< Deutéronome 2 >

1 Puis nous nous tournâmes, et nous partîmes pour le désert, par le chemin de la mer Rouge, comme l'Éternel me l'avait dit, et nous encerclâmes la montagne de Séir pendant plusieurs jours.
Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
2 L'Éternel m'a parlé, en disant:
Sai Ubangiji ya ce mini,
3 « Tu as assez longtemps encerclé cette montagne. Tourne-toi vers le nord.
“Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
4 Tu donneras cet ordre au peuple: « Vous allez traverser la frontière de vos frères, les enfants d'Ésaü, qui habitent en Séir, et ils auront peur de vous. Soyez donc prudents.
Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
5 Ne vous disputez pas avec eux, car je ne vous donnerai aucune de leurs terres, pas même pour que la plante du pied les foule, car j'ai donné la montagne de Séir en propriété à Ésaü.
kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
6 Tu achèteras d'eux, à prix d'argent, des aliments que tu pourras manger. Tu leur achèteras aussi de l'eau à prix d'argent, pour que tu puisses boire.'"
Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
7 Car Yahvé ton Dieu t'a béni dans tout le travail de tes mains. Il a connu ta marche dans ce grand désert. Ces quarante années, Yahvé ton Dieu a été avec toi. Tu n'as manqué de rien.
Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
8 Et nous passâmes à côté de nos frères, les fils d'Ésaü, qui habitent en Séir, par le chemin de la plaine d'Elath et d'Ezion Geber. Nous nous tournâmes et passâmes par le chemin du désert de Moab.
Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
9 Yahvé m'a dit: « N'importune pas Moab et ne te bats pas avec lui, car je ne te donnerai aucune de ses terres en propriété, comme j'ai donné Ar en propriété aux enfants de Lot. »
Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
10 (Les Emim y habitaient auparavant, peuple grand et nombreux, et de taille égale à celle des Anakim.
(Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
11 Ceux-ci aussi sont considérés comme des Rephaïm, comme les Anakim; mais les Moabites les appellent Emim.
Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
12 Les Horites habitaient aussi autrefois en Séir, mais les fils d'Ésaü leur succédèrent. Ils les détruisirent devant eux et habitèrent à leur place, comme Israël l'a fait pour le pays qu'il possédait et que Yahvé leur avait donné).
Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
13 « Maintenant, lève-toi et traverse le torrent de Zered. » Nous avons traversé le ruisseau Zered.
Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
14 Les jours que nous fîmes depuis Kadès-Barnéa jusqu'au passage du torrent de Zéred furent de trente-huit ans, jusqu'à ce que toute la génération des hommes de guerre eût disparu du milieu du camp, comme l'avait juré l'Éternel.
Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
15 Et la main de l'Éternel fut contre eux, pour les détruire depuis le milieu du camp, jusqu'à ce qu'ils eussent disparu.
Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
16 Lorsque tous les hommes de guerre furent consumés et morts parmi le peuple,
To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
17 l'Éternel me parla, et dit:
sai Ubangiji ya ce mini,
18 « Tu passeras aujourd'hui par Ar, la frontière de Moab.
“Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
19 Quand tu approcheras de la frontière des enfants d'Ammon, ne les importune pas et ne leur cherche pas querelle, car je ne te donnerai aucune possession du pays des enfants d'Ammon, puisque je l'ai donné en possession aux enfants de Lot. »
Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
20 (Cela aussi est considéré comme un pays de Rephaïm. Les Rephaïm y habitaient autrefois, mais les Ammonites les appellent Zamzummim,
(Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
21 un peuple grand, nombreux et de haute taille, comme les Anakim; mais Yahvé les détruisit de devant Israël, et ils leur succédèrent et habitèrent à leur place,
Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
22 comme il fit pour les fils d'Ésaü qui habitent en Séir, lorsqu'il détruisit de devant eux les Horites; et ils leur succédèrent et habitèrent à leur place jusqu'à ce jour.
Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
23 Puis les Avvim, qui habitaient des villages jusqu'à Gaza: les Caphtorim, sortis de Caphtor, les détruisirent et habitèrent à leur place).
Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
24 « Lève-toi, pars, et franchis le torrent de l'Arnon. Voici, j'ai livré entre tes mains Sihon, l'Amoréen, roi de Hesbon, et son pays; commence à le posséder, et livre bataille contre lui.
“Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
25 Aujourd'hui, je commencerai à mettre l'épouvante et la crainte de toi sur les peuples qui sont sous tout le ciel, qui entendront parler de toi, et qui trembleront et seront dans l'angoisse à cause de toi. »
A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
26 Du désert de Kedemoth, j'envoyai des messagers à Sihon, roi de Hesbon, avec des paroles de paix, en disant:
Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
27 « Laisse-moi passer par ton pays. Je passerai par la route. Je ne me tournerai ni à droite ni à gauche.
“Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
28 Tu me vendras à prix d'argent de la nourriture, pour que je mange, et tu me donneras à prix d'argent de l'eau, pour que je boive. Laissez-moi seulement passer sur mes pieds,
Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
29 comme m'ont traité les enfants d'Ésaü qui habitent en Séir et les Moabites qui habitent à Ar, jusqu'à ce que je passe le Jourdain pour entrer dans le pays que Yahvé notre Dieu nous donne. »
kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
30 Mais Sihon, roi de Heshbon, ne voulut pas nous laisser passer devant lui, car Yahvé ton Dieu avait endurci son esprit et rendu son cœur obstiné, afin de le livrer entre tes mains, comme c'est le cas aujourd'hui.
Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
31 Yahvé me dit: « Voici, j'ai commencé à livrer Sihon et son pays devant toi. Commence à le posséder, pour que tu hérites de son pays. »
Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
32 Alors Sihon sortit contre nous, lui et tout son peuple, pour combattre à Jahaz.
Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
33 Yahvé notre Dieu le livra devant nous, et nous le frappâmes, lui, ses fils et tout son peuple.
sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
34 Nous prîmes alors toutes ses villes, et nous dévouâmes par interdit toutes les villes habitées, avec les femmes et les petits enfants. Nous n'avons laissé personne en vie.
A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
35 Nous ne prîmes pour nous que le bétail, avec le butin des villes que nous avions prises.
Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
36 Depuis Arœr, qui est au bord du torrent de l'Arnon, et la ville qui est dans la vallée, jusqu'à Galaad, il n'y avait pas de ville trop élevée pour nous. Yahvé notre Dieu a tout livré devant nous.
Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
37 Seulement, au pays des enfants d'Ammon, vous ne vous êtes pas approchés: toutes les rives du fleuve Jabbok, les villes de la montagne, et partout où Yahvé notre Dieu nous l'a interdit.
Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.

< Deutéronome 2 >