< Deutéronome 34 >

1 Moïse monta des plaines de Moab au mont Nébo, au sommet du Pisga, qui est en face de Jéricho. Yahvé lui montra tout le pays de Galaad jusqu'à Dan,
Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
2 tout Nephtali, le pays d'Éphraïm et de Manassé, et tout le pays de Juda, jusqu'à la mer Occidentale,
da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
3 et le sud, la plaine de la vallée de Jéricho, la ville des palmiers, jusqu'à Zoar.
da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
4 Yahvé lui dit: « Voici le pays que j'ai juré à Abraham, à Isaac et à Jacob, en disant: « Je le donnerai à ta postérité ». Je te l'ai fait voir de tes yeux, mais tu n'y passeras pas. »
Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
5 Et Moïse, serviteur de Yahvé, mourut là, au pays de Moab, selon la parole de Yahvé.
Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
6 Il fut enterré dans la vallée du pays de Moab, en face de Beth Peor, mais personne ne sait encore aujourd'hui où se trouve sa tombe.
Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
7 Moïse était âgé de cent vingt ans lorsqu'il mourut. Son œil ne s'était pas affaibli, et sa force n'avait pas disparu.
Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
8 Les enfants d'Israël pleurèrent Moïse dans les plaines de Moab pendant trente jours, jusqu'à ce que les jours de deuil de Moïse fussent terminés.
Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
9 Josué, fils de Nun, était rempli de l'esprit de sagesse, car Moïse avait posé ses mains sur lui. Les enfants d'Israël l'écoutèrent et firent ce que l'Éternel avait ordonné à Moïse.
To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
10 Depuis lors, il n'a pas paru en Israël de prophète semblable à Moïse, que l'Éternel a connu face à face,
Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
11 par tous les signes et les prodiges que l'Éternel l'a envoyé faire au pays d'Égypte, à Pharaon, à tous ses serviteurs et à tout son pays,
wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
12 par toute la puissance de sa main et par toutes les merveilles qu'il a faites aux yeux de tout Israël.
Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.

< Deutéronome 34 >