< 2 Samuel 9 >

1 David dit: « Y a-t-il encore quelqu'un qui reste de la maison de Saül, pour que je lui fasse du bien à cause de Jonathan? »
Wata rana Dawuda ya yi tambaya ya ce, “Akwai wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu wanda zan nuna masa alheri saboda Yonatan?”
2 Il y avait dans la maison de Saül un serviteur dont le nom était Tsiba, et on l'appela auprès de David; le roi lui dit: « Es-tu Tsiba? ». Il a dit: « Je suis ton serviteur. »
To, akwai wani bawa na gidan Shawulu mai suna Ziba. Sai aka kira shi yă bayyana a gaban Dawuda, sarki ya ce masa, “Kai ne Ziba?” Sai ya ce, “I, ni ne, ranka yă daɗe.”
3 Le roi dit: « N'y a-t-il pas encore quelqu'un de la maison de Saül, pour que je puisse lui montrer la bonté de Dieu? » Ziba dit au roi: « Jonathan a encore un fils, qui boite des pieds. »
Sa’an nan sarki ya yi tambaya ya ce, “Babu wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu don in nuna masa alherin Allah?” Ziba ya ce wa sarki, “Har yanzu akwai ɗan Yonatan da ya rage, sai dai shi gurgu ne a dukan ƙafafu.”
4 Le roi lui dit: « Où est-il? » Ziba dit au roi: « Voici, il est dans la maison de Makir, fils d'Ammiel, à Lo Debar. »
Sarki ya ce, “Ina yake?” Ziba ya ce, “Yana a gidan Makir ɗan Ammiyel a Lo Debar.”
5 Le roi David l'envoya chercher dans la maison de Makir, fils d'Ammiel, à Lo Debar.
Saboda haka Sarki Dawuda ya umarta aka kawo shi daga gidan Makir ɗan Ammiyel, daga Lo Debar.
6 Mephiboscheth, fils de Jonathan, fils de Saül, vint auprès de David, tomba sur sa face et lui témoigna du respect. David dit: « Mephibosheth? » Il répondit: « Voici ton serviteur! »
Sa’ad da Mefiboshet ɗan Yonatan, ɗan Shawulu, ya zo wurin Dawuda, sai ya rusuna har ƙasa ya yi gaisuwar bangirma. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Shi kuwa ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, ga ni, bawanka.”
7 David lui dit: « N'aie pas peur, car je te ferai du bien à cause de Jonathan, ton père, et je te rendrai tout le pays de Saül, ton père. Tu mangeras continuellement du pain à ma table. »
Dawuda ya ce, “Kada ka ji tsoro, gama tabbatacce zan nuna maka alheri saboda mahaifinka Yonatan. Zan mayar maka da dukan ƙasar da take ta kakanka Shawulu, kullum kuma za ka ci a teburina.”
8 Il se prosterna, et dit: « Quel est ton serviteur, pour que tu regardes un chien mort comme moi? »
Mefiboshet ya rusuna ya ce, “Ni ne wa har da za ka kula da ni? Ai! Ni bawanka ne da bai ma fi mataccen kare daraja ba.”
9 Le roi appela Tsiba, serviteur de Saül, et lui dit: « Je donne au fils de ton maître tout ce qui appartenait à Saül et à toute sa maison.
Sai sarki ya kira Ziba bawan Shawulu, ya ce masa, “Na ba wa jikan maigidanka kome da yake na Shawulu da iyalinsa
10 Cultivez pour lui le pays, vous, vos fils et vos serviteurs. Fais la moisson, afin que le fils de ton maître ait du pain à manger; mais Mephibosheth, le fils de ton maître, mangera toujours du pain à ma table. » Or Tsiba avait quinze fils et vingt serviteurs.
Kai da’ya’yanka maza da bayinka za ku riƙa yin masa noma, ku kuma kawo hatsin, don jikan maigidanka yă sami abinci. Mefiboshet kuma, jikan maigidanka, zai riƙa ci a teburina.” (Ziba kuwa yana da’ya’ya maza goma sha biyar da kuma bayi ashirin.)
11 Et Tsiba dit au roi: « Tout ce que mon seigneur le roi ordonne à son serviteur, ton serviteur le fera aussi. » Mephibosheth mangea donc à la table du roi comme l'un des fils du roi.
Sai Ziba ya ce wa sarki, “Bawanka zai aikata dukan abin da ranka yă daɗe sarki, ya umarce shi.” Saboda haka Mefiboshet ya riƙa ci a teburin Dawuda kamar sauran’ya’yan sarki.
12 Mephibosheth avait un jeune fils, dont le nom était Mica. Tous ceux qui habitaient dans la maison de Tsiba étaient les serviteurs de Mephibosheth.
Mefiboshet yana da wani ƙaramin ɗa sunansa Mika, dukan iyalin gidan Ziba kuwa bayin Mefiboshet ne.
13 Mephibosheth habitait donc à Jérusalem, car il mangeait continuellement à la table du roi. Il était boiteux des deux pieds.
Mefiboshet ya zauna a Urushalima, gama kullum yana ci a teburin sarki, shi kuwa gurgu ne a dukan ƙafafu.

< 2 Samuel 9 >