< Deutéronome 18 >

1 Les prêtres et les lévites - toute la tribu de Lévi - n'auront ni part ni héritage avec Israël. Ils mangeront les offrandes consumées par le feu de l'Éternel et sa part.
Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
2 Ils n'auront pas d'héritage parmi leurs frères. C'est Yahvé qui est leur héritage, comme il le leur a dit.
Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
3 Voici ce que les prêtres recevront du peuple, de ceux qui offrent un sacrifice, qu'il s'agisse d'un bœuf ou d'un mouton, et qu'ils donneront au prêtre: l'épaule, les deux joues et les parties intérieures.
To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
4 Tu lui donneras les prémices de ton blé, de ton vin nouveau et de ton huile, et les premières toisons de tes brebis.
Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
5 Car Yahvé ton Dieu l'a choisi parmi toutes tes tribus pour qu'il se tienne debout et fasse le service au nom de Yahvé, lui et ses fils pour toujours.
Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
6 Si un Lévite vient de l'une de vos portes, de tout Israël où il habite, et s'il vient avec tout le désir de son âme au lieu que l'Éternel choisira,
Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
7 il fera le service au nom de l'Éternel, son Dieu, comme tous ses frères les Lévites, qui se tiennent là devant l'Éternel.
Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
8 Ils auront des portions identiques à manger, en plus de ce qui provient de la vente des biens de sa famille.
Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
9 Lorsque tu seras entré dans le pays que Yahvé ton Dieu te donne, tu n'apprendras pas à imiter les abominations de ces nations.
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
10 Il ne se trouvera pas chez toi quelqu'un qui fasse passer son fils ou sa fille par le feu, quelqu'un qui pratique la divination, quelqu'un qui dise la bonne aventure, ou un enchanteur, ou un magicien,
Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
11 ou un charmeur, ou quelqu'un qui consulte un esprit familier, ou un magicien, ou un nécromancien.
ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
12 Car quiconque fait ces choses est en abomination à Yahvé. A cause de ces abominations, Yahvé ton Dieu les chasse de devant toi.
Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
13 Tu seras irréprochable devant Yahvé ton Dieu.
Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
14 Car ces nations que tu vas déposséder écoutent ceux qui pratiquent la sorcellerie et les devins; mais toi, l'Éternel, ton Dieu, ne te permet pas de le faire.
Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
15 L'Éternel, ton Dieu, te suscitera un prophète du milieu de toi, parmi tes frères, comme moi. Tu l'écouteras.
Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
16 Ceci est conforme à tout ce que tu as demandé à l'Éternel, ton Dieu, à Horeb, le jour de l'assemblée, en disant: « Que je n'entende plus la voix de l'Éternel, mon Dieu, et que je ne voie plus ce grand feu, afin que je ne meure pas. »
Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
17 Yahvé me dit: « Ils ont bien dit ce qu'ils ont dit.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
18 Je leur susciterai un prophète du milieu de leurs frères, comme toi. Je mettrai mes paroles dans sa bouche, et il leur dira tout ce que je lui commanderai.
Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
19 Quiconque n'écoutera pas les paroles qu'il prononcera en mon nom, je le lui demanderai.
Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
20 Mais le prophète qui prononcera en mon nom une parole présomptueuse que je ne lui aurai pas ordonné de prononcer, ou qui parlera au nom d'autres dieux, ce même prophète mourra. »
Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
21 Vous pouvez dire en votre cœur: « Comment connaîtrons-nous la parole que l'Éternel n'a pas prononcée? »
Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
22 Lorsqu'un prophète parle au nom de l'Éternel, si la chose ne suit pas, ni n'arrive, c'est la chose que l'Éternel n'a pas dite. Le prophète a parlé de manière présomptueuse. Vous ne devez pas avoir peur de lui.
In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.

< Deutéronome 18 >