Yusuf ya sa Isra’ilawa su rantse masa. Ya ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, sai ku ɗibi ƙasusuwana tare da ku daga wannan wuri.”
20 Ils partirent de Succoth et campèrent à Étham, à l'extrémité du désert.
Bayan sun bar Sukkot sai suka kafa sansani a Etam a bakin hamada.
21 L'Éternel marchait devant eux, le jour dans une colonne de nuée, pour les conduire sur leur chemin, et la nuit dans une colonne de feu, pour les éclairer, afin qu'ils pussent marcher de jour et de nuit.
Da rana Ubangiji yakan ja gabansu a cikin al’amudin girgije domin yă bishe su a kan hanyarsu, da dare kuma a cikin al’amudin wuta domin yă ba su haske, domin su iya tafiya dare da rana.
22 La colonne de nuée, le jour, et la colonne de feu, la nuit, ne s'écartaient pas de devant le peuple.
Al’amudan nan biyu, na girgije da na wuta, ba su daina yi wa jama’a jagora ba.

< Exode 13 >