< Daniel 6 >
1 Il plut à Darius d'établir sur le royaume cent vingt gouverneurs locaux, qui devaient être répartis dans tout le royaume;
Ya gamshi Dariyus ya naɗa muƙaddasai 120 su yi shugabanci a duk fāɗin masarautar,
2 et sur eux trois présidents, dont Daniel faisait partie, afin que ces gouverneurs locaux leur rendent compte et que le roi ne subisse aucune perte.
ya naɗa mutum uku a bisa waɗannan muƙaddasan, Daniyel yana ɗaya daga cikin mutum ukun nan. Sai aka sa muƙaddasan nan a ƙarƙashin waɗannan uku ɗin domin kada sarki ya yi hasarar kome.
3 Ce Daniel se distingua des présidents et des gouverneurs locaux, parce qu'il avait un esprit excellent, et le roi pensa à l'établir sur tout le royaume.
To, Daniyel dai ya yi ficce a cikin shugabannin nan uku har da muƙaddasan ma, saboda waɗansu halaye nagari da yake da su, wanda ya sa sarki ya yi shiri ya ɗora shi a kan dukan mulkinsa.
4 Alors les présidents et les gouverneurs locaux cherchèrent à trouver une occasion contre Daniel en ce qui concerne le royaume; mais ils ne purent trouver ni occasion ni faute, parce qu'il était fidèle. Ils ne trouvèrent ni erreur ni faute en lui.
A kan haka, shugabannin nan uku da muƙaddasan nan suka yi ƙoƙari su sami wani laifi a kan Daniyel a yadda yake tafiyar da aikin shugabancinsa, amma ba su samu ba. Ba su same shi da wani laifin cin hanci ba, domin shi amintacce ne kuma babu wani aibi a kansa ko rashin kula.
5 Alors ces hommes dirent: « Nous ne trouverons aucune occasion contre ce Daniel, à moins que nous ne la trouvions contre lui au sujet de la loi de son Dieu. »
A ƙarshe waɗannan mutane suka ce; “Ba za mu taɓa samun wani laifin da za mu kama Daniyel da shi ba, sai dai ko abin ya shafi dokar Allahnsa.”
6 Alors ces présidents et ces gouverneurs locaux s'assemblèrent auprès du roi, et lui dirent ceci: « Roi Darius, vis éternellement!
Saboda haka shugabannin nan suka haɗu da muƙaddasan nan suka tafi wurin sarki a ƙungiyance suka ce, “Ya Sarki Dariyus, ranka yă daɗe!
7 Tous les présidents du royaume, les députés et les gouverneurs locaux, les conseillers et les gouverneurs, se sont consultés pour établir une loi royale et un décret fort, selon lequel quiconque demandera une requête à un dieu ou à un homme pendant trente jours, sauf à toi, ô roi, sera jeté dans la fosse aux lions.
Shugabannin masarauta, da masu mulki, da muƙaddasai, da mashawarta da gwamnoni duk sun amince cewa sarki yă kafa doka yă kuma yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu’a ga wani allah ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, jefa shi cikin kogon zakoki.
8 Maintenant, ô roi, établis le décret et signe l'écrit, afin qu'il ne soit pas modifié, selon la loi des Mèdes et des Perses, qui ne change pas. »
Yanzu, ya sarki, sai ka yi umarni ka kuma yi shi a rubuce saboda kada a canja shi, bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
9 Le roi Darius signa donc l'écrit et le décret.
Sai Sarki Dariyus ya ba da umarnin a rubuce.
10 Lorsque Daniel sut que l'écriture était signée, il entra dans sa maison (les fenêtres de sa chambre étaient maintenant ouvertes vers Jérusalem) et il se mit à genoux trois fois par jour, et pria, et rendit grâce devant son Dieu, comme il le faisait auparavant.
To, da Daniyel ya ji labarin cewa an fitar da doka, sai ya tafi gidansa a ɗakinsa na sama inda tagogin ɗakin suke duban wajen Urushalima. Sau uku yakan durƙusa yă yi addu’a yana yin godiya ga Allahnsa, kamar yadda ya saba yi.
11 Alors ces hommes s'assemblèrent et trouvèrent Daniel en train de prier et de supplier son Dieu.
Sai waɗannan mutane suka tafi a ƙungiyance suka kuma iske Daniyel yana addu’a yana roƙon Allah yă taimake shi.
12 Alors ils s'approchèrent et parlèrent devant le roi au sujet du décret du roi: « N'as-tu pas signé un décret selon lequel tout homme qui, dans les trente jours, adressera une requête à un dieu ou à un homme, sauf à toi, ô roi, sera jeté dans la fosse aux lions? ». Le roi répondit: « Cette chose est vraie, selon la loi des Mèdes et des Perses, qui ne change pas. »
Sai suka tafi wurin sarki suka yi masa magana game da dokar mulkinsa, suka ce, “Ashe, ba ka yi doka cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda aka tarar yana addu’a ga wani allah ko mutum in ba kai ba, ya sarki, za ka jefa shi a cikin ramin zakoki ba?” Sarki ya amsa ya ce, “Dokar tana nan daram bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
13 Alors ils prirent la parole et dirent devant le roi: « Ce Daniel, qui est d'entre les enfants de la captivité de Juda, ne te respecte pas, ô roi, ni le décret que tu as signé, mais il fait sa demande trois fois par jour. »
Sai suka ce wa sarki, “Daniyel ɗin nan, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda aka kwaso daga Yahuda, bai kula da kai ba, ya sarki, balle fa dokar da ka yi. Har yanzu yana addu’a sau uku a rana.”
14 Alors le roi, en entendant ces paroles, fut très mécontent, et il jeta son dévolu sur Daniel pour le délivrer; et il travailla jusqu'au coucher du soleil pour le secourir.
Da sarki ya ji haka, sai ya damu sosai, ya ƙudura yă ceci Daniyel, ya yi ta fama har fāɗuwar rana yadda zai yi yă kuɓutar da shi.
15 Alors ces hommes s'assemblèrent auprès du roi et lui dirent: « Sache, ô roi, que c'est une loi des Mèdes et des Perses, qu'aucun décret ni aucune loi que le roi établit ne peut être modifié. »
Sai mutanen nan suka je wurin sarki a ƙungiyance suka ce masa, “Ka tuna, ya sarki; cewa bisa ga dokar Medes da Farisa, babu umarni ko dokar da sarki ya yi da za a iya sokewa.”
16 Alors le roi ordonna qu'on amène Daniel et qu'on le jette dans la fosse aux lions. Le roi prit la parole et dit à Daniel: « Ton Dieu que tu sers sans cesse, il te délivrera. »
Saboda haka sai sarki ya ba da umarni suka kuma kawo Daniyel suka jefa shi cikin ramin zakoki. Sarki ya ce wa Daniyel, “Bari Allahn nan wanda kake bauta masa kullum, yă cece ka!”
17 On apporta une pierre qu'on posa sur l'ouverture de la fosse, et le roi la scella de son propre sceau et du sceau de ses grands, afin que rien ne fût changé au sujet de Daniel.
Aka kawo dutsen aka rufe bakin ramin, sa’an nan sarki ya hatimce shi da zobensa da kuma zoban manyan mutanensa, don kada wani yă canja yanayin Daniyel.
18 Le roi se rendit ensuite dans son palais, et passa la nuit à jeûner. On ne lui apporta aucun instrument de musique, et le sommeil le quitta.
Sa’an nan sarki ya koma fadarsa ya kwana bai ci ba, kuma babu wata liyafar da aka kawo masa. Ya kuma kāsa barci.
19 Le roi se leva de grand matin, et se rendit en hâte à la fosse aux lions.
Gari yana wayewa, sai sarki ya tashi ya hanzarta zuwa ramin zakoki.
20 Lorsqu'il s'approcha de la fosse, Daniel cria d'une voix troublée. Le roi prit la parole et dit à Daniel: « Daniel, serviteur du Dieu vivant, ton Dieu, que tu sers continuellement, est-il capable de te délivrer des lions? »
Da ya yi kusa da ramin zakokin, sai ya kira Daniyel da muryar mai cike da damuwa ya ce, “Daniyel bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta wa kullum, ya iya cetonka daga zakoki?”
21 Alors Daniel dit au roi: « O roi, vis éternellement!
Sai Daniyel ya amsa ya ce, “Ran sarki, yă daɗe!
22 Mon Dieu a envoyé son ange et a fermé la gueule des lions, et ils ne m'ont pas fait de mal, parce que l'innocence a été trouvée en moi devant lui; et aussi devant toi, ô roi, je n'ai fait aucun mal. »
Allahna ya aiko da mala’ikansa, ya kuwa rufe bakunan zakoki. Ba su yi mini rauni ba, gama an same ni marar laifi ne a gabansa. Ban kuwa taɓa yin wani abu marar kyau a gabanka ba, ya sarki.”
23 Le roi se réjouit et ordonna qu'on fasse sortir Daniel de la fosse. On fit donc sortir Daniel de la fosse, et on ne lui trouva aucun mal, car il avait mis sa confiance en son Dieu.
Sai sarki ya cika da murna ƙwarai, ya kuma yi umarni a ciro Daniyel daga ramin zakoki. Kuma da aka fito da Daniyel daga ramin, ba a sami wani rauni a jikinsa ba, domin ya dogara ga Allahnsa.
24 Le roi donna cet ordre. On amena les hommes qui avaient accusé Daniel et on les jeta dans la fosse aux lions, eux, leurs enfants et leurs femmes; les lions les déchiquetèrent et brisèrent tous leurs os avant qu'ils n'arrivent au fond de la fosse.
Sai sarki ya umarta, a kawo mutanen nan da suka yi wa Daniyel maƙarƙashiya, a tura su, da’ya’yansu, da matansu cikin ramin zakoki. Kafin ma su kai ƙurewar ramin, sai zakoki suka hallaka su suka yayyage su, suka yi kaca-kaca da su.
25 Alors le roi Darius écrivit à tous les peuples, nations et langues qui habitent sur toute la terre: « Que la paix vous soit multipliée.
Sa’an nan Sarki Dariyus ya rubuta wa dukan mutane, da al’ummai da kuma mutanen dukan harsunan a duk fāɗin ƙasar. “Bari yă yi nasara sosai!
26 « Je décrète que dans toute la domination de mon royaume, les hommes tremblent et craignent devant le Dieu de Daniel. « Car il est le Dieu vivant, et inébranlable pour toujours. Son royaume est celui qui ne sera pas détruit. Sa domination s'étendra jusqu'à la fin.
“Na fitar da doka cewa a cikin dukan iyakar ƙasar mulkina, dole mutane su ji tsoro su kuma girmama Allah na Daniyel.
27 Il délivre et sauve. Il accomplit des signes et des prodiges dans le ciel et sur la terre, qui a délivré Daniel de la puissance des lions. »
Yakan kuɓutar ya kuma ceci;
28 Ce Daniel prospéra donc sous le règne de Darius et sous le règne de Cyrus le Perse.
Daniyel kuwa ya bunkasa a lokacin mulkin Dariyus da kuma mulkin Sairus na Farisa.