< 2 Samuel 6 >

1 David rassembla de nouveau tous les hommes d'élite d'Israël, au nombre de trente mille.
Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
2 David se leva et partit avec tout le peuple qui était avec lui de Baalé Juda, pour faire monter de là l'arche de Dieu, qui porte le nom, le nom de l'Éternel des armées, qui est assis au-dessus des chérubins.
Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
3 Ils mirent l'arche de Dieu sur un char neuf, et la firent sortir de la maison d'Abinadab, qui était sur la colline; Uzza et Ahio, les fils d'Abinadab, conduisaient le char neuf.
Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
4 Ils le firent sortir de la maison d'Abinadab, qui était sur la colline, avec l'arche de Dieu; et Achio marchait devant l'arche.
da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
5 David et toute la maison d'Israël jouèrent devant l'Éternel avec toutes sortes d'instruments en bois de cyprès, avec des harpes, des instruments à cordes, des tambourins, des castagnettes et des cymbales.
Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
6 Lorsqu'ils arrivèrent à l'aire de Nacon, Uzza tendit le bras vers l'arche de Dieu et la saisit, car le bétail trébuchait.
Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
7 La colère de l'Éternel s'enflamma contre Uzza, et Dieu le frappa là pour sa faute; il mourut là près de l'arche de Dieu.
Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
8 David fut mécontent parce que l'Éternel s'était déchaîné contre Uzza, et il appela ce lieu Perez Uzza jusqu'à ce jour.
Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
9 David eut peur de l'Éternel ce jour-là, et il dit: « Comment l'arche de l'Éternel pourrait-elle venir à moi? »
Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
10 Et David ne voulut pas déplacer l'arche de Yahvé pour qu'elle soit avec lui dans la ville de David; mais David la transporta à l'écart, dans la maison d'Obed-Edom, le Gittien.
Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
11 L'arche de Yahvé resta trois mois dans la maison d'Obed-Edom, le Gittien, et Yahvé bénit Obed-Edom et toute sa maison.
Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
12 On dit au roi David: « Yahvé a béni la maison d'Obed-Edom et tout ce qui lui appartient, à cause de l'arche de Dieu. » David partit donc et fit monter l'arche de Dieu de la maison d'Obed-Edom dans la ville de David, avec joie.
To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
13 Lorsque ceux qui portaient l'arche de Yahvé eurent fait six pas, il sacrifia un bœuf et un veau gras.
Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
14 David dansa devant Yahvé de toutes ses forces, et David était vêtu d'un éphod de lin.
Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
15 Et David et toute la maison d'Israël firent monter l'arche de Yahvé avec des cris et au son de la trompette.
yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
16 Comme l'arche de l'Éternel entrait dans la ville de David, Mical, fille de Saül, regarda par la fenêtre et vit le roi David qui sautait et dansait devant l'Éternel; et elle le méprisa dans son cœur.
Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
17 On fit entrer l'arche de l'Éternel et on la plaça au milieu de la tente que David avait dressée pour elle; et David offrit des holocaustes et des sacrifices de prospérité devant l'Éternel.
Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
18 Lorsque David eut fini d'offrir les holocaustes et les sacrifices de paix, il bénit le peuple au nom de l'Éternel des armées.
Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
19 Il donna à tout le peuple, à toute la multitude d'Israël, aux hommes et aux femmes, à chacun une portion de pain, des dattes et des raisins secs. Et tout le peuple s'en alla, chacun dans sa maison.
Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
20 Puis David s'en retourna pour bénir sa maison. Mical, fille de Saül, sortit à la rencontre de David et dit: « Quelle gloire pour le roi d'Israël, qui s'est découvert aujourd'hui aux yeux des servantes de ses serviteurs, comme se découvre sans vergogne l'un de ces vaniteux! »
Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
21 David dit à Mical: « C'est devant Yahvé, qui m'a choisi au-dessus de ton père et de toute sa maison, pour m'établir prince sur le peuple de Yahvé, sur Israël. C'est pourquoi je me réjouirai devant Yahvé.
Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
22 Je serai encore plus indigne que cela, et je serai sans valeur à mes propres yeux. Mais les jeunes filles dont tu as parlé m'honoreront. »
Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
23 Mical, fille de Saül, n'eut pas d'enfant jusqu'au jour de sa mort.
Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.

< 2 Samuel 6 >