< 2 Samuel 24 >

1 La colère de Yahvé s'enflamma de nouveau contre Israël, et il poussa David contre eux, en disant: « Va, fais le compte d'Israël et de Juda. »
Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
2 Le roi dit à Joab, chef de l'armée, qui était avec lui: « Maintenant, va et viens dans toutes les tribus d'Israël, depuis Dan jusqu'à Beersheba, et compte le peuple, afin que je connaisse la somme du peuple. »
Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
3 Joab dit au roi: « Que Yahvé, ton Dieu, ajoute maintenant cent fois au peuple, quel que soit son nombre, et que les yeux de mon seigneur le roi le voient. Mais pourquoi mon seigneur le roi se réjouit-il de cette chose? »
Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
4 Néanmoins, la parole du roi l'emporta sur Joab et sur les chefs de l'armée. Joab et les chefs de l'armée sortirent de la présence du roi pour compter le peuple d'Israël.
Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
5 Ils passèrent le Jourdain et campèrent à Aroër, à droite de la ville qui est au milieu de la vallée de Gad, et jusqu'à Jazer;
Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
6 puis ils vinrent en Galaad et au pays de Tahtim Hodshi; ils vinrent à Dan Jaan et contournèrent Sidon,
Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
7 ils arrivèrent à la forteresse de Tyr et à toutes les villes des Héviens et des Cananéens, et ils sortirent au sud de Juda, à Beer Schéba.
Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
8 Après avoir parcouru tout le pays, ils arrivèrent à Jérusalem au bout de neuf mois et vingt jours.
Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
9 Joab remit au roi le compte du peuple. Il y avait en Israël huit cent mille hommes vaillants tirant l'épée, et en Juda cinq cent mille hommes.
Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
10 Le cœur de David le frappa après qu'il eut compté le peuple. David dit à Yahvé: « J'ai beaucoup péché par ce que j'ai fait. Mais maintenant, Yahvé, efface, je t'en prie, l'iniquité de ton serviteur, car j'ai fait une grande folie. »
Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
11 Lorsque David se leva le matin, la parole de Yahvé fut adressée au prophète Gad, le voyant de David, en ces termes:
Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
12 « Va dire à David: « Yahvé dit: Je te propose trois choses. Choisis l'une d'elles, que je te l'accorde »".
“Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
13 Gad se rendit auprès de David et lui dit: « Est-ce que sept années de famine t'arriveront dans ton pays? Ou bien fuiras-tu trois mois devant tes ennemis pendant qu'ils te poursuivent? Ou bien y aura-t-il trois jours de peste dans ton pays? Réponds maintenant, et considère quelle réponse je ferai à celui qui m'a envoyé. »
Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
14 David dit à Gad: « Je suis dans la détresse. Tombons maintenant dans la main de Yahvé, car sa miséricorde est grande. Que je ne tombe pas dans la main de l'homme. »
Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
15 Et l'Éternel envoya la peste sur Israël, depuis le matin jusqu'à l'heure fixée, et il mourut soixante-dix mille hommes du peuple, depuis Dan jusqu'à Beersheba.
Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
16 Lorsque l'ange étendit sa main vers Jérusalem pour la détruire, Yahvé se détourna du désastre et dit à l'ange qui détruisait le peuple: « C'est assez. Maintenant, retire ta main. » L'ange de Yahvé était près de l'aire de battage d'Arauna, le Jébusien.
Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
17 David s'adressa à Yahvé lorsqu'il vit l'ange qui frappait le peuple, et il dit: « Voici, j'ai péché et j'ai agi avec perversité; mais ces brebis, qu'ont-elles fait? Je t'en prie, que ta main soit contre moi et contre la maison de mon père. »
Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
18 Gad vint ce jour-là auprès de David et lui dit: « Monte, bâtis un autel à Yahvé sur l'aire d'Arauna, le Jébusien. »
A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
19 David monta, selon la parole de Gad, comme l'avait ordonné l'Éternel.
Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
20 Arauna regarda dehors et vit le roi et ses serviteurs qui venaient vers lui. Alors Arauna sortit et se prosterna devant le roi, le visage contre terre.
Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
21 Aravna dit: « Pourquoi le roi mon seigneur est-il venu vers son serviteur? » David dit: « Pour acheter ton aire, pour construire un autel à Yahvé, afin que la peste cesse d'affliger le peuple. »
Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
22 Arauna dit à David: « Que le roi mon seigneur prenne et offre ce qui lui semble bon. Voici le bétail pour l'holocauste, les traîneaux à battre et les jougs des bœufs pour le bois.
Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
23 Tout cela, ô roi, Arauna le donne au roi. » Aravna dit au roi: « Que Yahvé ton Dieu t'accueille. »
Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
24 Le roi dit à Arauna: « Non, mais je veux bien te l'acheter à prix d'or. Je ne veux pas offrir à Yahvé mon Dieu des holocaustes qui ne me coûtent rien. » David acheta donc l'aire et les bœufs pour cinquante sicles d'argent.
Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
25 David bâtit là un autel à Yahvé, et il offrit des holocaustes et des sacrifices de prospérité. Il implora Yahvé pour le pays, et la plaie fut retirée d'Israël.
Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.

< 2 Samuel 24 >