< Amos 9 >
1 Je vis l'Éternel debout près de l'autel, et il dit: « Frappez le sommet des colonnes, afin que les seuils soient ébranlés. Brisez-les en morceaux sur la tête de chacun d'eux. Je tuerai le dernier d'entre eux par l'épée. Pas un seul d'entre eux ne s'enfuira. Pas un seul d'entre eux n'échappera.
Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
2 S'ils creusent dans le séjour des morts, là ma main les saisira; S'ils montent au ciel, là je les ferai descendre. (Sheol )
Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol )
3 S'ils se cachent au sommet du Carmel, je les chercherai et les enlèverai; s'ils se dérobent à ma vue au fond de la mer, j'y commanderai au serpent, et il les mordra.
Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
4 S'ils vont en captivité devant leurs ennemis, là je commanderai à l'épée, et elle les tuera. Je tournerai mes regards vers eux pour le mal et non pour le bien.
Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
5 Car c'est le Seigneur, l'Éternel des armées, qui touche la terre et la fait fondre, et tous ceux qui l'habitent se lamentent; elle se soulève entièrement comme le fleuve, et elle retombe comme le fleuve d'Égypte.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
6 C'est lui qui bâtit ses chambres dans les cieux, et qui a fondé sa voûte sur la terre; c'est lui qui appelle les eaux de la mer, et qui les répand sur la surface de la terre - Yahvé est son nom.
shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
7 N'êtes-vous pas pour moi comme les enfants des Éthiopiens, enfants d'Israël? dit Yahvé. « N'ai-je pas fait monter Israël du pays d'Égypte, les Philistins de Caphtor, et les Syriens de Kir?
“Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
8 Voici, les yeux du Seigneur Yahvé sont sur le royaume du péché, et je le détruirai de la surface de la terre, sauf que je ne détruirai pas complètement la maison de Jacob », dit Yahvé.
“Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
9 « Car voici, je commanderai, et je criblerai la maison d'Israël parmi toutes les nations, comme on crible du grain dans un tamis, et il ne tombera pas le moindre grain sur la terre.
“Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
10 Tous les pécheurs de mon peuple mourront par l'épée, eux qui disent: « Le mal ne nous atteindra pas et ne nous rencontrera pas ».
Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
11 En ce jour-là, je relèverai la tente de David, qui est tombée, je fermerai ses brèches, je relèverai ses ruines, et je la rebâtirai comme aux jours d'autrefois,
“A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
12 afin qu'ils possèdent le reste d'Édom et toutes les nations appelées par mon nom, dit Yahvé qui fait cela.
domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
13 « Voici, les jours viennent, dit Yahvé, « que le laboureur dépasse le moissonneur, et celui qui foule les raisins celui qui sème la graine; et du vin doux coulera des montagnes, et coulent des collines.
“Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
14 Je ramènerai mon peuple Israël de la captivité, ils rebâtiront les villes en ruines et les habiteront; ils planteront des vignes et en boiront le vin. Ils feront aussi des jardins, et manger leurs fruits.
Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
15 Je les planterai sur leur terre, et ils ne seront plus arrachés du pays que je leur ai donné, » dit Yahvé ton Dieu.
Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.