< Deutéronome 4 >

1 Maintenant, Israël, écoute les lois et les ordonnances que je t'enseigne, pour les mettre en pratique, afin que tu vives, que tu entres et que tu possèdes le pays que Yahvé, le Dieu de tes pères, te donne.
To, ku ji, ya Isra’ila, ku kasa kunne ga ƙa’idodi da dokokin da nake shirin koya muku. Ku bi su domin ku yi tsawon rai, ku kuma shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku yake ba ku.
2 Vous n'ajouterez rien à la parole que je vous prescris, et vous n'en retrancherez rien, afin d'observer les commandements de l'Éternel, votre Dieu, que je vous prescris.
Kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin abin da nake umarce ku. Amma ku kiyaye umarnan nan na Ubangiji Allahnku, da na ba ku.
3 Tes yeux ont vu ce que l'Éternel a fait à cause de Baal Peor; car l'Éternel, ton Dieu, a fait disparaître du milieu de toi tous les hommes qui suivaient Baal Peor.
Da idanunku, kun ga abin da Ubangiji ya yi a Ba’al-Feyor. Yadda Ubangiji Allahnku ya hallaka waɗansu daga cikinku waɗanda suka yi wa Ba’al-Feyor sujada,
4 Mais vous, qui avez été fidèles à l'Éternel, votre Dieu, vous êtes tous vivants aujourd'hui.
Amma ku da kuka manne ga Ubangiji Allahnku, kuna da rai har wa yau.
5 Voici, je vous ai enseigné des lois et des ordonnances, comme l'Éternel, mon Dieu, me l'a ordonné, afin que vous les mettiez en pratique au milieu du pays dont vous allez prendre possession.
Ga shi, na koya muku ƙa’idodi da dokoki, yadda Ubangiji Allahna ya umarce ni, don ku bi su a ƙasar da za ku shiga ku mallaki.
6 Gardez-les donc et mettez-les en pratique, car c'est là votre sagesse et votre intelligence aux yeux des peuples qui entendront toutes ces lois et qui diront: « Certes, cette grande nation est un peuple sage et intelligent. »
Ku kiyaye su, ku aikata su, gama yin haka zai tabbatar wa sauran al’ummai, kuna da hikima da ganewa. Sa’ad da al’ummai za su ji waɗannan dokoki, za su ce, “Ba shakka, wannan babbar al’umma tana da hikima da ganewa.”
7 Car quelle est la grande nation qui ait un dieu aussi proche d'elle que l'est Yahvé, notre Dieu, quand nous l'invoquons?
Wace al’umma ce mai girma haka wadda allolinta take kusa da su yadda Ubangiji Allahnmu yake kusa da mu a duk sa’ad da muka yi addu’a gare shi?
8 Quelle est la grande nation qui ait des lois et des ordonnances aussi justes que toute cette loi que je vous présente aujourd'hui?
Wace al’umma ce mai girma haka wadda take da ƙa’idodi da dokoki masu adalci kamar waɗannan ƙunshin dokokin da nake sa a gabanku a yau?
9 Seulement, prends garde et garde ton âme avec soin, de peur que tu n'oublies les choses que tes yeux ont vues et qu'elles ne s'éloignent de ton cœur tous les jours de ta vie; mais fais-les connaître à tes enfants et aux enfants de tes enfants -
Ku kula, ku kuma lura da kanku sosai, don kada ku manta da abubuwan da idanunku suka gani, ko kuwa ku bari su fita daga zuciyarku muddin ranku. Ku koyar da su ga’ya’yanku, da’ya’yan’ya’yanku.
10 le jour où tu t'es tenu devant l'Éternel, ton Dieu, à Horeb, quand l'Éternel m'a dit: « Assemble le peuple auprès de moi, et je leur ferai entendre mes paroles, afin qu'ils apprennent à me craindre tous les jours qu'ils vivront sur la terre, et qu'ils les enseignent à leurs enfants. »
Ku tuna da ranar da kuka tsaya a gaban Ubangiji Allahnku a Horeb, sa’ad da ya ce mini, “Ka tara mutane a gabana, don su ji maganata, su koya yin mini bangirma muddin ransu a ƙasar, su kuma iya koyar da su ga’ya’yansu.”
11 Vous vous êtes approchés et vous vous êtes tenus sous la montagne. La montagne brûlait de feu jusqu'au cœur du ciel, avec des ténèbres, des nuages et une obscurité épaisse.
Sai kuka matso kusa, kuka tsaya a gindin dutse yayinda yana cin wuta har zuwa sararin sama, ga kuma baƙin gizagizai da kuma baƙin duhu.
12 Yahvé vous a parlé du milieu du feu: vous avez entendu des paroles, mais vous n'avez pas vu de forme, vous avez seulement entendu une voix.
Sai Ubangiji ya yi magana daga wutar. Kuka ji furcin kalmomin, amma ba ku ga siffar kome ba, sai dai murya kaɗai kuka ji.
13 Il vous a annoncé son alliance, qu'il vous a ordonné d'exécuter, les dix commandements. Il les a écrits sur deux tables de pierre.
Ya furta alkawarinsa gare ku, Dokoki Goma, waɗanda ya umarce ku ku bi, ya kuma rubuta su a alluna biyu.
14 En ce temps-là, Yahvé m'a ordonné de vous enseigner des lois et des ordonnances, afin que vous les mettiez en pratique dans le pays dont vous allez prendre possession.
Sa’an nan Ubangiji ya umarce ni a wannan lokaci, in koya muku ƙa’idodi da dokokin da za ku bi a ƙasar da kuke hayewa Urdun don mallake.
15 Soyez très attentifs, car vous n'avez vu aucune forme le jour où l'Éternel vous a parlé à Horeb, du milieu du feu,
Ba ku ga wata siffa a ranar da Ubangiji ya yi magana da ku a Horeb daga wuta ba. Saboda haka ku lura da kanku sosai,
16 de peur que vous ne vous corrompiez et que vous ne vous fassiez une image taillée, sous la forme d'une figure quelconque, la ressemblance d'un mâle ou d'une femelle,
don kada ku lalace, ku kuma yi wa kanku gunki, siffa ta wani kama, ko a kamannin namiji, ko kuwa ta mace,
17 la ressemblance de tout animal qui est sur la terre, la ressemblance de tout oiseau ailé qui vole dans le ciel,
ko a kamannin wata dabba a duniya, ko na wani tsuntsun da yake tashi a sama,
18 la ressemblance de tout ce qui rampe sur le sol, la ressemblance de tout poisson qui est dans l'eau sous la terre;
ko kuwa a kamannin wata halittar da take rarrafe a ƙasa, ko na wani kifi a cikin ruwaye a ƙarƙashi.
19 et de peur que, levant les yeux vers le ciel, tu ne voies le soleil, la lune et les étoiles, toute l'armée du ciel, et que tu ne te laisses entraîner à les adorer et à les servir, eux que l'Éternel, ton Dieu, a donnés à tous les peuples qui sont sous le ciel entier.
Sa’ad da kuka ɗaga ido kuka kali sama, kuka ga rana da wata, da taurari, da dukan halittun sama, sai ku kula fa, kada ku jarrabtu, ku ce za ku yi musu sujada, ko ku bauta musu; abubuwan nan Ubangiji Allahnku ne ya rarraba wa dukan al’umman da suke ko’ina a ƙarƙashin sararin sama.
20 Mais l'Éternel t'a pris et t'a fait sortir de la fournaise de fer, de l'Égypte, pour être à ses yeux un peuple d'héritage, comme il en est aujourd'hui.
Amma ku, Ubangiji ya ɗauke ku, ya fid da ku daga matuya mai narken ƙarfe, wato, daga Masar, domin ku zama jama’arsa ta musamman kamar yadda kuke a yau.
21 Mais l'Éternel s'est irrité contre moi à cause de vous, et il a juré que je ne passerais pas le Jourdain, et que je n'entrerais pas dans le bon pays que l'Éternel, ton Dieu, te donne en héritage;
Ubangiji ya yi fushi da ni saboda ku, ya kuma yi rantsuwa cewa ba zan haye Urdun, in shiga ƙasan nan mai kyau da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo ba.
22 mais je dois mourir dans ce pays. Je ne passerai pas le Jourdain, mais toi, tu passeras et tu posséderas ce bon pays.
Zan mutu a wannan ƙasa; ba zan haye Urdun ba; amma kuna gab da ƙetarewa, ku mallaki wannan ƙasa mai kyau.
23 Prenez garde que vous n'oubliiez l'alliance de l'Éternel, votre Dieu, qu'il a conclue avec vous, et que vous ne vous fassiez une image taillée en forme de ce que l'Éternel, votre Dieu, vous a interdit.
Ku yi hankali kada ku manta da alkawarin da Ubangiji Allahnku ya yi da ku; kada fa ku yi wa kanku gunki a kamannin wani abin da Ubangiji Allahnku ya hana.
24 Car l'Éternel, ton Dieu, est un feu dévorant, un Dieu jaloux.
Gama Ubangiji Allahnku wuta ne mai ƙuna, Allah ne mai kishi.
25 Lorsque vous aurez engendré des enfants et des enfants d'enfants, que vous aurez séjourné longtemps dans le pays, et que vous vous serez corrompus, que vous vous serez fait une image taillée en forme de quoi que ce soit, et que vous aurez fait ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, votre Dieu, pour l'irriter,
Bayan kun haifi’ya’ya da jikoki, kuka kuma zauna na dogon lokaci a ƙasar, in har kuka lalace, kuka kuma yi wani irin gunki, kuna aikata mugunta a gaban Ubangiji Allahnku, kuna kuma sa shi fushi.
26 j'en prends aujourd'hui à témoin contre vous le ciel et la terre: vous disparaîtrez bientôt du pays dont vous prendrez possession en passant le Jourdain. Vous n'y prolongerez pas vos jours, mais vous serez entièrement détruits.
Yau, na kira sama da duniya, su zama shaidata a kanku. Idan kuka yi rashin biyayya, lalle za ku hallaka nan da nan daga ƙasar da kuke ƙetare Urdun ku gāda. Ba za ku daɗe a cikinta ba, amma za a kawar da ku ƙaƙaf.
27 Yahvé vous dispersera parmi les peuples, et vous resterez peu nombreux parmi les nations où Yahvé vous conduira.
Ubangiji zai watsar da ku a cikin mutane, ɗan kaɗan ne kaɗai za su ragu a cikin al’umman da Ubangiji zai kai ku.
28 Là, vous servirez des dieux, ouvrage de la main de l'homme, bois et pierre, qui ne voient ni n'entendent, ne mangent ni ne sentent.
A can za ku bauta wa allolin da mutum ya yi, na itace da dutse da ba sa gani, ba sa ji, ba sa ci, ba kuma iya sansanawa.
29 Mais de là, tu chercheras Yahvé ton Dieu, et tu le trouveras, si tu le cherches de tout ton cœur et de toute ton âme.
Amma daga can in kuka nemi Ubangiji Allahnku, da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, za ku same shi.
30 Quand tu seras dans l'oppression, et que toutes ces choses t'arriveront, dans la suite des temps, tu reviendras à l'Éternel, ton Dieu, et tu écouteras sa voix.
Sa’ad da kuke cikin wahala saboda waɗannan abubuwan da suka same ku nan gaba, to, sai ku juyo ga Ubangiji Allahnku, ku kuma yi masa biyayya.
31 Car Yahvé ton Dieu est un Dieu de miséricorde. Il ne te laissera pas tomber, ne te détruira pas et n'oubliera pas l'alliance de tes pères qu'il leur a jurée.
Gama Ubangiji Allahnku, Allah ne mai jinƙai; ba zai yashe ku ko yă hallaka, ko kuma yă manta da alkawarin da ya yi da kakanninku, wanda ya tabbatar da su da rantsuwa ba.
32 Car demandez-vous maintenant, parmi les jours passés, qui vous ont précédés, depuis le jour où Dieu a créé l'homme sur la terre, et d'une extrémité du ciel à l'autre, s'il y a eu quelque chose d'aussi grand que cette chose, ou si l'on a entendu quelque chose de semblable?
Ku bincika dukan tarihi mana, tun daga lokacin da Allah ya halicci mutane a cikin duniya har yă zuwa yanzu; ku tantambaya daga wannan kusurwa ta samaniya zuwa waccan, ko wani babban abu irin wannan ya taɓa faruwa, ko kuma an taɓa jin labarin irinsa?
33 Un peuple a-t-il jamais entendu la voix de Dieu parlant du milieu du feu, comme vous l'avez entendue, et vit-il?
Akwai waɗansu mutanen da suka taɓa jin muryar Allah yana magana daga wuta, kamar yadda kuka ji har suka rayu?
34 Ou bien Dieu a-t-il essayé d'aller prendre pour lui une nation au milieu d'une autre nation, par des épreuves, par des signes, par des prodiges, par la guerre, par une main puissante, par un bras étendu, et par de grandes terreurs, selon tout ce que Yahvé ton Dieu a fait pour toi en Égypte, sous tes yeux?
Akwai wani allahn da ya taɓa yin ƙoƙari yă ɗauko wa kansa wata al’umma daga wata al’umma, ta wurin gwaje-gwaje, ta wurin alamu masu banmamaki da al’ajabai, ta wurin yaƙi, ta wurin hannu mai iko, da kuma hannu mai ƙarfi, ko kuwa ta wurin ayyuka masu bangirma da na banmamaki, kamar dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi saboda ku a Masar, a kan idanunku?
35 Cela vous a été montré pour que vous sachiez que Yahvé est Dieu. Il n'y a personne d'autre que lui.
An nuna muku dukan waɗannan abubuwa saboda ku san cewa Ubangiji, shi ne Allah; ban da shi, babu wani.
36 Du haut des cieux, il vous a fait entendre sa voix, pour qu'il vous instruise. Sur la terre, il vous a fait voir son grand feu, et vous avez entendu ses paroles au milieu du feu.
Daga sama ya sa kuka ji muryarsa, don yă hore ku. A duniya ya nuna muku wutarsa mai girma, kuka kuma ji kalmominsa daga wuta.
37 Parce qu'il a aimé vos pères, il a choisi leurs descendants après eux, et il vous a fait sortir d'Égypte par sa présence, par sa grande puissance,
Domin ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓi zuriyarsu a bayansu, ya fitar da ku daga Masar ta wurin kasancewarsa da kuma ƙarfinsa mai girma,
38 pour chasser devant vous des nations plus grandes et plus puissantes que vous, pour vous faire entrer, pour vous donner leur pays en héritage, comme il l'est aujourd'hui.
don yă fitar da ku a gaban al’ummai da suka fi ku girma da kuma ƙarfi, ya kawo ku cikin ƙasarsu, don yă ba ku ita ta zama gādonku, kamar yadda yake a yau.
39 Sachez donc aujourd'hui, et prenez-le à cœur, que Yahvé lui-même est Dieu en haut dans les cieux et en bas sur la terre. Il n'y a personne d'autre.
Ku sani, ku kuma riƙe a zuciya a wannan rana, cewa Ubangiji shi ne Allah a sama da kuma a ƙasa. Babu wani kuma.
40 Tu observeras ses lois et ses commandements que je te prescris aujourd'hui, afin que tout aille bien pour toi et pour tes enfants après toi, et que tu prolonges tes jours dans le pays que Yahvé ton Dieu te donne à perpétuité.
Ku kiyaye ƙa’idodi da umarnai, waɗanda nake ba ku a yau, domin zaman lafiyarku da kuma na zuriyarku bayan ba ku, domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasa wadda Ubangiji Allahnku yake ba ku har abada.
41 Moïse mit à part trois villes au-delà du Jourdain, vers le soleil levant,
Sa’an nan Musa ya keɓe birane uku gabas da Urdun,
42 afin que s'y réfugie le meurtrier qui tue involontairement son prochain et qui ne le haïssait pas autrefois, et qu'en s'enfuyant dans l'une de ces villes, il puisse vivre:
waɗanda duk wanda ya yi kisankai, in ba da gangan ba ne ya kashe maƙwabcinsa, wanda babu ƙiyayya tsakaninsu a dā, zai iya gudu zuwa. Zai iya gudu zuwa cikin ɗaya daga waɗannan birane, yă tsira da ransa.
43 Bezer au désert, dans la plaine, pour les Rubénites; Ramoth en Galaad pour les Gadites; et Golan en Basan pour les Manassites.
Biranen kuwa su ne, Bezer a dutsen hamada, don mutanen Ruben; Ramot Gileyad, don mutanen Gad; da kuma Golan a Bashan, don mutanen Manasse.
44 Telle est la loi que Moïse mit devant les enfants d'Israël.
Wannan ita ce dokar da Musa ya sa a gaban Isra’ilawa.
45 Tels sont les témoignages, les lois et les ordonnances que Moïse adressa aux enfants d'Israël à leur sortie d'Égypte,
Waɗannan su ne farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Musa ya ba su, sa’ad da suka fito daga Masar.
46 de l'autre côté du Jourdain, dans la vallée en face de Beth Peor, au pays de Sihon, roi des Amoréens, qui habitait à Hesbon, et que Moïse et les enfants d'Israël battirent à leur sortie d'Égypte.
Sa’ad da suke a kwari kusa da Bet-Feyor, gabas da Urdun, a ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon, da Musa da Isra’ilawa suka ci da yaƙi sa’ad da suka fito daga Masar.
47 Ils prirent possession de son pays et du pays d'Og, roi de Basan, les deux rois des Amoréens, qui étaient au-delà du Jourdain, vers le soleil levant,
Suka mallaki ƙasarsa da kuma ƙasar Og sarkin Bashan, sarakuna biyu na Amoriyawa, gabas da Urdun.
48 depuis Arœr, qui est sur le bord de la vallée de l'Arnon, jusqu'à la montagne de Sion (appelée aussi Hermon),
Wannan ƙasa ta tashi daga Arower a kewayen Kwarin Arnon zuwa Dutsen Siyon (wato, Hermon),
49 et toute la plaine au-delà du Jourdain, vers l'est, jusqu'à la mer de la plaine, sous les pentes du Pisga.
ya kuma haɗa da dukan Araba gabas da Urdun, har zuwa tekun Araba a gindin gangaren Fisga.

< Deutéronome 4 >