< Amos 3 >

1 Écoutez cette parole que Yahvé a prononcée contre vous, enfants d'Israël, contre toute la famille que j'ai fait monter du pays d'Égypte, en disant:
Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
2 « Je t'ai seulement choisi parmi toutes les familles de la terre. C'est pourquoi je vous punirai pour tous vos péchés. »
“Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
3 Deux personnes marchent ensemble, à moins qu'ils ne soient d'accord?
Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
4 Le lion rugit dans le fourré, quand il n'a pas de proie? Est-ce qu'un jeune lion crie hors de sa tanière, s'il n'a rien attrapé?
Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
5 Un oiseau peut-il tomber dans un piège sur la terre, où aucun piège ne lui est tendu? Est-ce qu'un piège jaillit du sol, quand il n'y a rien à attraper?
Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
6 Est-ce que l'alarme de la trompette sonne dans une ville, sans que les gens aient peur? Le mal arrive-t-il à une ville, et Yahvé ne l'a pas fait?
Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
7 Le Seigneur Yahvé ne fera rien, à moins qu'il ne révèle son secret à ses serviteurs les prophètes.
Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
8 Le lion a rugi. Qui n'aura pas peur? Le Seigneur Yahvé a parlé. Qui ne peut que prophétiser?
Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
9 Proclamez dans les palais d'Ashdod, et dans les palais du pays d'Égypte, et dire: « Rassemblez-vous sur les montagnes de Samarie, et voir quelle agitation règne en elle, et quelle oppression il y a parmi eux. »
Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
10 « En effet, ils ne savent pas faire le bien, dit l'Éternel, « Qui amassent le pillage et le butin dans leurs palais. »
“Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
11 C'est pourquoi le Seigneur Yahvé dit: « Un adversaire envahira le pays; et il abattra vos forteresses, et vos forteresses seront pillées. »
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
12 Yahvé dit: « Comme le berger qui sauve de la gueule du lion deux pattes, ou un morceau d'oreille, Ainsi seront sauvés les enfants d'Israël qui sont assis à Samarie sur le coin d'un divan, et sur les coussins de soie d'un lit. »
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
13 « Écoutez, et témoignez contre la maison de Jacob, dit le Seigneur Yahvé, le Dieu des armées.
“Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
14 « Car le jour où je visiterai sur lui les transgressions d'Israël, Je visiterai aussi les autels de Béthel; et les cornes de l'autel seront coupées, et tombent sur le sol.
“A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
15 Je frapperai la maison d'hiver avec la maison d'été; et les maisons d'ivoire périront, et les grandes maisons auront une fin, » dit Yahvé.
Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.

< Amos 3 >