< 2 Samuel 22 >

1 David adressa à Yahvé les paroles de ce cantique, le jour où Yahvé le délivra de la main de tous ses ennemis et de la main de Saül,
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 et il dit: « Yahvé est mon rocher, ma forteresse, et mon libérateur, même le mien;
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 Dieu est mon rocher, en qui je trouve refuge; mon bouclier, et la corne de mon salut, ma haute tour et mon refuge. Mon sauveur, tu me sauves de la violence.
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 J'invoque Yahvé, qui est digne d'être loué; Ainsi je serai sauvé de mes ennemis.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 Car les vagues de la mort m'ont entouré. Les flots de l'impiété m'ont fait peur.
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 Les cordes du séjour des morts m'entouraient. Les pièges de la mort m'ont attrapé. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
7 Dans ma détresse, j'ai invoqué Yahvé. Oui, j'ai appelé mon Dieu. Il a entendu ma voix hors de sa tempe. Mon cri est parvenu à ses oreilles.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 Alors la terre trembla et s'ébranla. Les fondations du ciel ont tremblé et ont été ébranlées, parce qu'il était en colère.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 De la fumée sortait de ses narines. Un feu dévorant est sorti de sa bouche. Des charbons ont été allumés par elle.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 Il a aussi incliné les cieux, et il est descendu. Une obscurité épaisse était sous ses pieds.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 Il était monté sur un chérubin, et il volait. Oui, il a été vu sur les ailes du vent.
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 Il a fait des ténèbres un abri autour de lui, le rassemblement des eaux, et les nuages épais des cieux.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 A la clarté devant lui, des charbons ardents ont été allumés.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 Yahvé tonna du ciel. Le Très-Haut a fait entendre sa voix.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 Il envoya des flèches et les dispersa, des éclairs et les a rendus confus.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 Alors les canaux de la mer apparurent. Les fondations du monde ont été mises à nu par la réprimande de Yahvé, au souffle de ses narines.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 Il a envoyé d'en haut et il m'a pris. Il m'a tiré de nombreuses eaux.
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 Il m'a délivré de mon ennemi puissant, de ceux qui me haïssaient, car ils étaient trop puissants pour moi.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 Ils sont venus sur moi au jour de ma calamité, mais Yahvé était mon soutien.
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 Il m'a aussi fait sortir dans un grand lieu. Il m'a délivré, car il s'est réjoui de moi.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 L'Éternel m'a récompensé selon ma justice. Il m'a récompensé selon la propreté de mes mains.
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 Car j'ai gardé les voies de l'Éternel, et je ne me suis pas éloigné de mon Dieu par méchanceté.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 Car toutes ses ordonnances étaient devant moi. Quant à ses statuts, je ne m'en suis pas écarté.
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 J'étais aussi parfait envers lui. Je me suis gardé de mon iniquité.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 C'est pourquoi Yahvé m'a récompensé selon ma justice, Selon ma propreté dans sa vue.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 Avec les miséricordieux, tu te montreras miséricordieux. Avec l'homme parfait, vous vous montrerez parfaite.
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 Avec les purs, tu te montreras pur. Avec les tordus, vous vous montrerez astucieux.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 Tu sauveras le peuple affligé, mais tes yeux sont sur les arrogants, pour les faire tomber.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 Car tu es ma lampe, Yahvé. Yahvé va éclairer mes ténèbres.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 Car par toi, je cours contre une troupe. Par mon Dieu, je saute par-dessus un mur.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 Quant à Dieu, sa voie est parfaite. La parole de Yahvé est mise à l'épreuve. Il est un bouclier pour tous ceux qui se réfugient en lui.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 Car qui est Dieu, en dehors de Yahvé? Qui est un rocher, à part notre Dieu?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 Dieu est ma forte forteresse. Il rend mon chemin parfait.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 Il rend ses pieds semblables à ceux des biches, et me place sur mes hauts lieux.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 Il apprend à mes mains à combattre, pour que mes bras fassent un arc de bronze.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 Tu m'as aussi donné le bouclier de ton salut. Votre gentillesse m'a rendu grand.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 Tu as élargi mes pas sous moi. Mes pieds n'ont pas glissé.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 J'ai poursuivi mes ennemis et je les ai détruits. Je ne me suis pas retourné jusqu'à ce qu'ils soient consommés.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 Je les ai consumés, et les a transpercés, pour qu'ils ne puissent pas surgir. Oui, ils sont tombés sous mes pieds.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 Car tu m'as armé de force pour le combat. Tu as soumis à moi ceux qui s'élevaient contre moi.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 Tu as aussi fait en sorte que mes ennemis me tournent le dos, afin d'exterminer ceux qui me haïssent.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 Ils regardèrent, mais il n'y avait personne à sauver; même à Yahvé, mais il ne leur a pas répondu.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 Puis je les ai battus comme de la poussière de la terre. Je les ai écrasés comme la boue des rues, et je les ai répandus.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 C'est toi aussi qui m'as délivré de l'oppression de mon peuple. Tu m'as gardé pour être le chef des nations. Un peuple que je n'ai pas connu me servira.
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 Les étrangers se soumettront à moi. Dès qu'ils entendront parler de moi, ils m'obéiront.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 Les étrangers disparaîtront, et sortiront en tremblant de leurs lieux clos.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 Yahvé est vivant! Béni soit mon rocher! Exalté soit Dieu, le rocher de mon salut,
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 même le Dieu qui exécute la vengeance pour moi, qui fait tomber les peuples sous mes ordres,
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 qui m'emmène loin de mes ennemis. Oui, tu me soulèves au-dessus de ceux qui s'élèvent contre moi. Tu me délivres de l'homme violent.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 C'est pourquoi je te louerai, Yahvé, parmi les nations, et chanteront les louanges de ton nom.
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 Il accorde une grande délivrance à son roi, et fait preuve de bonté envers ses oints, à David et à sa descendance, pour toujours. »
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”

< 2 Samuel 22 >