< Daniel 8 >

1 La troisième année du règne du roi Belschatsar, une vision m'apparut, à moi, Daniel, après celle qui m'était apparue la première fois.
A shekara ta uku ta mulkin sarki Belshazar, ni, Daniyel, na ga wahayi, bayan wancan da na riga gani.
2 Je vis la vision. Or, lorsque j'ai eu la vision, j'étais dans la citadelle de Suse, qui est dans la province d'Élam. Je vis dans la vision, et je me trouvais près du fleuve d'Ulai.
A cikin wahayin, na ga kaina a mafakar Shusha a yankin Elam; a wahayin na ga ina a bakin Kogin Ulai.
3 Alors je levai les yeux et je regardai, et voici, un bélier qui avait deux cornes se tenait devant le fleuve. Les deux cornes étaient hautes, mais l'une était plus haute que l'autre, et la plus haute montait la dernière.
Na ɗaga ido, a gabana kuwa sai ga rago mai ƙahoni biyu, yana tsaye a gefen mashigin kogin, ƙahonin kuma suna da tsawo. Ɗaya daga cikin ƙahonin ya fi ɗayan tsawo. Wanda ya fi tsawon shi ne ya tsiro daga baya.
4 Je vis le bélier qui poussait vers l'ouest, vers le nord et vers le sud. Aucun animal ne pouvait se dresser devant lui. Il n'y avait personne qui pût délivrer de sa main, mais il faisait ce qu'il voulait, et il se glorifiait.
Na lura da ragon sa’ad da ya kai karo wajen yamma da arewa da kudu. Babu wata dabbar da ta iya ƙarawa da shi, babu kuma wanda ya iya kuɓuta daga ikonsa. Ya yi yadda ya ga dama, ya kuma zama mai girma.
5 Comme je considérais, voici qu'un bouc vint de l'ouest sur la surface de toute la terre, et ne toucha pas le sol. Le bouc avait une corne remarquable entre les yeux.
Yayinda nake tunani game da wannan, farat ɗaya sai ga bunsurun da yake da sanannen ƙaho tsakanin idanunsa ya ɓullo daga wajen yamma, yana ratsa dukan duniya ba ya ko taɓa ƙasa.
6 Il s'approcha du bélier aux deux cornes, que je voyais debout devant le fleuve, et se précipita sur lui dans la fureur de sa puissance.
Ya zo wajen rago mai ƙahoni biyu ɗin nan da na riga na gani tsaye a gefen mashigin kogin nan ya tasar masa da fushi mai zafi.
7 Je l'ai vu s'approcher du bélier, et il s'est mis en colère contre lui; il a frappé le bélier et lui a brisé les deux cornes. Le bélier n'avait pas la force de se tenir devant lui, mais il le jeta à terre et le piétina. Il n'y avait personne qui pût délivrer le bélier de sa main.
Na ga ya zo kusa da ragon, ya husata da shi ƙwarai, ya kai wa ragon hari. Ya kakkarya ƙahoninsa nan biyu. Ƙarfin ragon ya kāsa, bai iya kāre kansa daga bunsurun ba. Bunsurun ya buge shi ƙasa ya tattake shi. Ba wanda ya iya ceton ragon daga bunsurun.
8 Le bouc s'éleva à un haut degré d'orgueil. Quand il fut fort, la grande corne se brisa, et à sa place s'élevèrent quatre grandes cornes vers les quatre vents du ciel.
Bunsurun kuwa ya ƙasaita, amma a ƙwanƙolin ikonsa sai aka karye babban ƙahonsa, kuma a wurin da ƙahon nan ya kasance waɗansu sanannun ƙahoni huɗu suka tsiro suna fuskantar kusurwoyin nan huɗu.
9 De l'une d'elles sortit une petite corne, qui devint extrêmement grande, vers le midi, vers l'orient, et vers le pays glorieux.
Daga cikin ɗayansu kuma wani ƙaramin ƙaho ya fito, ya yi girma ya ƙasaita ƙwarai zuwa kudu da kuma gabas da wajen Kyakkyawar Ƙasa.
10 Elle s'éleva jusqu'à l'armée du ciel; elle jeta à terre une partie de l'armée et des étoiles, et les foula aux pieds.
Ya yi girma sai da ya kai rundunar sammai, ya kuma fid da waɗansu rundunar taurari zuwa ƙasa ya kuma tattake su.
11 Elle s'éleva jusqu'au chef de l'armée; elle lui enleva l'holocauste perpétuel, et le lieu de son sanctuaire fut renversé.
Sai ya ɗora kansa ya zama mai girma kamar Sarkin runduna; sai aka ɗauke hadaya ta kullayaumi daga gare shi, aka kuma saukar da wurin masujadarsa ƙasa.
12 L'armée lui fut livrée, ainsi que l'holocauste perpétuel, par la désobéissance. Il a jeté la vérité par terre, et il a fait sa volonté et a prospéré.
Saboda tawaye, sai aka ba da rundunar tsarkaka da kuma hadayar ƙonawa ta kowace rana ga ƙahon. Sai ya yi watsi da gaskiya, ya yi abin da ya ga dama, ya kuwa yi nasara.
13 Alors j'entendis un saint qui parlait; et un autre saint dit à celui qui parlait: « Jusqu'à quand durera la vision concernant l'holocauste perpétuel, et la désobéissance qui désole, pour que le sanctuaire et l'armée soient foulés aux pieds? »
Sa’an nan na ji mai tsarkin nan yana magana, wani mai tsarki kuma ya ce da wancan, “Har yaushe wannan wahayi zai tabbata, wahayi game da hadaya ta kullayaumi, da tawayen da yake kawo lalacewa, da kuma miƙa wuri mai tsarki da kuma na rundunar da za a tattake a ƙarƙashin sawu?”
14 Il me dit: « Jusqu'à deux mille trois cents soirs et matins. Alors le sanctuaire sera purifié. »
Sai ya ce mini, “Zai ɗauki safiya da yamma 2,300; sa’an nan za a sāke tsarkake wuri mai tsarki.”
15 Lorsque moi, Daniel, j'eus vu la vision, je cherchai à la comprendre. Et voici que se tenait devant moi quelqu'un qui avait l'apparence d'un homme.
Yayinda ni, Daniyel, nake duban wahayi ina ƙoƙari in fahimce shi, sai ga wani a gabana wanda ya yi kama da mutum.
16 Entre les rives de l'Oulaï, j'entendis la voix d'un homme qui appelait et disait: « Gabriel, fais comprendre la vision à cet homme. »
Sai na ji muryar wani mutum daga Ulai tana cewa, “Jibra’ilu, faɗa wa wannan mutum ma’anar wahayin.”
17 Il s'approcha donc de l'endroit où je me tenais; quand il arriva, j'eus peur et je tombai sur ma face; mais il me dit: « Comprends, fils d'homme, car la vision appartient au temps de la fin. »
Da ya zo kusa da inda nake tsaye, na firgita na kuma fāɗi rubda ciki. Ya ce da ni “Ɗan mutum, ka gane da cewa wannan wahayi yana magana ne a kan kwanakin ƙarshe.”
18 Comme il me parlait, je tombai dans un profond sommeil, le visage contre terre, mais il me toucha et me redressa.
Yayinda yake magana da ni, barci mai nauyi ya kwashe ni, da nake kwance rubda ciki. Sai ya taɓa ni ya kuma tashe ni tsaye.
19 Il dit: « Voici, je vais te faire connaître ce qui arrivera au dernier moment de la colère, car cela appartient au temps fixé de la fin.
Sai ya ce, “Zan faɗa maka abin da zai faru a lokacin fushi, saboda wahayin yana magana ne a kan lokacin da aka ƙayyade na ƙarshe.
20 Le bélier que tu as vu, qui avait deux cornes, ce sont les rois de Médie et de Perse.
Rago mai ƙahoni biyu da ka gani, yana a madadin sarakunan Medes da Farisa ne.
21 Le bouc rude, c'est le roi de Grèce. La grande corne qui est entre ses yeux, c'est le premier roi.
Bunsurun kuwa sarkin Girka ne, kuma babban ƙahon da yake tsakanin idanunsa, sarki na farko ne.
22 Quant à ce qui a été brisé, à la place où quatre se sont levés, quatre royaumes se lèveront de la nation, mais non avec sa puissance.
Ƙahoni huɗu da suka maya wannan da ya karye yana a madadin masarautu huɗu da za su tashi daga cikin al’ummarsa amma ba za su sami irin ikonsa ba.
23 « Au dernier temps de leur règne, quand les transgresseurs seront au comble, se lèvera un roi à la face farouche, et qui comprendra des énigmes.
“Can wajen ƙarshe mulkinsu, sa’ad da muguntarsu ta kai intaha, wani mugun sarki mai rashin hankali, uban makirci, zai fito.
24 Sa puissance sera grande, mais non par sa propre force. Il fera des ravages et prospérera dans ce qu'il fera. Il détruira les puissants et le peuple saint.
Zai yi ƙarfi ƙwarai da gaske, amma ba da ikonsa ba. Zai jawo mummunar hallakarwa kuma zai yi nasara a duk abin da ya sa gaba. Zai hallakar da majiya ƙarfi da kuma tsarkaka.
25 Par sa politique, il fera prospérer la tromperie dans sa main. Il se glorifiera dans son cœur, et il détruira beaucoup de gens dans leur sécurité. Il se dressera aussi contre le prince des princes, mais il sera brisé sans mains humaines.
Zai sa yaudara ta ƙara yin yawa, zai ɗaukaka kansa. Sa’ad da suke ji sun sami mafaka, zai hallaka mutane da yawa sa’an nan kuma yă fara gāba da Sarkin sarakuna. Duk da haka za a hallaka shi, amma ba da ikon mutum ba.
26 « La vision des soirs et des matins qui a été racontée est vraie; mais scellez la vision, car elle concerne de nombreux jours à venir. »
“Wahayin nan na safiya da yamma da aka nuna maka gaskiya ne, amma ka ɓoye wahayin, gama ya shafi nan gaba mai tsawo ne.”
27 Moi, Daniel, je me suis évanoui et j'ai été malade pendant quelques jours. Puis je me suis levé et j'ai fait les affaires du roi. Je m'interrogeais sur la vision, mais personne ne la comprenait.
Ni, Daniyel, na gaji matuƙa na kuma yi rashin lafiya na kwanaki masu yawa. Sa’an nan sai na tashi na ci gaba da hidimar sarki. Wahayin ya shige mini duhu, ya fi ƙarfin fahimtata.

< Daniel 8 >