< 2 Samuel 17 >

1 Achitophel dit à Absalom: Laisse-moi maintenant choisir douze mille hommes, je me lèverai et je poursuivrai David cette nuit.
Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
2 J'arriverai sur lui pendant qu'il sera fatigué et épuisé, et je l'effrayerai. Tout le peuple qui est avec lui s'enfuira. Je ne frapperai que le roi,
Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
3 et je ramènerai tout le peuple vers toi. L'homme que tu cherches est comme si tous étaient revenus. Tout le peuple sera en paix. »
in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
4 Cette parole plut à Absalom et à tous les anciens d'Israël.
Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
5 Et Absalom dit: « Maintenant, appelez aussi Huschaï, l'Architecte, et écoutons de même ce qu'il dira. »
Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
6 Lorsque Huschaï fut arrivé auprès d'Absalom, celui-ci lui parla ainsi: « Ahithophel a parlé ainsi. Faisons-nous ce qu'il dit? Sinon, parlez. »
Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
7 Huschaï dit à Absalom: « Le conseil qu'Ahitophel a donné cette fois-ci n'est pas bon. »
Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
8 Huschaï dit encore: « Tu connais ton père et ses hommes, ce sont des hommes puissants, et ils sont féroces dans leur esprit, comme une ourse qui a volé ses petits dans les champs. Ton père est un homme de guerre, et il ne veut pas loger avec le peuple.
Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
9 Voici, il est maintenant caché dans quelque fosse, ou dans quelque autre lieu. Lorsque quelques-uns d'entre eux seront tombés les premiers, quiconque l'entendra dira: « Il y a un massacre parmi le peuple qui suit Absalom! »
Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
10 Même celui qui est vaillant et dont le cœur est comme celui d'un lion se fondra dans la masse; car tout Israël sait que ton père est un homme puissant et que ceux qui sont avec lui sont des hommes vaillants.
Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
11 Mais je conseille que tout Israël se rassemble autour de toi, depuis Dan jusqu'à Beersheba, comme le sable qui est au bord de la mer pour la multitude, et que tu ailles au combat dans ta propre personne.
“Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
12 Nous l'atteindrons dans quelque lieu où il se trouvera, et nous l'éclairerons comme la rosée tombe sur le sol; puis nous ne laisserons pas un seul de lui et de tous les hommes qui sont avec lui.
Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
13 De plus, s'il est entré dans une ville, tout Israël apportera des cordes à cette ville, et nous la tirerons dans le fleuve, jusqu'à ce qu'il ne s'y trouve plus une seule petite pierre. »
In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
14 Absalom et tous les hommes d'Israël dirent: « Le conseil de Huschaï, l'Architecte, vaut mieux que le conseil d'Achitophel. » Car Yahvé avait décidé de faire échouer le bon conseil d'Achitophel, afin que Yahvé fasse venir le malheur sur Absalom.
Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
15 Alors Huschaï dit aux sacrificateurs Tsadok et Abiathar: Ahithophel a conseillé à Absalom et aux anciens d'Israël de suivre cette voie, et moi j'ai conseillé de suivre cette voie.
Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
16 Maintenant, envoie vite dire à David: « Ne passe pas cette nuit aux gués du désert, mais passe absolument, de peur que le roi et tout le peuple qui est avec lui ne soient engloutis ».
Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
17 Or Jonathan et Ahimaaz logeaient près d'En Rogel; une servante avait l'habitude d'aller leur faire des rapports, et ils allaient en parler au roi David, car ils ne pouvaient pas risquer d'être vus en entrant dans la ville.
Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
18 Mais un garçon les vit et le dit à Absalom. Tous deux s'en allèrent rapidement et arrivèrent à la maison d'un homme de Bahurim, qui avait un puits dans sa cour, et ils y descendirent.
Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
19 La femme prit la couverture et l'étendit sur l'embouchure du puits, et y répandit du grain pilé; et rien ne fut connu.
Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
20 Les serviteurs d'Absalom vinrent trouver la femme à la maison; ils dirent: « Où sont Ahimaats et Jonathan? » La femme leur dit: « Ils sont passés de l'autre côté du ruisseau. » Après avoir cherché et n'avoir pu les trouver, ils retournèrent à Jérusalem.
Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
21 Après leur départ, ils remontèrent du puits et allèrent avertir le roi David; ils lui dirent: « Lève-toi et passe rapidement l'eau, car c'est ainsi qu'Achitophel a conseillé contre toi. »
Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
22 Alors David se leva, ainsi que tout le peuple qui était avec lui, et ils passèrent le Jourdain. A la lumière du matin, il ne manquait pas un seul d'entre eux qui n'avait pas passé le Jourdain.
Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
23 Lorsqu'Ahithophel vit que son conseil n'était pas suivi, il sella son âne, se leva, rentra dans sa ville, remit sa maison en ordre et se pendit; il mourut et fut enterré dans le tombeau de son père.
Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
24 Puis David arriva à Mahanaïm. Absalom passa le Jourdain, lui et tous les hommes d'Israël avec lui.
Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
25 Absalom mit Amasa à la tête de l'armée à la place de Joab. Or Amasa était le fils d'un homme du nom d'Ithra, l'Israélite, qui était entré en relation avec Abigaïl, fille de Nahash, sœur de Tseruja, mère de Joab.
Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
26 Israël et Absalom campèrent dans le pays de Galaad.
Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
27 Lorsque David fut arrivé à Mahanaïm, Schobi, fils de Nachasch, de Rabba, des enfants d`Ammon, Makir, fils d`Ammiel, de Lodebar, et Barzillaï, Galaadite, de Rogelim,
Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
28 apportèrent des lits, des bassins, des vases de terre, du froment, de l`orge, de la farine, des grains desséchés, des haricots, des lentilles, des grains rôtis,
suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
29 du miel, du beurre, des brebis et du fromage du troupeau, pour le repas de David et du peuple qui était avec lui; car ils disaient: « Le peuple a faim, il est fatigué et il a soif dans le désert. »
da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”

< 2 Samuel 17 >