< Daniel 11 >

1 « Quant à moi, la première année de Darius le Mède, je me suis levé pour le confirmer et le renforcer.
A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
2 « Maintenant, je vais te montrer la vérité. Voici que trois autres rois vont se lever en Perse. Le quatrième sera beaucoup plus riche que tous les autres. Quand il sera devenu fort par ses richesses, il soulèvera tout contre le royaume de Grèce.
“Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
3 Un roi puissant se lèvera, qui dominera avec une grande autorité, et fera ce qu'il voudra.
Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
4 Quand il se lèvera, son royaume sera brisé et partagé aux quatre vents du ciel, mais non pas pour sa postérité, ni selon la domination avec laquelle il a régné; car son royaume sera arraché, même pour d'autres que ceux-là.
Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
5 « Le roi du midi sera puissant. L'un de ses princes deviendra plus fort que lui et dominera. Sa domination sera une grande domination.
“Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
6 A la fin des années, ils s'uniront; et la fille du roi du midi ira vers le roi du nord pour conclure une alliance, mais elle ne conservera pas la force de son bras. Lui aussi ne tiendra pas, et son bras non plus; mais elle sera livrée, avec ceux qui l'ont amenée, et celui qui l'a engendrée, et celui qui l'a fortifiée en ces temps-là.
Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
7 « Mais d'un rejeton sorti de ses racines se lèvera un homme à sa place, qui ira à l'armée et entrera dans la forteresse du roi du nord; il traitera avec eux et sera vainqueur.
“Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
8 Il emmènera aussi en captivité en Égypte leurs dieux, avec leurs images en fonte, et leurs vases d'argent et d'or. Il s'abstiendra quelques années du roi du nord.
Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
9 Il entrera dans le royaume du roi du midi, mais il retournera dans son pays.
Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
10 Ses fils feront la guerre et rassembleront une multitude de grandes forces qui arriveront, déborderont et passeront. Ils reviendront et feront la guerre, jusqu'à sa forteresse.
’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
11 « Le roi du Midi sera irrité et sortira pour le combattre, même le roi du Nord. Il enverra une grande multitude, et la multitude sera livrée entre ses mains.
“Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
12 La multitude sera emportée, et son cœur s'élèvera. Il renversera des dizaines de milliers, mais il ne vaincra pas.
Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
13 Le roi du nord reviendra, et il enverra une multitude plus nombreuse que la précédente. Il arrivera à la fin des temps, des années, avec une grande armée et des provisions abondantes.
Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
14 « En ces temps-là, beaucoup se dresseront contre le roi du Midi. Les enfants des violents parmi ton peuple se lèveront aussi pour établir la vision, mais ils tomberont.
“A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
15 Alors le roi du nord viendra, il élèvera un monticule et prendra une ville bien fortifiée. Les forces du sud ne tiendront pas, ni ses troupes choisies, et il n'y aura pas de force pour tenir.
Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
16 Mais celui qui viendra contre lui agira selon sa propre volonté, et personne ne tiendra devant lui. Il se tiendra dans le pays de la gloire, et la destruction sera dans sa main.
Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
17 Il se préparera à venir avec la force de tout son royaume, et avec lui des conditions équitables. Il les exécutera. Il lui donnera la fille des femmes, pour détruire le royaume, mais elle ne tiendra pas, et ne sera pas pour lui.
Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
18 Après cela, il tournera sa face vers les îles, et il en prendra beaucoup, mais un prince fera cesser l'opprobre qui lui est fait. Oui, bien plus, il fera en sorte que l'opprobre se retourne contre lui.
Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
19 Puis il tournera sa face vers les forteresses de son pays; mais il trébuchera et tombera, et on ne le retrouvera pas.
Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
20 « Alors se dressera à sa place celui qui fera passer un collecteur d'impôts dans le royaume pour en maintenir la gloire; mais en peu de jours il sera détruit, non par la colère, ni par la bataille.
“Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
21 « A sa place se lèvera un homme méprisable, à qui on n'avait pas donné l'honneur du royaume; mais il viendra au temps de la sécurité, et il obtiendra le royaume par des flatteries.
“Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
22 Les forces écrasantes seront submergées devant lui, et seront brisées. Oui, aussi le prince de l'alliance.
Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
23 Après le traité conclu avec lui, il agira avec ruse; car il s'élèvera et deviendra fort avec peu de gens.
Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
24 Au temps de la sécurité, il s'attaquera même aux lieux les plus gras de la province. Il fera ce que ses pères n'ont pas fait, ni les pères de ses pères. Il répandra parmi eux la proie, le pillage et la richesse. Oui, il élaborera ses plans contre les forteresses, mais seulement pour un temps.
Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
25 « Il excitera sa puissance et son courage contre le roi du Midi avec une grande armée; et le roi du Midi livrera bataille avec une armée extrêmement grande et puissante, mais il ne tiendra pas, car on ourdira des plans contre lui.
“Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
26 Oui, ceux qui mangeront de ses mets le détruiront, et son armée sera balayée. Beaucoup tomberont tués.
Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
27 Quant à ces deux rois, leur cœur sera porté à faire le mal, et ils diront des mensonges à une table; mais cela ne réussira pas, car la fin sera toujours au temps fixé.
Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
28 Puis il retournera dans son pays avec de grandes richesses. Son cœur sera contre l'alliance sainte. Il agira, et retournera dans son pays.
“Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
29 « Il reviendra au temps fixé et entrera dans le Midi; mais ce ne sera pas au dernier temps comme au premier.
“A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
30 Car des navires de Kittim viendront contre lui. C'est pourquoi il sera affligé, et il reviendra, et il s'indignera contre l'alliance sainte, et il agira. Il reviendra même, et aura égard à ceux qui abandonnent l'alliance sainte.
Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
31 « Des forces de sa part profaneront le sanctuaire, la forteresse, et feront disparaître l'holocauste perpétuel. Puis ils dresseront l'abomination qui désole.
“Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
32 Il corrompra par des flatteries les méchants de l'alliance, mais le peuple qui connaît son Dieu sera fort et agira.
Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
33 « Les sages parmi le peuple en instruiront beaucoup; mais ils tomberont par l'épée et par la flamme, par la captivité et par le pillage, pendant plusieurs jours.
“Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
34 Lorsqu'ils tomberont, on leur portera un petit secours; mais beaucoup se joindront à eux par des flatteries.
Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
35 Quelques-uns des sages tomberont pour les affiner, pour les purifier, pour les blanchir, jusqu'au temps de la fin, car c'est encore pour le temps fixé.
Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
36 « Le roi fera ce qu'il voudra. Il s'élèvera et se glorifiera au-dessus de tout dieu, et il dira des choses merveilleuses contre le Dieu des dieux. Il prospérera jusqu'à l'accomplissement de l'indignation, car ce qui est déterminé s'accomplira.
“Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
37 Il ne tiendra pas compte des dieux de ses pères, ni du désir des femmes, ni d'aucun dieu, car il s'élèvera au-dessus de tous.
Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
38 Mais à leur place, il honorera le dieu des forteresses. Il honorera un dieu que ses pères n'ont pas connu, avec de l'or, de l'argent, des pierres précieuses et des choses agréables.
A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
39 Il vaincra les forteresses les plus puissantes avec l'aide d'un dieu étranger. Il accroîtra la gloire de ceux qui le reconnaîtront. Il les fera dominer sur beaucoup de gens, et il partagera le pays à prix d'argent.
Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
40 « Au temps de la fin, le roi du midi lui fera la guerre, et le roi du nord viendra contre lui comme un tourbillon, avec des chars, des cavaliers et de nombreux navires. Il entrera dans les pays, il les débordera et les traversera.
“A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
41 Il entrera aussi dans le pays de la gloire, et beaucoup de pays seront renversés; mais ceux-ci seront délivrés de sa main: Édom, Moab, et le chef des enfants d'Ammon.
Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
42 Il étendra aussi sa main sur les pays. Le pays d'Égypte n'échappera pas.
Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
43 Mais il aura le pouvoir sur les trésors d'or et d'argent, et sur tous les objets précieux de l'Égypte. Les Libyens et les Éthiopiens suivront ses traces.
Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
44 Mais des nouvelles de l'Orient et du Nord le troubleront, et il sortira avec une grande fureur pour détruire et exterminer beaucoup de gens.
Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
45 Il plantera les tentes de son palais entre la mer et la glorieuse montagne sainte; mais il arrivera à sa perte, et personne ne lui viendra en aide.
Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.

< Daniel 11 >