< Esther 3 >

1 Après cela, le roi Assuérus donna de l'avancement à Haman, fils d'Hammedatha, l'Agaguite, et le plaça au-dessus de tous les chefs qui étaient avec lui.
Bayan waɗannan al’amura, sai Sarki Zerzes ya girmama Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, ya ɗaukaka shi, ya kuma ba shi matsayi mafi girma fiye da na dukan sauran hakiman.
2 Tous les serviteurs du roi qui se trouvaient à la porte du roi se prosternèrent et rendirent hommage à Haman, car le roi avait donné cet ordre à son sujet. Mais Mardochée ne se prosterna pas et ne lui rendit pas hommage.
Dukan masu hidimar da suke a ƙofar sarki suka riƙa durƙusa suna ba wa Haman girma, gama sarki ya ba da umarni a yi masa haka. Amma Mordekai bai durƙusa ya ba shi girma ba.
3 Alors les serviteurs du roi qui étaient à la porte du roi dirent à Mardochée: « Pourquoi désobéis-tu à l'ordre du roi? »
Sa’an nan masu hidimar da suke a ƙofar sarki suka tambaye Mordekai, “Me ya sa ba ka yin biyayya da umarnin sarki?”
4 Or, comme ils lui parlaient tous les jours et qu'il ne les écoutait pas, ils en parlèrent à Haman, pour voir si la raison de Mardochée tiendrait, car il leur avait dit qu'il était Juif.
Kowace rana suna masa magana, amma ya ƙi yă yi. Saboda haka, suka faɗa wa Haman game da wannan don su ga ko za a jure da halin Mordekai, gama ya faɗa musu cewa shi mutumin Yahuda ne.
5 Lorsque Haman vit que Mardochée ne se prosternait pas et ne lui rendait pas hommage, il fut plein de colère.
Sa’ad da Haman ya ga cewa Mordekai ba ya durƙusa ko yă girmama shi, sai ya fusata.
6 Mais il dédaigna l'idée de porter la main sur Mardochée seul, car on lui avait fait connaître le peuple de Mardochée. Haman chercha donc à faire périr tous les Juifs qui se trouvaient dans tout le royaume d'Assuérus, même ceux du peuple de Mardochée.
Da yake an faɗa masa asalin Mordekai, sai ya ga a kashe Mordekai kaɗai ba zai biya masa bukata ba. A maimakon haka, Haman ya nemi hanya a hallaka dukan mutanen Mordekai, wato, Yahudawa, a ko’ina a dukan masarautar Zerzes.
7 Le premier mois, qui est le mois de Nisan, la douzième année du roi Assuérus, on jeta le pur, c'est-à-dire le sort, devant Haman, de jour en jour et de mois en mois, et on choisit le douzième mois, qui est le mois d'Adar.
A shekara ta goma sha biyu ta Sarki Zerzes, a wata na farko, watan Nisan, sai suka jefa fur (wato, ƙuri’a) a gaban Haman don a zaɓi rana da watan da zai dace da ƙulle-ƙullen. Sai ƙuri’a ta fāɗa a kan wata na goma sha biyu, wato, watan Adar.
8 Haman dit au roi Assuérus: « Il y a un certain peuple éparpillé et dispersé parmi les peuples dans toutes les provinces de ton royaume, et leurs lois sont différentes de celles des autres peuples. Ils n'observent pas les lois du roi. Il n'est donc pas dans l'intérêt du roi de leur permettre de rester.
Sai Haman ya ce wa Sarki Zerzes, “Akwai waɗansu mutanen da suke a warwatse, sun kuma bazu a cikin mutane cikin dukan lardunan masarautarka, waɗanda al’adunsu sun yi dabam da na dukan sauran mutane. Mutanen nan ba sa biyayya da dokokin sarki; ba zai yi wa sarki kyau a jure su ba.
9 Si le roi le veut, qu'on écrive qu'ils soient détruits, et je verserai dix mille talents d'argent entre les mains de ceux qui ont la charge des affaires du roi, pour qu'ils les apportent dans les trésors du roi. »
In ya gamshi sarki, bari a yi doka, don a hallaka su, zan kuma sa talenti dubu goma na azurfa a cikin ma’ajin fada saboda mutanen da suka aikata wannan sha’ani.”
10 Le roi prit l'anneau de sa main et le donna à Haman, fils d'Hammedatha l'Agagite, l'ennemi des Juifs.
Saboda haka sarki ya zare zoben hatimi daga yatsarsa, ya ba wa Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, abokin gāban Yahudawa.
11 Le roi dit à Haman: « L'argent t'est donné, le peuple aussi, tu en feras ce que tu voudras. »
Sarki ya ce wa Haman, “Ka riƙe kuɗin, ka kuma yi da mutanen yadda ka ga dama.”
12 Et les scribes du roi furent convoqués le premier mois, le treizième jour du mois; et tout ce qu'Haman avait ordonné fut écrit aux gouverneurs locaux du roi, et aux gouverneurs qui étaient sur chaque province, et aux princes de chaque peuple, à chaque province selon son écriture, et à chaque peuple dans sa langue. Il était écrit au nom du roi Assuérus, et il était scellé avec l'anneau du roi.
Sa’an nan aka kira magatakardun sarki a rana ta goma sha uku na wata na fari. Suka rubuta dukan umarnin Haman a irin rubutun kowane lardi, kuma cikin harshen kowane mutane, zuwa ga shugabannin mahukuntai na sarki, da gwamnonin larduna dabam-dabam, da kuma hakiman mutane dabam-dabam. Aka rubuta waɗannan a sunan Sarki Zerzes da kansa, aka kuma hatimce da zobensa.
13 Des lettres furent envoyées par des courriers dans toutes les provinces du roi, pour détruire, tuer et faire périr tous les Juifs, jeunes et vieux, petits enfants et femmes, en un seul jour, le treizième jour du douzième mois, qui est le mois d'Adar, et pour piller leurs biens.
Aka aika’yan-kada-tă-kwana da saƙoni zuwa dukan lardunan sarki da umarni a hallaka, a karkashe, a kuma kawar da dukan Yahudawa, manya da ƙanana, mata da yara, a kuma washe kayayyakinsu.
14 Une copie de la lettre, indiquant que le décret devait être distribué dans chaque province, fut publiée à tous les peuples, afin qu'ils se tiennent prêts pour ce jour-là.
Za a ba da kofin rubutun a matsayin doka a kowane lardi, a kuma sanar da mutanen kowace al’umma, domin su zauna da shiri don wannan rana.
15 Sur l'ordre du roi, les courriers partirent en hâte, et le décret fut publié dans la citadelle de Suse. Le roi et Haman s'assirent pour boire; mais la ville de Suse était perplexe.
Bisa ga umarnin sarki, sai’yan-kada-tă-kwana, suka tafi da sauri. Aka ba da umarni a mazaunin masarauta da yake a Shusha. Sai Sarki da Haman suka zauna don su sha, amma birnin Shusha ya ruɗe.

< Esther 3 >