< Amos 4 >

1 Écoutez cette parole, vaches de Basan, qui êtes sur la montagne de Samarie, qui opprimez le pauvre, qui écrasez l'indigent, qui dites à vos maris: « Apportez-nous à boire! »
Ku kasa kunne ga wannan, ya ku shanun Bashan a kan Dutsen Samariya, ku matan da kuke cin zalin matalauta, kuke kuma danne matalauta, kuna kuma ce wa mazanku, “Ku kawo mana abin sha!”
2 Le Seigneur Yahvé a juré par sa sainteté, « Voici que les jours viendront pour vous où l'on vous emmènera avec des crochets, et le dernier d'entre vous avec des hameçons.
Ubangiji Mai Iko Duka ya rantse da tsarkinsa. “Tabbatacce lokaci yana zuwa da za a jawo ku da ƙugiyoyi, na ƙarshenku za a kama da ƙugiyar kifi.
3 Vous sortirez par les brèches du mur, tout le monde droit devant elle; et vous vous jetterez dans Harmon, dit Yahvé.
Dukanku za ku wuce ta kai tsaye ta inda katangar ta tsage, za a jefar da ku a Harmon,” in ji Ubangiji.
4 « Va à Béthel, et pèche; à Gilgal, et pécher encore. Apportez vos sacrifices chaque matin, vos dîmes tous les trois jours,
“Ku tafi Betel ku yi ta aikata zunubi; ku je Gilgal ku ƙara yin zunubi. Ku kawo hadayunku kowace safiya, zakkarku kowace shekara uku.
5 offrir un sacrifice d'action de grâces de ce qui est levé, et proclamer des offres de libre arbitre et s'en vanter; car cela vous plaît, enfants d'Israël, dit le Seigneur Yahvé.
Ku ƙona burodinku mai yisti kamar hadaya ta godiya, ku yi fariya game da hadayunku na yarda rai, ku yi taƙama game da su, ya ku Isra’ilawa, gama abin da kuke jin daɗin aikata ke nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
6 « Je vous ai aussi donné la pureté des dents dans toutes vos villes, et le manque de pain dans chaque ville; et vous n'êtes pas revenus vers moi, dit Yahvé.
“Na bar ku da yunwa a kowace birni, da kuma rashin abinci a kowane gari, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
7 « Moi aussi, je vous ai refusé la pluie, alors qu'il restait encore trois mois avant la récolte; et j'ai fait pleuvoir sur une ville, et a fait en sorte qu'il ne pleuve pas sur une autre ville. Un terrain a été touché par la pluie, et le champ où il n'a pas plu s'est desséché.
“Na kuma hana muku ruwan sama tun shuke-shuken suna wata uku kafin lokacin girbi. Na sa aka yi ruwan sama a wani gari, sai na hana a yi a wani gari. Wata gona ta sami ruwan sama; wata gona kuma ta bushe.
8 Ainsi, deux ou trois villes se sont rendues dans une seule ville pour boire de l'eau, et n'étaient pas satisfaits; et vous n'êtes pas revenus vers moi, dit Yahvé.
Mutane suna tangaɗi daga gari zuwa gari suna neman ruwa amma ba su sami isashen ruwan sha ba, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
9 « Je t'ai frappé plusieurs fois de mildiou et d'oïdium dans tes jardins et tes vignes, et les sauterelles ont dévoré tes figuiers et tes oliviers; et vous n'êtes pas revenus vers moi, dit Yahvé.
“Sau da yawa na ɓata gonakinku da fumfuna da kuma cuta. Fāri suka cinye itatuwanku na inabi da na ɓaure, da na zaitun duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
10 « J'ai envoyé des fléaux parmi vous comme j'ai fait en Égypte. J'ai tué vos jeunes hommes par l'épée, et ont emporté vos chevaux. J'ai rempli vos narines de la puanteur de votre camp, et vous n'êtes pas revenus vers moi, dit Yahvé.
“Na aiko muku annoba yadda na yi a Masar. Na karkashe samarinku da takobi, tare da kamammun dawakanku. Na cika hancinku da warin sansaninku, duk da haka ba ku juyo gare ni ba” in ji Ubangiji.
11 « J'ai renversé certains d'entre vous, comme lorsque Dieu a renversé Sodome et Gomorrhe, et vous étiez comme un bâton brûlant arraché du feu; et vous n'êtes pas revenus vers moi, dit Yahvé.
“Na hallaka waɗansunku kamar yadda na hallaka Sodom da Gomorra. Kuna kama da itace mai cin wutar da na cire daga cikin wuta, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
12 « C'est pourquoi je vais te faire ceci, Israël; parce que je vais te faire ça, préparez-vous à rencontrer votre Dieu, Israël.
“Saboda haka ga abin da zan yi da ku, ya Isra’ila, don kuwa zan yi muku haka, sai ku yi shirin gamuwa da Allahnku, ya Isra’ila.”
13 Car voici, celui qui forme les montagnes, crée le vent, déclare à l'homme ce qu'il pense, qui rend le matin obscur, et foule les hauteurs de la terre: Yahvé, le Dieu des armées, est son nom. »
Shi wanda ya yi duwatsu, ya halicci iska, ya kuma bayyana wa mutum tunaninsa, shi wanda ya juya safiya ta zama duhu yana takawa a wurare masu tsawo na duniya, Ubangiji Allah Maɗaukaki ne sunansa.

< Amos 4 >