< Exode 12 >

1 Yahvé parla à Moïse et à Aaron au pays d'Égypte, et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
2 « Ce mois-ci sera pour vous le commencement des mois. Il sera pour vous le premier mois de l'année.
“Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
3 Parle à toute l'assemblée d'Israël, et dis: Le dixième jour de ce mois, on prendra chacun un agneau, selon les maisons de ses pères, un agneau par maison;
Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
4 et si la maison est trop petite pour un agneau, lui et son voisin de maison en prendront un selon le nombre des âmes. Tu feras ton compte pour l'agneau en fonction de ce que chacun pourra manger.
In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
5 Ton agneau sera sans défaut, un mâle d'un an. Tu le prendras parmi les brebis ou parmi les chèvres.
Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
6 Tu le garderas jusqu'au quatorzième jour du même mois, et toute l'assemblée de la communauté d'Israël l'immolera le soir.
Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
7 Ils prendront du sang et en mettront sur les deux montants de la porte et sur le linteau, dans les maisons où ils le mangeront.
Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
8 Cette nuit-là, ils mangeront la viande rôtie au feu, avec des pains sans levain. Ils la mangeront avec des herbes amères.
A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
9 Vous ne la mangerez pas crue, ni bouillie à l'eau, mais rôtie au feu, avec sa tête, ses pattes et ses entrailles.
Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
10 Vous n'en laisserez rien jusqu'au matin; mais ce qui en restera jusqu'au matin, vous le brûlerez au feu.
Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
11 Voici comment vous le mangerez: votre ceinture à la taille, vos sandales aux pieds et votre bâton à la main, et vous le mangerez en hâte: c'est la Pâque de l'Éternel.
Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
12 Car cette nuit-là, je traverserai le pays d'Égypte et je frapperai tous les premiers-nés du pays d'Égypte, hommes et animaux. J'exécuterai des jugements contre tous les dieux d'Égypte. Je suis Yahvé.
“A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
13 Le sang sera pour vous un signe sur les maisons où vous serez. Quand je verrai le sang, je passerai au-dessus de vous, et il n'y aura sur vous aucune plaie qui vous détruise, quand je frapperai le pays d'Égypte.
Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
14 Ce jour sera pour vous un mémorial. Vous le célébrerez comme une fête en l'honneur de Yahvé. Vous le célébrerez comme une fête de génération en génération, par une ordonnance perpétuelle.
“Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
15 "'Pendant sept jours, vous mangerez des pains sans levain; le premier jour, vous ôterez le levain de vos maisons; car quiconque mangera du pain levé, du premier au septième jour, sera retranché d'Israël.
Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
16 Le premier jour, il y aura pour vous une convocation sainte, et le septième jour, une convocation sainte; on n'y fera aucune espèce de travail, si ce n'est ce que chacun doit manger, et seulement ce qui peut être fait par vous.
A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
17 Vous observerez la fête des pains sans levain, car c'est en ce jour que j'ai fait sortir vos armées du pays d'Égypte. C'est pourquoi vous observerez ce jour, de génération en génération, comme une ordonnance perpétuelle.
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
18 Le premier mois, le quatorzième jour du mois, au soir, vous mangerez des pains sans levain, jusqu'au vingt et unième jour du mois, au soir.
A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
19 Il ne se trouvera pas de levure dans vos maisons pendant sept jours, car quiconque mangera du pain levé sera retranché de l'assemblée d'Israël, qu'il soit étranger ou né dans le pays.
Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
20 Vous ne mangerez rien de levé. Dans toutes vos habitations, vous mangerez des pains sans levain.'"
Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
21 Moïse appela tous les anciens d'Israël, et leur dit: « Sortez, prenez des agneaux selon vos familles, et immolez la Pâque.
Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
22 Vous prendrez un bouquet d'hysope, vous le tremperez dans le sang qui sera dans le bassin, et vous frapperez le linteau et les deux montants de la porte avec le sang qui sera dans le bassin. Aucun de vous ne sortira par la porte de sa maison jusqu'au matin.
Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
23 Car l'Éternel passera pour frapper les Égyptiens; et quand il verra le sang sur le linteau et sur les deux montants de la porte, l'Éternel passera par-dessus la porte et ne permettra pas au destructeur d'entrer dans vos maisons pour vous frapper.
Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
24 Tu observeras cette chose comme une ordonnance pour toi et pour tes fils, à perpétuité.
“Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
25 Lorsque vous serez arrivés dans le pays que l'Éternel vous donnera, comme il l'a promis, vous observerez ce service.
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
26 Lorsque vos enfants vous demanderont: « Que signifie ce service? »,
Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
27 vous répondrez: « C'est le sacrifice de la Pâque de l'Éternel, qui a passé au-dessus des maisons des enfants d'Israël en Égypte, lorsqu'il a frappé les Égyptiens et épargné nos maisons ». Le peuple s'inclina et se prosterna.
Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
28 Les enfants d'Israël allèrent et firent ainsi; ils firent ce que Yahvé avait ordonné à Moïse et à Aaron.
Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
29 A minuit, Yahvé frappa tous les premiers-nés du pays d'Egypte, depuis le premier-né de Pharaon assis sur son trône jusqu'au premier-né du captif qui était dans le cachot, et tous les premiers-nés du bétail.
Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
30 Pharaon se leva la nuit, lui, tous ses serviteurs et tous les Égyptiens. Il y eut un grand cri en Égypte, car il n'y avait pas une maison où il n'y eût un mort.
Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
31 Il appela de nuit Moïse et Aaron, et dit: « Lève-toi, sors du milieu de mon peuple, toi et les enfants d'Israël, et va servir Yahvé, comme tu l'as dit!
A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
32 Prenez vos troupeaux et vos bêtes, comme vous l'avez dit, et partez; et bénissez-moi aussi! ».
Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
33 Les Égyptiens étaient pressés par le peuple, pour l'expulser du pays en toute hâte, car ils disaient: « Nous sommes tous des hommes morts. »
Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
34 Le peuple prit sa pâte avant qu'elle ne soit levée, ses pétrins étant liés dans leurs vêtements sur leurs épaules.
Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
35 Les enfants d'Israël agirent selon la parole de Moïse; ils demandèrent aux Égyptiens des bijoux d'argent, des bijoux d'or et des vêtements.
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
36 L'Éternel accorda au peuple la faveur des Égyptiens, qui leur donnèrent ce qu'ils demandaient. Ils pillèrent les Égyptiens.
Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
37 Les enfants d'Israël firent le voyage de Ramsès à Succoth, environ six cent mille hommes à pied, sans compter les enfants.
Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
38 Une multitude hétéroclite montait aussi avec eux, avec des troupeaux, des bœufs et même beaucoup de bétail.
Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
39 Ils cuisaient des gâteaux sans levain avec la pâte qu'ils avaient apportée d'Égypte, car elle n'était pas levée, parce qu'ils avaient été poussés hors d'Égypte, qu'ils ne pouvaient pas attendre et qu'ils n'avaient pas préparé de nourriture pour eux.
Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
40 Or, le temps que les enfants d'Israël vécurent en Égypte fut de quatre cent trente ans.
Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
41 Au bout de quatre cent trente ans, jour pour jour, toutes les armées de Yahvé sortirent du pays d'Égypte.
A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
42 C'est une nuit à laquelle on rend hommage à l'Éternel pour les avoir fait sortir du pays d'Égypte. C'est la nuit de Yahvé, que tous les enfants d'Israël observeront de génération en génération.
Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
43 Yahvé dit à Moïse et à Aaron: « Voici l'ordonnance de la Pâque. Aucun étranger n'en mangera,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
44 mais le serviteur acheté à prix d'argent, quand vous l'aurez circoncis, en mangera.
Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
45 L'étranger et le mercenaire n'en mangeront pas.
amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
46 La viande doit être mangée dans une seule maison. Tu ne porteras pas de viande en dehors de la maison. Vous ne briserez aucun de ses os.
“Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
47 Toute la congrégation d'Israël l'observera.
Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
48 Lorsqu'un étranger habitera chez vous en tant qu'étranger et qu'il voudra célébrer la Pâque en l'honneur de l'Éternel, que tous ses mâles soient circoncis, puis qu'il s'approche et la célèbre. Il sera comme celui qui est né dans le pays, mais aucun incirconcis n'en mangera.
“Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
49 Une seule loi s'appliquera à celui qui est né dans le pays, et à l'étranger qui vit au milieu de vous comme un étranger. »
Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
50 Tous les enfants d'Israël firent ainsi. Ils firent ce que Yahvé avait ordonné à Moïse et à Aaron.
Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
51 Ce même jour, Yahvé fit sortir les enfants d'Israël du pays d'Égypte par leurs armées.
A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.

< Exode 12 >