< Daniel 2 >

1 La deuxième année du règne de Nebucadnetsar, Nebucadnetsar eut des songes; son esprit fut troublé, et le sommeil le quitta.
A shekara ta biyu ta mulkinsa, Nebukadnezzar ya yi mafarkai; hankalinsa ya tashi har ya kāsa barci.
2 Alors le roi ordonna que l'on appelle les magiciens, les enchanteurs, les sorciers et les Chaldéens pour qu'ils racontent au roi ses rêves. Ils entrèrent donc et se tinrent devant le roi.
Sai sarki ya sa aka tattara masa masu sihiri da masu dabo da bokaye da masanan taurari domin su faɗi abin da ya yi mafarki a kai. Da suka shigo suka tsaya a gaban sarki,
3 Le roi leur dit: « J'ai fait un rêve, et mon esprit est troublé de connaître ce rêve. »
sai ya ce musu, “Na yi mafarkin da ya dame ni kuma ina so in san me yake nufi.”
4 Alors les Chaldéens s'adressèrent au roi en langue syrienne: « O roi, vis éternellement! Raconte le rêve à tes serviteurs, et nous t'en donnerons l'interprétation. »
Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki da Arameyanci “Ran sarki yă daɗe! Ka faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma sai mu fassara.”
5 Le roi répondit aux Chaldéens: « La chose s'est éloignée de moi. Si vous ne me faites pas connaître le rêve et son interprétation, vous serez taillés en pièces, et vos maisons seront transformées en tas de fumier.
Sai sarki ya amsa wa masanan taurarin ya ce, “Na mance da abin, idan ba ku tuno mini mafarkin, duk da fassararsa ba, to, za a daddatse ku gunduwa-gunduwa, a mai da gidajenku juji.
6 Mais si tu me fais connaître le rêve et son interprétation, tu recevras de moi des dons, des récompenses et de grands honneurs. Montre-moi donc le rêve et son interprétation. »
Amma in har kuka faɗa mini mafarkina kuka kuma bayyana fassararsa, za ku sami lada mai girma. Saboda haka ku faɗa mini mafarkin da kuma fassararsa.”
7 Ils prirent la parole une seconde fois et dirent: « Que le roi raconte le songe à ses serviteurs, et nous en montrerons l'interprétation. »
Sai suka sāke amsa masa suka ce, “Ran sarki yă daɗe, faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma za mu fassara shi.”
8 Le roi répondit: « Je sais avec certitude que tu cherches à gagner du temps, car tu vois que la chose s'est éloignée de moi.
Sai sarki ya amsa ya ce, “Na gane cewa kuna ƙoƙari ku ɓata lokaci ne kawai domin ku ga na manta da abin.
9 Mais si tu ne me fais pas connaître le rêve, il n'y a qu'une seule loi pour toi, car tu as préparé des paroles mensongères et corrompues pour parler devant moi, jusqu'à ce que la situation change. C'est pourquoi, dis-moi le rêve, et je saurai que tu peux me montrer son interprétation. »
In ba ku faɗa mini mafarkin ba, akwai hukunci guda ɗaya kurum dominku. Kun haɗa baki domin ku faɗa mini munanan al’amura domin ku ruɗe ni har lokaci yă wuce. Sai ku faɗa mini mafarkin, ta haka kuwa zan sani za ku iya yi mini fassararsa.”
10 Les Chaldéens répondirent au roi et dirent: « Il n'y a pas un homme sur la terre qui puisse montrer l'affaire du roi, car aucun roi, aucun seigneur, aucun chef n'a demandé une telle chose à aucun magicien, aucun enchanteur, aucun Chaldéen.
Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki suka ce, “Babu wani mutum a duniyan nan da zai iya yin abin da sarki yake nema! Babu wani sarki mai daraja da girma wanda ya taɓa yin irin wannan tambaya ga masu sihiri ko masu dabo ko masanan taurari.
11 C'est une chose rare que le roi demande, et il n'y a personne qui puisse la montrer devant le roi, si ce n'est les dieux, dont la demeure n'est pas avec la chair. »
Abin da sarki yake nema yana da wuya matuƙa. Babu wani da zai iya bayyana wannan ga sarki sai dai alloli; kuma ba su zama tare da’yan adam.”
12 A cause de cela, le roi était en colère et très furieux, et il ordonna que tous les sages de Babylone soient détruits.
Wannan ya sa sarki ya fusata ƙwarai, ya ba da umarni a tafi da dukan masu hikima na Babilon a kashe su.
13 Le décret fut donc publié, et les sages devaient être tués. On chercha à faire tuer Daniel et ses compagnons.
Sai aka ba da dokar da za a kashe masu hikima, sa’an nan aka aika mutane su je su nemo Daniyel da abokansa domin a kashe su.
14 Alors Daniel répondit avec conseil et prudence à Arioch, chef des gardes du roi, qui était sorti pour tuer les sages de Babylone.
Sa’ad da Ariyok, shugaban ƙungiyar matsaran sarki, ya fita domin yă kashe masu hikima na Babilon, sai Daniyel ya yi masa magana cikin hikima da dabara.
15 Il répondit à Arioch, le chef des gardes du roi: « Pourquoi le décret du roi est-il si urgent? » Et Arioch fit connaître la chose à Daniel.
Ya tambayi mai tsaro na sarki, “Me ya sa sarki ya fitar da wannan doka haka da fushi?” Sai Ariyok ya yi wa Daniyel bayanin batun.
16 Daniel entra, et demanda au roi de lui fixer un moment, et de lui montrer l'interprétation.
Da jin haka sai Daniyel ya tafi wurin sarki ya nemi ƙarin lokaci, domin yă bayyana wa sarki mafarkin da kuma fassararsa.
17 Alors Daniel alla dans sa maison et fit connaître la chose à Hanania, à Mischaël et à Azaria, ses compagnons:
Sa’an nan Daniyel ya komo gida ya kuma sanar wa abokansa Hananiya, Mishayel da Azariya, batun nan duka.
18 afin qu'ils demandent au Dieu des cieux la grâce de ce secret, pour que Daniel et ses compagnons ne périssent pas avec le reste des sages de Babylone.
Ya roƙe su su roƙi jinƙan Allah na sama domin wannan mafarki, saboda kada a kashe shi da abokansa tare da sauran masu hikima na Babilon.
19 Alors le secret fut révélé à Daniel dans une vision pendant la nuit. Alors Daniel bénit le Dieu des cieux.
A wannan dare sai aka bayyana wa Daniyel mafarkin cikin wahayi. Daniyel kuwa ya ɗaukaka Allah na sama.
20 Daniel répondit, « Béni soit le nom de Dieu pour les siècles des siècles; car la sagesse et la puissance lui appartiennent.
Ya ce, “Yabo ya tabbata ga sunan Allah har abada abadin; hikima da iko nasa ne.
21 Il change les temps et les saisons. Il destitue les rois et établit les rois. Il donne la sagesse aux sages, et la connaissance à ceux qui ont de l'intelligence.
Yana sāke lokuta, yana tuɓe sarakuna yana kuma naɗa waɗansu. Yana ba da hikima ga masu hikima kuma ilimi ga masu basira.
22 Il révèle les choses profondes et secrètes. Il sait ce qu'il y a dans les ténèbres, et la lumière habite avec lui.
Yakan bayyana zurfafa da ɓoyayyun abubuwa; ya san abin da yake cikin dare, haske kuwa yana zaune tare da shi.
23 Je te remercie et je te loue, O Dieu de mes pères, qui m'ont donné la sagesse et la puissance, et m'ont maintenant fait connaître ce que nous désirions de vous; car vous nous avez fait part de l'affaire du roi. »
Na gode maka ina yabonka, Allah na kakannina. Kai ka san hikima da iko, ka sanar da ni abin da muka tambaye ka, ka kuma sanar da mu mafarkin sarki.”
24 Daniel alla donc trouver Arioch, que le roi avait chargé de détruire les sages de Babylone. Il alla lui dire ceci: « Ne détruis pas les sages de Babylone. Fais-moi entrer devant le roi, et je montrerai au roi l'interprétation. »
Sai Daniyel ya tafi wurin Ariyok, wanda sarki ya sa yă kashe masu hikiman Babilon, ya kuma ce masa, “Kada ka kashe masu hikiman Babilon ka kai ni wurin sarki, ni kuma zan fassara masa mafarkinsa.”
25 Alors Arioch fit venir Daniel en hâte devant le roi, et lui dit ceci: « J'ai trouvé un homme parmi les enfants de la captivité de Juda qui fera connaître au roi l'interprétation. »
Sai Ariyok ya kai Daniyel wurin sarki nan take ya ce masa, “Na gano wani mutum daga cikin kamammun kabilar Yahuda wanda zai faɗa wa sarki abin da mafarkin yake nufi.”
26 Le roi prit la parole et dit à Daniel, qui s'appelait Belteshazzar: « Peux-tu me faire connaître le rêve que j'ai vu et son interprétation? »
Sarki ya tambayi Daniyel (wanda ake kira Belteshazar), za ka iya faɗa mini mafarkin da na yi ka kuma fassara shi?
27 Daniel prit la parole devant le roi et dit: « Le secret que le roi a demandé ne peut être révélé au roi par des sages, des enchanteurs, des magiciens ou des devins;
Daniyel ya amsa, “Babu wani mai hikima, ko mai sihiri, ko mai dabo ko mai duban da zai iya warware wa sarki wannan matsala da ta dame shi,
28 mais il y a dans les cieux un Dieu qui révèle les secrets, et il a fait connaître au roi Nebucadnetsar ce qui arrivera dans la suite des temps. Voici ton rêve et les visions de ta tête sur ton lit:
amma akwai Allahn da yake a sama wanda yake bayyana asirai, ya nuna wa sarki Nebukadnezzar abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayin da ya wuce cikin tunaninka a sa’ad da kake kwance a gadonka su ne,
29 « Quant à toi, ô roi, tes pensées sont venues sur ta couche, ce qui doit arriver après; et celui qui révèle les secrets t'a fait connaître ce qui arrivera.
“A sa’ad da kake kwance, ya sarki, tunaninka ya ga al’amuran da suke zuwa, kuma shi mai bayyana al’amuran ya bayyana maka asiran abubuwan da za su faru.
30 Quant à moi, ce secret ne m'est pas révélé à cause d'une sagesse que j'aurais plus qu'aucun vivant, mais dans le but que l'interprétation soit connue du roi, et que tu puisses connaître les pensées de ton cœur.
Amma ba a bayyana mini wannan asiri saboda ina da wata hikima fiye da sauran mutane ba, sai dai domin a sanar wa sarki da fassarar, ka kuma san tunanin da ya shiga zuciyarka.
31 « Toi, ô roi, tu as vu, et voici, une grande image. Cette image, qui était puissante et dont l'éclat était excellent, se tenait devant toi, et son aspect était terrifiant.
“Ya sarki, ka ga wata babbar siffa, mai girma, siffa ce mai haske, abar bantsoro tana tsaye a gabanka.
32 Cette statue avait une tête d'or fin, une poitrine et des bras d'argent, un ventre et des cuisses d'airain,
An yi kan wannan siffa da zinariya zalla, ƙirjinta da kuma hannuwanta an yi su da azurfa, cikinta da kuma cinyarta da tagulla ne.
33 des jambes de fer, des pieds en partie de fer et en partie d'argile.
An yi ƙafafun da ƙarfe, tafin ƙafafunta kuma an yi rabi da ƙarfe rabi kuma da yumɓu.
34 Tu as vu jusqu'à ce qu'une pierre taillée sans main frappe la statue sur ses pieds de fer et d'argile, et les mette en pièces.
A lokacin da kake dubawa, sai aka yanko wani dutse, amma ba da hannun mutum ba. Ya fāɗa a kan ƙafafun siffar na ƙarfen da aka haɗa da yumɓu aka kuma ragargaje su.
35 Alors le fer, l'argile, l'airain, l'argent et l'or se brisèrent ensemble, et devinrent comme la balle des aires de battage d'été. Le vent les emporta, et il n'y eut plus de place pour eux. La pierre qui avait frappé la statue devint une grande montagne et remplit toute la terre.
Sai ƙarfen da yambun da tagulla da azurfan da kuma zinariyan suka ragargaje a lokaci ɗaya ya zama kamar ƙaiƙayi a masussuka a lokacin kaka. Sai iska ta kwashe su ta tafi, har ba a iya ganin ko alamarsu. Amma dutsen da ya fāɗo a siffar ya girke ya zama tsauni ya kuma cika dukan duniya.
36 Voici le songe, et nous allons en donner l'interprétation devant le roi.
“Wannan shi ne mafarkin, yanzu kuma za mu fassara ta wa sarki.
37 Toi, ô roi, tu es le roi des rois, celui à qui le Dieu des cieux a donné le règne, la puissance, la force et la gloire.
Ya, sarki, kai ne sarkin sarakuna. Allah na sama ya ba ka iko da girma da suna;
38 Partout où habitent les enfants des hommes, il a remis entre tes mains les animaux des champs et les oiseaux du ciel, et il t'a fait dominer sur eux tous. Tu es la tête d'or.
a cikin hannunka ya sanya ɗan adam, da namun jeji da tsuntsayen sama. A duk inda suke zaune, ya maishe ka ka yi mulki a bisansu kai ne kan zinariyan nan na siffar.
39 Après toi, il s'élèvera un autre royaume qui te sera inférieur, et un troisième royaume d'airain, qui dominera sur toute la terre.
“A bayanka, za a yi wani mulki, wanda bai kai naka ba. A gaba kuma, za a yi mulki na uku wanda yake na tagulla, zai yi mulkin dukan duniya.
40 Le quatrième royaume sera fort comme le fer, car le fer met tout en pièces et soumet tout; et comme le fer qui écrase tout cela, il mettra tout en pièces et écrasera.
A ƙarshe, za a yi mulki na huɗu, mai ƙarfi kamar ƙarfe, Da yake baƙin ƙarfe yakan kakkarya, ya ragargaje abubuwa, haka nan wannan mulki zai ragargaje sauran mulkoki
41 Comme tu as vu les pieds et les orteils, en partie d'argile et en partie de fer, ce sera un royaume divisé; mais il y aura en lui de la force du fer, parce que tu as vu le fer mêlé à l'argile.
Ka kuma ga an yi ƙafafun da yatsotsin da baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu, wato, mulkin zai rabu, amma zai kasance da ƙarfi kamar na baƙin ƙarfe da yake gauraye da yumɓu.
42 Comme les orteils des pieds étaient en partie de fer et en partie d'argile, ainsi le royaume sera en partie fort et en partie fragile.
Kamar yadda yatsotsin rabi na ƙarfe rabi kuma na yumɓu ne, haka wannan mulki zai zama rabi mai ƙarfi rabi kuma marar ƙarfi.
43 Comme tu as vu le fer mêlé à l'argile, ils se mêleront à la race des hommes, mais ils ne s'attacheront pas les uns aux autres, comme le fer ne se mêle pas à l'argile.
Kamar dai yadda ka ga ƙarfen ya gauraye da yumɓu, haka mutanen za su zama a gauraye amma ba za su haɗu da juna ba, kamar yadda baƙin ƙarfe da yumɓu ba su haɗuwa.
44 « Dans les jours de ces rois, le Dieu des cieux établira un royaume qui ne sera jamais détruit, et dont la souveraineté ne sera jamais confiée à un autre peuple; mais il brisera et consumera tous ces royaumes, et il subsistera à jamais.
“A lokacin mulkin waɗannan sarakunan, Allah na sama zai kafa mulki da ba zai taɓa rushewa ba, ba kuma za a ba ma waɗansu mutane ba. Zai ragargaje waɗannan mulkokin da kuma kawo su ga ƙarshe, amma shi wannan mulki zai dawwama har abada.
45 Parce que tu as vu qu'une pierre s'est détachée sans main de la montagne et qu'elle a brisé le fer, le bronze, l'argile, l'argent et l'or, le grand Dieu a fait connaître au roi ce qui arrivera dans la suite. Le rêve est certain, et son interprétation est sûre. »
Wannan shi ne ma’anar wannan wahayin da ka gani na dutsen da aka yanko daga jikin tsaunin, amma ba da hannun ɗan adam ba, dutsen da ya ragargaza ƙarfen, da tagullar, da yumɓun da azurfar da kuma zinariyar. “Allah mai girma ya nuna wa sarki abin da zai faru nan gaba. Mafarkin gaskiya ne, fassararsa kuma abin dogara ne.”
46 Alors le roi Nebucadnetsar tomba sur sa face, se prosterna devant Daniel, et ordonna qu'on lui présente une offrande et des parfums doux.
Sai sarki Nebukadnezzar ya fāɗi da fuskarsa har ƙasa a gaban Daniyel domin ya girmama shi ya kuma umarta a miƙa hadaya da kuma hadayar ƙonawa ta turare ga Daniyel.
47 Le roi prit la parole et dit à Daniel: « En vérité, ton Dieu est le Dieu des dieux, le Seigneur des rois et le révélateur des secrets, puisque tu as pu révéler ce secret. »
Sarki ya kuma ce wa Daniyel, “Tabbatacce Allahnka shi ne Allahn alloli da kuma Sarkin sarakuna da mai bayyana asirai, gama ka iya bayyana wannan asiri.”
48 Alors le roi fit de Daniel un grand homme et lui fit beaucoup de dons importants, et il le fit gouverner toute la province de Babylone et être le principal gouverneur de tous les sages de Babylone.
Sai sarki ya ɗora Daniyel a babban matsayi ya kuma sanya shi mai mulki a kan dukan yankin ƙasar Babilon; ya kuma ɗora shi yă zama mai kula da duk masu hikima.
49 Daniel demanda au roi de nommer Schadrac, Méschac et Abed-Nego pour diriger les affaires de la province de Babylone, mais Daniel était à la porte du roi.
Bugu da ƙari, bisa ga bukatar Daniyel sai sarki yă naɗa Shadrak da Meshak da Abednego su zama masu kula da harkokin lardin Babilon, amma Daniyel kuma ya tsaya a fadar sarki.

< Daniel 2 >