< 2 Samuel 4 >

1 Lorsque le fils de Saül apprit qu'Abner était mort à Hébron, ses mains devinrent faibles, et tous les Israélites furent troublés.
Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
2 Le fils de Saül avait deux hommes qui étaient chefs de bandes de pillards. L'un s'appelait Baana et l'autre Rechab, fils de Rimmon, le Beérothien, d'entre les fils de Benjamin (car Beéroth est aussi considéré comme faisant partie de Benjamin;
To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
3 et les Beérothiens se sont enfuis à Gittaïm, où ils ont vécu comme des étrangers jusqu'à ce jour).
domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
4 Or Jonathan, fils de Saül, avait un fils qui était boiteux des pieds. Il avait cinq ans lorsque la nouvelle de la mort de Saül et de Jonathan arriva de Jizreel; sa nourrice le prit et s'enfuit. Comme elle se hâtait de fuir, il tomba et devint boiteux. Il s'appelait Mephibosheth.
(Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
5 Les fils de Rimmon, le Beérothien, Rechab et Baana, sortirent et vinrent, vers la chaleur du jour, à la maison d'Ishbosheth, qui se reposait à midi.
To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
6 Là, ils entrèrent au milieu de la maison comme s'ils voulaient aller chercher du blé, et ils le frappèrent au corps; et Rechab et Baana, son frère, échappèrent.
Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
7 Et quand ils entrèrent dans la maison, comme il était couché sur son lit dans sa chambre, ils le frappèrent, le tuèrent, le décapitèrent et prirent sa tête, et ils passèrent toute la nuit sur le chemin de la plaine.
Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
8 Ils apportèrent la tête d'Ishbosheth à David, à Hébron, et dirent au roi: « Voici la tête d'Ishbosheth, le fils de Saül, ton ennemi, qui en voulait à ta vie! Aujourd'hui, Yahvé a vengé mon seigneur le roi de Saül et de sa descendance. »
Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
9 David prit la parole devant Rechab et Baana, son frère, fils de Rimmon, le Beérothite, et leur dit: « L'Éternel est vivant, lui qui a racheté mon âme de toute détresse.
Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
10 Quand quelqu'un m'a dit: « Voici Saül mort », pensant qu'il apportait une bonne nouvelle, je l'ai saisi et je l'ai tué à Tsiklag, ce qui était la récompense que je lui donnais pour sa nouvelle.
sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
11 A plus forte raison, lorsque des méchants ont tué un juste dans sa propre maison, sur son lit, ne devrais-je pas exiger son sang de ta main et débarrasser la terre de toi? ».
Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
12 David donna des ordres à ses jeunes gens, qui les tuèrent, leur coupèrent les mains et les pieds et les pendirent au bord de l'étang d'Hébron. Mais ils prirent la tête d'Ishbosheth et l'enterrèrent dans le tombeau d'Abner à Hébron.
Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.

< 2 Samuel 4 >