< Deutéronome 11 >

1 C'est pourquoi tu aimeras l'Éternel, ton Dieu, et tu observeras toujours ses instructions, ses lois, ses ordonnances et ses commandements.
To, sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kullum ku kuma kiyaye abubuwan da yake bukata, ku kiyaye ƙa’idodinsa, dokokinsa da kuma umarnansu.
2 Sachez aujourd'hui, car je ne parle pas à vos enfants qui n'ont pas connu et qui n'ont pas vu le châtiment de l'Éternel, votre Dieu, sa grandeur, sa main puissante, son bras étendu,
Ku tuna a yau, cewa’ya’yanku ba su ne suka gani suka kuma ɗanɗana horon Ubangiji Allahnku ba; ba su suka gani girmansa, hannunsa mai ƙarfi, hannunsa mai iko;
3 ses signes et ses œuvres, qu'il a faits au milieu de l'Égypte à Pharaon, roi d'Égypte, et à tout son pays,
alamun da ya aikata da abubuwan da ya yi a cikin Masar, ga Fir’auna sarkin Masar da kuma ga dukan ƙasarsa ba;
4 et ce qu'il a fait à l'armée d'Égypte, à ses chevaux et à ses chars; comment il a fait déborder les eaux de la mer Rouge pendant qu'ils vous poursuivaient, et comment Yahvé les a détruits jusqu'à ce jour;
ba su suka gani abin da ya yi wa mayaƙan Masar, da dawakansu da keken yaƙinsu, yadda ya sha kansu da ruwan Jan Teku yayinda suke bin ku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf ba.
5 et ce qu'il vous a fait dans le désert jusqu'à ce que vous arriviez en ce lieu;
Ba’ya’yanku ba ne suka gani abin da ya yi dominku a hamada har sai da kuka kai wannan wuri ba,
6 et ce qu'il a fait à Dathan et Abiram, fils d'Eliab, fils de Ruben, comment la terre a ouvert sa bouche et les a engloutis, avec leurs maisons, leurs tentes et tout ce qui vivait à leur suite, au milieu de tout Israël;
ba su ba ne suka gani abin da ya yi ga Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab mutumin Ruben, sa’ad da ƙasa ta buɗe bakinta a tsakiyar dukan Isra’ila ta haɗiye su tare da gidajensu, tentunansu da kowane abu mai rai da yake nasu ba.
7 mais tes yeux ont vu toute la grandeur de l'œuvre de Yahvé.
Amma idanunku ne suka ga dukan waɗannan manyan abubuwan da Ubangiji ya yi.
8 Tu observeras donc tout le commandement que je te prescris aujourd'hui, afin que tu sois fort, que tu entres en possession du pays dont tu vas prendre possession,
Saboda haka sai ku kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, don ku sami ƙarfin da za ku shiga, ku kuma karɓi ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaka,
9 et que tu prolonges tes jours dans le pays que Yahvé a juré à tes pères de leur donner, à eux et à leur postérité, un pays où coulent le lait et le miel.
domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su da zuriyarsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
10 Car le pays dont tu vas entrer en possession n'est pas comme le pays d'Égypte d'où tu es sorti, où tu as semé ta semence et arrosé de ton pied, comme un jardin d'herbes aromatiques;
Ƙasar da kuke shiga, ku karɓa, ba kamar ƙasar Masar ba ce, inda kuka fito, inda kuka shuka iri, ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu.
11 mais le pays dont tu vas entrer en possession est un pays de collines et de vallées qui boit l'eau de la pluie du ciel,
Amma ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaki, ƙasa ce ta duwatsu da kwaruruka wadda ruwan sama ne yake jiƙe ta.
12 un pays dont Yahvé ton Dieu prend soin. L'Éternel, ton Dieu, a toujours les yeux sur lui, depuis le début de l'année jusqu'à la fin de l'année.
Ƙasa ce da Ubangiji Allahnku yake lura da ita; idanun Ubangiji Allahnku yana a kai daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta.
13 Si tu écoutes attentivement les commandements que je te prescris aujourd'hui, si tu aimes l'Éternel, ton Dieu, et si tu le sers de tout ton cœur et de toute ton âme,
Saboda haka in kun yi biyayya ga umarnan da nake ba ku a yau cikin aminci, kuna ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna kuma bauta masa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
14 je donnerai à ton pays la pluie en son temps, la pluie de l'aube et la pluie de l'arrière-saison, pour que tu recueilles ton blé, ton moût et ton huile.
sai in aika da ruwan sama a ƙasarku a lokacinsa, ruwan saman bazara da kuma na kaka, don ku tattara hatsinku, sabon inabinku da kuma manku.
15 Je donnerai de l'herbe dans tes champs pour ton bétail, et tu mangeras et te rassasieras.
Zan tanadar da ciyawa a filaye don shanunku, za ku ci, ku kuma ƙoshi.
16 Prends garde que ton cœur ne se laisse tromper, et que tu ne te détournes pour servir d'autres dieux et te prosterner devant eux;
Ku yi hankali, kada a ruɗe ku har ku bauta wa alloli, ku kuma yi musu sujada,
17 et que la colère de l'Éternel ne s'enflamme contre toi, qu'il ne ferme le ciel, qu'il n'y ait pas de pluie, que la terre ne donne pas son fruit, et que tu ne périsses rapidement du bon pays que l'Éternel te donne.
don kada fushin Ubangiji yă ƙuna a kanku, yă rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.
18 C'est pourquoi tu garderas ces paroles que je te dis dans ton cœur et dans ton âme. Tu les lieras comme un signe sur ta main, et elles seront comme des fronteaux entre tes yeux.
Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.
19 Tu les enseigneras à tes enfants, et tu en parleras quand tu seras assis dans ta maison, quand tu iras en chemin, quand tu te coucheras et quand tu te lèveras.
Ku koyar da su ga’ya’yanku, ku yi ta haddace su, sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
20 Tu les écriras sur les montants de ta maison et sur tes portes,
Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,
21 afin que tes jours et les jours de tes enfants soient multipliés dans le pays que l'Éternel a juré à tes pères de leur donner, comme les jours des cieux au-dessus de la terre.
saboda kwanakinku da kwanakin’ya’yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, muddin sama tana bisa duniya.
22 En effet, si tu observes tous les commandements que je te prescris, si tu les mets en pratique, si tu aimes Yahvé ton Dieu, si tu marches dans toutes ses voies et si tu t'attaches à lui,
In kuka lura, kuka kuma kiyaye dukan umarnai da nake ba ku, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma riƙe shi gam,
23 alors Yahvé chassera toutes ces nations devant toi, et tu déposséderas des nations plus grandes et plus puissantes que toi.
Ubangiji zai kori dukan waɗannan al’ummai a gabanku, za ku kuma kore al’umman da suka fi ku yawa da ƙarfi.
24 Tout lieu que foulera la plante de ton pied sera à toi: depuis le désert et le Liban, depuis le fleuve, l'Euphrate, jusqu'à la mer occidentale, ce sera ta frontière.
Duk inda tafin ƙafanku ya taka, zai zama naku; iyakarku zai kama daga hamadan Lebanon da kuma daga Kogin Yuferites zuwa Bahar Rum.
25 Aucun homme ne pourra se tenir devant toi. L'Éternel, ton Dieu, fera régner la crainte et l'effroi sur tout le pays que tu fouleras, comme il te l'a dit.
Babu mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku, zai sa razana da tsoronku a dukan ƙasar, a duk inda kuka tafi, kamar yadda ya alkawarta muku.
26 Voici, je mets aujourd'hui devant toi une bénédiction et une malédiction:
Ga shi, a yau, ina sa a gabanku albarka da kuma la’ana,
27 la bénédiction, si tu écoutes les commandements de l'Éternel, ton Dieu, que je te prescris aujourd'hui;
albarka in kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, da nake ba ku;
28 et la malédiction, si tu n'écoutes pas les commandements de l'Éternel, ton Dieu, et si tu te détournes de la voie que je te prescris aujourd'hui, pour aller après d'autres dieux que tu n'as pas connus.
la’ana in ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma juya daga hanyar da na umarce ku, ta wurin bin waɗansu alloli, waɗanda ba ku sani ba.
29 Lorsque Yahvé ton Dieu te fera entrer dans le pays dont tu vas prendre possession, tu placeras la bénédiction sur le mont Gerizim et la malédiction sur le mont Ebal.
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da za ku shiga ku ci gādonta, sai ku yi shelar albarkun nan a dutsen Gerizim, ku kuma yi na la’ana a dutsen Ebal.
30 Ne sont-ils pas de l'autre côté du Jourdain, derrière le chemin du soleil couchant, dans le pays des Cananéens qui habitent la plaine, près de Gilgal, à côté des chênes de Moreh?
Waɗannan duwatsu biyu suna a hayin Urdun, yamma da hanya a ƙasar Kan’aniyawa mazaunan Araba, kusa da Gilgal wajajen manyan itatuwan More.
31 Car vous allez passer le Jourdain pour entrer en possession du pays que Yahvé votre Dieu vous donne, vous le posséderez et vous y habiterez.
Kuna gab da ƙetare Urdun fa, ku shiga, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa’ad da kuka karɓe ta, kuka kuma zauna a can,
32 Tu observeras et tu mettras en pratique toutes les lois et les ordonnances que je mets aujourd'hui devant toi.
ku tabbata kun yi biyayya da dukan ƙa’idodi, da kuma dokokin da nake sawa a gabanku a yau.

< Deutéronome 11 >