< 2 Samuel 2 >

1 Après cela, David consulta Yahvé, en disant: « Monterai-je dans l'une des villes de Juda? » Yahvé lui dit: « Monte. » David a dit: « Où dois-je monter? » Il a dit: « À Hébron. »
Bayan’yan kwanaki, sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In haura zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda?” Ubangiji ya ce, “Haura.” Dawuda ya ce, “Wanne zan tafi?” Ubangiji ya ce, “Je Hebron.”
2 Et David y monta avec ses deux femmes, Ahinoam, la Jizreélite, et Abigaïl, la femme de Nabal, le Carmélite.
Saboda haka sai Dawuda ya tafi can tare da matansa biyu, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel.
3 David fit monter les hommes qui étaient avec lui, chacun avec sa famille. Ils habitaient dans les villes d'Hébron.
Dawuda kuma ya tafi tare da dukan mutanen da suke tare da shi, kowa da iyalinsa, suka zauna a Hebron da garuruwansa.
4 Les hommes de Juda vinrent, et là ils oignirent David comme roi de la maison de Juda. Ils dirent à David: « Les hommes de Jabesh Galaad sont ceux qui ont enterré Saül. »
Sa’an nan mutanen Yahuda suka zo Hebron, a can kuwa suka naɗa Dawuda sarkin Yahuda. Sa’ad da aka gaya wa Dawuda cewa mutanen Yabesh Gileyad ne suka binne Shawulu,
5 David envoya des messagers aux hommes de Jabesh Galaad, et leur dit: « Vous êtes bénis par Yahvé de ce que vous avez fait preuve de cette bonté envers votre seigneur, même envers Saül, et que vous l'avez enterré.
sai ya aiki manzanni zuwa Yabesh Gileyad a ce musu, “Ubangiji yă albarkace ku saboda alherin da kuka nuna wa Shawulu ta wurin binne shi.
6 Que Yahvé vous fasse maintenant preuve de bonté et de vérité. Moi aussi, je te récompenserai de cette bonté, parce que tu as fait cela.
Bari Ubangiji yă nuna muku ƙaunarsa da amincinsa, ni kuma zan nuna muku irin wannan alherin saboda kun yi haka.
7 Maintenant, que tes mains soient fortes et vaillantes, car Saül, ton seigneur, est mort, et la maison de Juda m'a oint comme roi sur elle. »
Yanzu fa, sai ku ƙarfafa, ku yi jaruntaka, gama Shawulu sarkinku ya mutu, gidan Yahuda kuwa sun naɗa ni sarki a kansu.”
8 Abner, fils de Ner, chef de l'armée de Saül, avait pris Ischboscheth, fils de Saül, et l'avait amené à Mahanaïm.
Ana cikin haka, Abner ɗan Ner, komandan sojojin Shawulu, ya ɗauki Ish-Boshet ɗan Shawulu ya kawo shi Mahanayim.
9 Il l'établit roi sur Galaad, sur les Ashurites, sur Jezréel, sur Ephraïm, sur Benjamin et sur tout Israël.
Ya naɗa shi sarkin Gileyad, da na Ashuri, da na Yezireyel, da a kan Efraim, da Benyamin, da kuma na dukan Isra’ila.
10 Ishbosheth, fils de Saül, avait quarante ans lorsqu'il commença à régner sur Israël, et il régna deux ans. Mais la maison de Juda suivit David.
Ish-Boshet ɗan Shawulu yana da shekaru arba’in sa’ad da ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi sarauta shekara biyu. Amma fa, gidan Yahuda, suka bi Dawuda.
11 Le temps pendant lequel David fut roi à Hébron sur la maison de Juda fut de sept ans et six mois.
Tsawon lokacin da Dawuda ya yi mulki a Hebron a kan gidan Yahuda, shekara bakwai ne da wata shida.
12 Abner, fils de Ner, et les serviteurs d'Ischboscheth, fils de Saül, sortirent de Mahanaïm pour aller à Gabaon.
Abner ɗan Ner, tare da mutanen Ish-Boshet ɗan Shawulu, suka bar Mahanayim suka tafi Gibeyon.
13 Joab, fils de Tseruja, et les serviteurs de David sortirent et les rencontrèrent près de l'étang de Gabaon; ils s'assirent, l'un d'un côté de l'étang, l'autre de l'autre côté de l'étang.
Yowab wanda ake ce mamarsa Zeruhiya tare da waɗansu mutanen Dawuda suka fito suka haɗu da su tafkin Gibeyon, Suka zauna, waɗannan a wannan gefe, waɗancan a wancan gefe.
14 Abner dit à Joab: « Que les jeunes gens se lèvent et se battent devant nous! » Joab dit: « Qu'ils se lèvent! »
Sa’an nan Abner ya ce wa Yowab, “Bari mu bar waɗansu samari su tashi su yi faɗa hannu da hannu a gabanmu.” Yowab ya ce, “To, su tashi.”
15 Ils se levèrent et passèrent en revue par ordre de grandeur: douze pour Benjamin et pour Ishbosheth, fils de Saül, et douze des serviteurs de David.
Saboda haka samarin suka tashi aka ƙidaya su, mutum sha biyu wajen Benyamin da Ish-Boshet ɗan Shawulu, sha biyu kuma wajen Dawuda.
16 Chacun d'eux saisit son adversaire par la tête et enfonça son épée dans le flanc de son compagnon, et ils tombèrent ensemble. C'est pourquoi on appela ce lieu de Gabaon Helkath Hazzurim.
Sa’an nan kowannensu ya kama abokin gābansa a kā ya soki da wuƙa a jiki, sai duka suka fāɗi a ƙasa. Saboda haka ne ake kiran wannan wuri Helkat Hazzurim a Gibeyon.
17 Le combat fut très rude ce jour-là, et Abner fut battu, ainsi que les hommes d'Israël, devant les serviteurs de David.
Faɗan ya yi zafi a ranar ƙwarai, mutanen Dawuda suka ci mutanen Abner da na Isra’ila.
18 Les trois fils de Tseruja étaient là: Joab, Abischaï et Asaël. Asaël avait le pied léger comme une gazelle sauvage.
’Ya’yan Zeruhiya, maza uku sun kasance a can. Su ne, Yowab, Abishai da Asahel. To, Asahel mai gudu ne kamar barewa.
19 Asaël poursuivit Abner. Il ne se tourna ni à droite ni à gauche pour suivre Abner.
Ya fafari Abner, bai juya dama ko hagu ba, yayinda yake fafararsa.
20 Alors Abner regarda derrière lui et dit: « C'est toi, Asahel? » Il a répondu: « C'est le cas. »
Abner ya waiga, sai ya ce, “Kai ne, Asahel?” Ya ce, “Ni ne.”
21 Abner lui dit: « Détourne-toi à droite ou à gauche, saisis un des jeunes gens et prends son armure. » Mais Asaël ne voulut pas se détourner de lui.
Sai Abner ya ce masa, “Yi dama ko hagu ka runtumi ɗaya daga cikin samarin, ka ƙwace makamansa.” Amma Asahel bai bar fafararsa ba.
22 Abner dit encore à Asaël: « Détourne-toi de moi. Pourquoi te frapperais-je à terre? Comment pourrais-je alors regarder Joab, ton frère, en face? »
Abner ya sāke gargaɗe shi ya ce, “Ka bar fafarata! Yaya zan kashe ka? Yaya zan yin ido biyu da ɗan’uwanka Yowab?”
23 Mais il refusa de se détourner. Alors Abner, avec l'extrémité arrière de la lance, le frappa au corps, de sorte que la lance sortit derrière lui; il tomba là et mourut au même endroit. Tous ceux qui arrivèrent au lieu où Asaël était tombé et était mort s'arrêtèrent.
Amma Asahel ya ƙi yă bar fafararsa; saboda haka Abner ya soki Asahel da māshinsa a ciki; har māshin ya fita ta bayansa. Nan take ya fāɗi, ya mutu. Kowa da ya zo wurin da Asahel ya fāɗi, ya mutu, sai yă tsaya.
24 Joab et Abishaï poursuivirent Abner. Le soleil se couchait lorsqu'ils arrivèrent à la colline d'Amma, qui est en face de Gia, sur le chemin du désert de Gabaon.
Amma Yowab da Abishai suka fafari Abner, kuma da rana tana fāɗuwa sai suka iso tudun Amma, kusa da Giya, a hanyar zuwa jejin Gibeyon.
25 Les fils de Benjamin se rassemblèrent après Abner et formèrent une seule bande, et ils se tinrent sur le sommet d'une colline.
Sa’an nan mutanen Benyamin suka haɗa kansu suka koyi bayan Abner. Suka zama ƙungiya guda, suka tsaya daram a kan tudu.
26 Abner appela Joab, et dit: « L'épée dévorera-t-elle à jamais? Ne sais-tu pas qu'il y aura de l'amertume à la fin? Combien de temps s'écoulera-t-il donc avant que tu demandes au peuple de ne plus suivre ses frères? »
Sai Abner ya kira Yowab ya ce, har abada ne māshi zai yi ta hallakarwa? Ba ka sani cewa ƙarshen zai zama da ɗaci ba. Sai yaushe za ka umarci mutanenka su daina fafaran’yan’uwansu?
27 Joab dit: « Dieu est vivant! Si tu n'avais pas parlé, le matin, le peuple serait parti, et chacun n'aurait pas suivi son frère. »
Yowab ya ce, “Muddin Allah yana a raye, da ba a ce ka yi magana ba, da mutanen za su ci gaba da fafaran’yan’uwansu har gari yă waye.”
28 Joab sonna de la trompette; tout le peuple s'arrêta et ne poursuivit plus Israël, et ils ne combattirent plus.
Sai Yowab ya busa ƙaho, dukan mutane kuwa suka tsaya; suka daina fafaran Isra’ila. Nan take faɗan ya tsaya.
29 Abner et ses hommes passèrent toute cette nuit-là par la plaine; ils passèrent le Jourdain, traversèrent tout Bithron et arrivèrent à Mahanaïm.
Abner da mutanensa suka ratsa kwarin Urdun dukan dare. Sa’an nan suka haye kogin, suka kuwa ci gaba dukan safe har suka zo Mahanayim.
30 Joab revint après avoir suivi Abner; et quand il eut rassemblé tout le peuple, il manqua dix-neuf hommes de David et Asahel.
Da Yowab ya dawo daga fafaran Abner, sai ya tattara dukan mutanensa. Ban da Asahel, sai ya gane an rasa mutum goma sha tara na Dawuda.
31 Mais les serviteurs de David avaient frappé les hommes de Benjamin Abner, de sorte que trois cent soixante hommes étaient morts.
Amma mutanen Dawuda sun kashe mutum ɗari uku da sittin daga kabilar Benyamin da suke tare da Abner.
32 On emporta Asaël et on l'enterra dans le tombeau de son père, qui était à Bethléem. Joab et ses hommes marchèrent toute la nuit, et le jour se leva sur eux à Hébron.
Suka ɗauki gawar Asahel suka binne a kabarin mahaifinsa a Betlehem. Sa’an nan Yowab da mutanensa suka bi dare har suka iso Hebron da safe.

< 2 Samuel 2 >