< Deutéronome 20 >
1 Lorsque tu sortiras pour combattre tes ennemis, et que tu verras des chevaux, des chars et un peuple plus nombreux que toi, tu ne les craindras pas, car l'Éternel, ton Dieu, qui t'a fait monter du pays d'Égypte, est avec toi.
Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, kuka ga dawakai da kekunan yaƙi da kuma mayaƙan da suka fi ku yawa, kada ku ji tsoronsu, domin Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar zai kasance tare da ku.
2 Lorsque vous approcherez de la bataille, le prêtre s'approchera et parlera au peuple,
Sa’ad da kuke gab da kama yaƙi, sai firist yă zo gaba yă yi wa mayaƙan jawabi.
3 et il lui dira: « Écoute, Israël, tu t'approches aujourd'hui de la bataille contre tes ennemis. Que ton cœur ne s'affaiblisse pas! N'aie pas peur, ne tremble pas et n'aie pas peur d'eux;
Zai ce, “Ku ji, ya Isra’ila, yau kuna gab da kama da abokan gābanku. Kada ku karai, ko ku ji tsoro; kada ku firgita, ko ku yi rawar jiki a gabansu.
4 car Yahvé ton Dieu est celui qui marche avec toi, pour combattre pour toi contre tes ennemis, pour te sauver. »
Gama Ubangiji Allahnku, yana tafe tare da ku, zai yaƙi abokan gābanku dominku, yă ba ku nasara.”
5 Les officiers parleront au peuple, en disant: « Quel est l'homme qui a construit une maison neuve et qui ne l'a pas consacrée? Qu'il aille et retourne dans sa maison, de peur qu'il ne meure dans la bataille et qu'un autre ne la dédie.
Hafsoshi za su ce wa mayaƙa, “Ko akwai wanda ya gina sabon gida bai kuma buɗe shi ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă buɗe shi.
6 Quel est l'homme qui a planté une vigne, et qui n'en a pas utilisé le fruit? Qu'il s'en aille et retourne dans sa maison, de peur qu'il ne meure dans la bataille, et qu'un autre n'en utilise le fruit.
Ko akwai wani da ya shuka inabi, bai kuwa fara jin daɗinsa ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă ji daɗinsa.
7 Quel est l'homme qui s'est engagé à épouser une femme, et qui ne l'a pas prise? Qu'il aille et retourne dans sa maison, de peur qu'il ne meure dans la bataille et qu'un autre homme ne la prenne. »
Ko akwai wani da aka yi masa alkawarin mata, bai kuwa aure ta ko ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă aure ta.”
8 Les officiers parleront encore au peuple, et ils diront: « Quel est l'homme qui a peur et qui est pusillanime? Qu'il s'en aille et retourne dans sa maison, de peur que le cœur de son frère ne se fonde comme son cœur. »
Sa’an nan hafsoshin za su ƙara da cewa, “Ko akwai wani da yake tsoro, ko ya karai? Bari yă tafi gida don kada’yan’uwansa su karai su ma.”
9 Lorsque les officiers auront fini de parler au peuple, ils nommeront des chefs d'armée à la tête du peuple.
Sa’ad da hafsoshin suka gama magana da mayaƙan, sai su naɗa komandodi a kansu.
10 Lorsque vous vous approchez d'une ville pour la combattre, annoncez-lui la paix.
Sa’ad da kuka haura don ku fāɗa wa birni, sai ku fara neman garin da salama.
11 Si elle te donne une réponse de paix et s'ouvre à toi, tous les habitants qui s'y trouvent deviendront tes travailleurs forcés et te serviront.
In sun yarda da salamar, suka buɗe ƙofofin garinsu, to, sai dukan mutanen da suke cikinsa su yi muku aikin gandu, su kuma yi muku aiki.
12 S'il ne veut pas faire la paix avec toi, mais te faire la guerre, tu l'assiégeras.
In kuwa suka ƙi salamar, suka fāɗa muku da yaƙi, sai ku yi wa wannan birni ƙawanya.
13 Lorsque Yahvé, ton Dieu, la livrera entre tes mains, tu en frapperas tous les mâles du tranchant de l'épée.
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba da shi cikin hannunku, sai ku kashe dukan mazan da suke cikinsa da takobi.
14 Mais tu prendras pour toi les femmes, les petits enfants, le bétail, tout ce qui se trouve dans la ville et tout son butin. Tu pourras utiliser le butin de tes ennemis, que Yahvé ton Dieu t'a donné.
Game da mata, yara, dabbobi da kuma sauran abubuwan da suke cikin birnin, za ku iya kwasa waɗannan a matsayin ganima wa kanku. Za ku kuma yi amfani da ganimar da Ubangiji Allahnku ya ba ku daga abokan gābanku.
15 Tu feras ainsi à toutes les villes qui sont très éloignées de toi et qui ne font pas partie des villes de ces peuples.
Haka za ku yi da dukan biranen da suke nesa da ku, waɗanda kuma ba na al’ummai da suke kusa ba.
16 Mais parmi les villes de ces peuples que l'Éternel, ton Dieu, te donne en héritage, tu ne sauveras rien de ce qui respire,
Amma fa, a cikin biranen al’ummai da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kada ku bar wani abu mai numfashi da rai.
17 mais tu les dévoueras par interdit, le Héthien, l'Amoréen, le Cananéen, le Phérézien, le Hévien et le Jébusien, comme l'Éternel, ton Dieu, te l'a ordonné,
Ku hallaka su ƙaƙaf, wato, Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa, yadda Ubangiji Allahnku ya umarce ku.
18 afin qu'ils ne t'apprennent pas à suivre toutes leurs abominations, qu'ils ont faites pour leurs dieux, et que tu ne pèches pas contre l'Éternel, ton Dieu.
In ba haka ba, za su koya muku ku bi dukan abubuwan banƙyaman da suke yi, ta yin sujada wa allolinsu, ta haka kuwa ku yi wa Ubangiji Allahnku zunubi.
19 Lorsque tu assiégeras une ville pendant une longue période, en lui faisant la guerre pour la prendre, tu ne détruiras pas ses arbres en maniant la hache contre eux, car tu pourras en manger. Tu ne les couperas pas, car l'arbre des champs est-il un homme, pour que tu l'assailles?
Sa’ad da kuka yi wa birni ƙawanya kuka daɗe, kuka yi ta yaƙi don ku ci shi, kada ku sassare itatuwansa da gatari, domin za ku ci’ya’yansu. Kada ku sassare su. Gama itatuwan da suke cikin gonaki, ba mutane ne da za ku yi musu ƙawanya?
20 Seuls les arbres dont tu sais qu'ils ne sont pas destinés à la nourriture, tu les détruiras et tu les couperas. Tu construiras des remparts contre la ville qui te fait la guerre, jusqu'à ce qu'elle tombe.
Amma fa, za ku iya sassare itatuwan da kuka sani ba sa ba da’ya’ya, ku kuma yi amfani da su don ayyukan gina ƙawanyar, sai an ci birnin da yaƙi.