< 2 Samuel 1 >

1 Après la mort de Saül, David revenait de la tuerie des Amalécites, et il était resté deux jours à Tsiklag.
Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
2 Le troisième jour, voici qu'un homme sortit du camp de la part de Saül, les vêtements déchirés et de la terre sur la tête. Lorsqu'il arriva à David, il se jeta à terre et lui témoigna du respect.
A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
3 David lui dit: « D'où viens-tu? » Il lui dit: « Je me suis échappé du camp d'Israël. »
Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
4 David lui dit: « Comment cela s'est-il passé? Dis-le-moi. » Il répondit: « Le peuple a fui la bataille, et beaucoup de gens sont tombés et sont morts. Saül et son fils Jonathan sont morts eux aussi. »
Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
5 David dit au jeune homme qui lui avait raconté: « Comment sais-tu que Saül et Jonathan, son fils, sont morts? »
Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
6 Le jeune homme qui le raconta dit: « Comme je me trouvais par hasard sur la montagne de Gilboa, voici que Saül s'appuyait sur sa lance; et voici que les chars et les cavaliers suivaient de près derrière lui.
Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
7 Quand il regarda derrière lui, il me vit et m'appela. Je répondis: Me voici!
Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
8 Il me dit: « Qui es-tu? Je lui répondis: Je suis un Amalécite.
“Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
9 Il me dit: « Mets-toi à côté de moi, je t'en prie, et tue-moi, car l'angoisse s'est emparée de moi, parce que ma vie est encore en moi.
“Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
10 Je me suis donc tenu à côté de lui et je l'ai tué, car j'étais sûr qu'il ne pourrait pas vivre après sa chute. J'ai pris la couronne qui était sur sa tête et le bracelet qui était à son bras, et je les ai apportés ici à mon seigneur. »
“Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
11 Alors David saisit ses vêtements et les déchira, et tous les hommes qui étaient avec lui firent de même.
Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
12 Ils se lamentèrent, pleurèrent et jeûnèrent jusqu'au soir sur Saül et sur Jonathan, son fils, sur le peuple de l'Éternel et sur la maison d'Israël, parce qu'ils étaient tombés par l'épée.
Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
13 David dit au jeune homme qui lui a parlé: « D'où viens-tu? » Il répondit: « Je suis le fils d'un étranger, un Amalécite. »
Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
14 David lui dit: « Pourquoi n'as-tu pas eu peur d'étendre ta main pour faire périr l'oint de Yahvé? ».
Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
15 David appela l'un des jeunes hommes et dit: « Approche, et coupe-le! ». Il le frappa de telle sorte qu'il mourut.
Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
16 David lui dit: « Que ton sang retombe sur ta tête, car ta bouche a rendu témoignage contre toi, en disant: J'ai tué l'oint de l'Éternel. »
Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
17 David se lamenta ainsi sur Saül et sur Jonathan, son fils
Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
18 (et il leur ordonna d'enseigner aux fils de Juda le chant de l'arc; voici, cela est écrit dans le livre de Jashar):
Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
19 « Ta gloire, Israël, a été tuée sur tes hauts lieux! Comme les puissants sont tombés!
“Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
20 Ne le dis pas à Gath. Ne le publiez pas dans les rues d'Ashkelon, de peur que les filles des Philistins ne se réjouissent, de peur que les filles des incirconcis ne triomphent.
“Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
21 Vous les montagnes de Gilboa, qu'il n'y ait ni rosée ni pluie sur vous, et pas de champs d'offrandes; car c'est là que le bouclier des puissants a été souillé et jeté, le bouclier de Saul n'a pas été oint d'huile.
“Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
22 Du sang des victimes, de la graisse des puissants, L'arc de Jonathan ne s'est pas retourné. L'épée de Saul n'est pas revenue vide.
“Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
23 Saül et Jonathan étaient charmants et agréables dans leur vie. Dans leur mort, ils n'ont pas été divisés. Ils étaient plus rapides que les aigles. Ils étaient plus forts que des lions.
Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
24 Filles d'Israël, pleurez sur Saül, qui t'a délicatement vêtu d'écarlate, qui ont mis des ornements d'or sur vos vêtements.
“Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
25 Comme les puissants sont tombés au milieu de la bataille! Jonathan a été tué sur vos hauts lieux.
“Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
26 Je suis dans l'angoisse pour toi, mon frère Jonathan. Vous avez été très agréable avec moi. Ton amour pour moi était merveilleux, surpassant l'amour des femmes.
Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
27 Comme les puissants sont tombés, et les armes de guerre ont péri! »
“Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”

< 2 Samuel 1 >