< 2 Samuel 11 >

1 Au retour de l'année, au moment où les rois sortent, David envoya avec lui Joab et ses serviteurs, et tout Israël; ils détruisirent les fils d'Ammon et assiégèrent Rabba. Mais David resta à Jérusalem.
Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
2 Le soir, David se leva de son lit et se promena sur le toit de la maison du roi. Du toit, il vit une femme qui se baignait, et cette femme était très belle à voir.
Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
3 David envoya demander des nouvelles de cette femme. On lui dit: « N'est-ce pas Bethsabée, fille d'Eliam, la femme d'Urie le Héthien? »
Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
4 David envoya des messagers, qui la prirent; elle entra chez lui, et il coucha avec elle (car elle était purifiée de son impureté); puis elle retourna dans sa maison.
Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
5 La femme devint enceinte; elle envoya avertir David, et dit: « Je suis enceinte. »
Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
6 David envoya dire à Joab: « Envoie-moi Urie, le Hittite. » Joab envoya Urie à David.
Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
7 Lorsque Urie fut arrivé auprès de lui, David lui demanda comment allait Joab, comment se portait le peuple et comment la guerre avait prospéré.
Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
8 David dit à Urie: « Descends dans ta maison et lave-toi les pieds. » Urie sortit de la maison du roi, et un présent du roi fut envoyé après lui.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
9 Mais Urie se coucha à l'entrée de la maison du roi avec tous les serviteurs de son maître, et il ne descendit pas dans sa maison.
Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
10 Lorsqu'on eut dit à David: « Urie n'est pas descendu dans sa maison », David dit à Urie: « Ne reviens-tu pas d'un voyage? Pourquoi n'es-tu pas descendu dans ta maison? »
Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
11 Urie dit à David: « L'arche, Israël et Juda sont sous des tentes, et mon seigneur Joab et les serviteurs de mon seigneur campent en plein champ. Irai-je donc dans ma maison pour manger et boire, et pour coucher avec ma femme? Aussi longtemps que tu vivras et que ton âme vivra, je ne ferai pas cela! ».
Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
12 David dit à Urie: « Reste ici aujourd'hui encore, et demain je te laisserai partir. » Urie resta donc à Jérusalem ce jour-là et le lendemain.
Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
13 Lorsque David l'eut appelé, il mangea et but en sa présence, et il le fit boire. Le soir, il sortit pour se coucher sur son lit avec les serviteurs de son seigneur, mais il ne descendit pas dans sa maison.
Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
14 Le matin, David écrivit une lettre à Joab et l'envoya par la main d'Urie.
Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
15 Il écrivit dans la lettre: « Envoie Urie au premier rang du combat le plus acharné, et retire-toi de lui, afin qu'il soit frappé et qu'il meure. »
A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
16 Joab, qui surveillait la ville, plaça Urie à l'endroit où il savait qu'il y avait des hommes vaillants.
Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
17 Les hommes de la ville sortirent et se battirent avec Joab. Une partie du peuple tomba, même des serviteurs de David, et Urie, le Hittite, mourut aussi.
Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
18 Joab envoya raconter à David tout ce qui s'était passé pendant la guerre.
Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
19 Il donna cet ordre au messager: « Quand tu auras fini de raconter au roi tout ce qui s'est passé pendant la guerre,
Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
20 si la colère du roi se manifeste et qu'il te demande: « Pourquoi t'es-tu approché de la ville pour combattre? Ne savais-tu pas qu'on tirerait du haut de la muraille?
wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
21 Qui a frappé Abimélec, fils de Jerubbesheth? Une femme n'a-t-elle pas jeté sur lui, du haut de la muraille, une meule de moulin, de sorte qu'il est mort à Thèbes? Pourquoi t'es-tu approché de la muraille? Tu diras alors: « Ton serviteur Urie, le Héthien, est mort lui aussi ».
Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
22 Le messager partit, et vint montrer à David tout ce que Joab lui avait envoyé chercher.
Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
23 Le messager dit à David: « Les hommes ont eu raison de nous, ils sont sortis dans les champs, et nous les avons poursuivis jusqu'à l'entrée de la porte.
Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
24 Les tireurs ont tiré sur tes serviteurs du côté de la muraille; certains des serviteurs du roi sont morts, et ton serviteur Urie le Hittite est également mort. »
Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
25 David dit au messager: « Dis à Joab: « Que cela ne te déplaise, car l'épée dévore aussi bien les uns que les autres. Fortifie ton combat contre la ville, et renverse-la ». Encourage-le. »
Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
26 Lorsque la femme d'Urie apprit qu'Urie, son mari, était mort, elle porta le deuil de son mari.
Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
27 Lorsque le deuil fut terminé, David l'envoya chercher et la prit dans sa maison; elle devint sa femme et lui donna un fils. Mais ce que David avait fait déplut à Yahvé.
Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.

< 2 Samuel 11 >