< 2 Rois 8 >
1 Élisée avait parlé à la femme dont il avait rendu la vie au fils, en disant: « Lève-toi, va, toi et ta famille, et reste quelque temps où tu pourras, car Yahvé a annoncé une famine. Elle s'abattra sur le pays pendant sept ans. »
To, Elisha ya riga ya ce wa matan da ya tā da ɗanta daga matattu, “Ki kwashe iyalinki ku tafi duk inda za ku tafi na ɗan lokaci, domin Ubangiji ya sa a yi yunwa na shekara bakwai a ƙasar.”
2 La femme se leva, et fit ce que l'homme de Dieu lui avait dit. Elle partit avec sa famille, et elle vécut sept ans dans le pays des Philistins.
Sai macen ta yi kamar yadda mutumin Allah ya faɗa. Ita da iyalinta suka tafi ƙasar Filistiyawa suka zauna shekara bakwai.
3 Au bout de sept ans, la femme revint du pays des Philistins. Elle sortit pour demander au roi sa maison et son pays.
A ƙarshen shekara bakwai ɗin sai ta dawo daga ƙasar Filistiyawa, ta kuma tafi wajen sarki ta roƙa a mayar mata da gidanta da filinta.
4 Or, le roi parlait avec Guéhazi, le serviteur de l'homme de Dieu, en disant: « Je te prie de me raconter toutes les grandes choses qu'Élisée a faites. »
Sarki kuwa yana magana da Gehazi bawan mutumin Allah, ya ce masa, “Ba ni labarin dukan abubuwan banmamakin da Elisha ya yi.”
5 Comme il racontait au roi comment il avait rendu la vie à celui qui était mort, voici que la femme dont il avait rendu la vie au fils supplia le roi pour sa maison et pour son pays. Guéhazi dit: « Mon seigneur, ô roi, voici la femme et voici son fils qu'Élisée a rendu à la vie. »
A sa’ad da Gehazi yana cikin ba shi labarin yadda Elisha ya tā da matacce ke nan, sai ga macen da aka tā da ɗanta daga matattu ta shigo don tă roƙi sarki yă mayar mata da gidanta da filinta. Gehazi ya ce, “Ranka yă daɗe, ai, ga macen, ga kuma ɗan da Elisha ya tā da daga matattu.”
6 Le roi interrogea la femme, et elle lui répondit. Alors le roi lui nomma un officier, en disant: « Restaure tout ce qui lui appartenait, et tous les fruits des champs depuis le jour où elle a quitté le pays, jusqu'à maintenant. »
Sarki ya tambayi macen game da al’amarin, ita kuwa ta faɗa masa. Sa’an nan ya sa wani hafsa yă dubi damuwarta ya kuma ce masa, “Ka mayar mata kome da yake nata, haɗe da dukan kuɗin da aka samo daga filin, daga ranar da ta bar ƙasar har yă zuwa yanzu.”
7 Elisée arriva à Damas, et Benhadad, le roi de Syrie, était malade. On lui dit: « L'homme de Dieu est venu ici. »
Sai Elisha ya tafi Damaskus, Ben-Hadad mutumin Aram kuwa yana ciwo. Sa’ad da aka faɗa wa sarki, “Mutumin Allah ya hauro tun daga can zuwa nan,”
8 Le roi dit à Hazaël: « Prends un présent dans ta main, va à la rencontre de l'homme de Dieu, et interroge par lui Yahvé en disant: « Vais-je guérir de cette maladie? »"
sai ya ce wa Hazayel, “Ɗauki wannan tare da kai ka tafi ka taryi mutumin Allah. Ka nemi nufin Ubangiji ta wurinsa; ka tambaye shi, ‘Zan warke daga ciwon nan?’”
9 Hazaël alla au-devant de lui et prit avec lui un présent, de tout ce qu'il y avait de bon à Damas, quarante charges de chameaux, puis il vint se placer devant lui et dit: « Ton fils Benhadad, roi de Syrie, m'a envoyé vers toi, en disant: « Vais-je guérir de cette maladie? »
Sai Hazayel ya tafi taryen Elisha, ya ɗauka kyauta na kowane irin kaya masu kyau na Damaskus tare da shi a raƙuma arba’in. Ya shiga ya tsaya a gaban Elisha ya ce, “Ɗanka Ben-Hadad na Aram ya aike ni in tambaye ka, ‘Zan warke daga ciwon nan?’”
10 Élisée lui dit: « Va, dis-lui: « Tu vas guérir », mais l'Éternel m'a montré qu'il allait mourir. »
Elisha ya amsa ya ce, “Je ka ce masa, ‘Ba shakka za ka warke’; ammaUbangiji ya nuna mini cewa ba shakka zai mutu.”
11 Il fixa son regard sur lui, jusqu'à ce qu'il ait honte. Alors l'homme de Dieu pleura.
Sai ya zuba wa Hazayel ido har sai da Hazayel ya ji kunya. Sa’an nan mutumin Allah ya fara kuka.
12 Hazaël dit: « Pourquoi pleures-tu, mon seigneur? » Il répondit: « Parce que je sais le mal que tu feras aux enfants d'Israël. Vous mettrez le feu à leurs forteresses, vous tuerez leurs jeunes gens par l'épée, vous mettrez en pièces leurs petits enfants et vous déchirerez leurs femmes enceintes. »
Hazayel ya ce masa, “Me ya sa ranka yă daɗe yake kuka?” Elisha ya amsa, “Domin na san illar da za ka yi wa Isra’ilawa. Za ka ƙona biranensu masu katanga, ka karkashe majiya ƙarfinsu da takobi, ka fyaffyaɗe ƙananan yaransu da ƙasa, ka tsattsage matansu masu ciki.”
13 Hazaël dit: « Mais qu'est-ce que ton serviteur, qui n'est qu'un chien, pour qu'il puisse faire cette grande chose? » Elisée répondit: « Yahvé m'a montré que tu seras roi de Syrie. »
Hazayel ya ce, “Yaya bawanka, wanda yake kare kawai, zai iya aikata wannan irin abu?” Elisha ya ce, “Ubangiji ya nuna mini cewa za ka zama sarkin Aram.”
14 Puis il se sépara d'Élisée et vint vers son maître, qui lui dit: « Que t'a dit Élisée? » Il a répondu: « Il m'a dit que vous alliez sûrement guérir. »
Sai Hazayel ya rabu da Elisha ya koma wurin maigidansa. Da Ben-Hadad ya yi tambaya, “Me Elisha ya ce maka?” Sai Hazayel ya amsa, “Ya faɗa mini cewa tabbatacce za ka warke.”
15 Le lendemain, il prit un linge épais, le trempa dans l'eau et l'étendit sur le visage du roi, de sorte qu'il mourut. Hazaël régna à sa place.
Amma kashegari sai ya ɗauki tsumma mai kauri, ya jiƙa shi, ya rufe fuskar sarki da shi, har sai da sarki ya mutu. Sai Hazayel ya gāje shi a matsayin sarki.
16 La cinquième année de Joram, fils d'Achab, roi d'Israël, Josaphat étant alors roi de Juda, Joram, fils de Josaphat, roi de Juda, commença à régner.
A shekara ta biyar ta mulkin Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra’ila, sa’ad da Yehoshafat yake sarautar Yahuda, Yoram ɗan Yehoshafat, ya fara mulkinsa a matsayin sarkin Yahuda.
17 Il avait trente-deux ans lorsqu'il devint roi. Il régna huit ans à Jérusalem.
Yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki na tsawon shekara takwas a Urushalima.
18 Il marcha dans la voie des rois d'Israël, comme la maison d'Achab, car il avait épousé la fille d'Achab. Il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel.
Ya bi gurbin sarakunan Isra’ila, yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya yi mugunta a gaban Ubangiji.
19 Cependant, l'Éternel ne voulut pas détruire Juda, à cause de David, son serviteur, car il lui avait promis de lui donner une lampe pour ses enfants, pour toujours.
Duk da haka, saboda bawansa Dawuda, Ubangiji bai ragargaza Yahuda ba. Ya riga ya yi alkawari zai bar wa Dawuda magāji har abada.
20 De son temps, Édom se révolta de dessous la main de Juda, et se fit un roi.
A kwanakin Yoram, Edom ta yi wa Yahuda tawaye, ta naɗa wa kanta sarki.
21 Et Joram passa à Zaïr, et tous ses chars avec lui; et il se leva de nuit et frappa les Édomites qui l'entouraient avec les chefs des chars; et le peuple s'enfuit dans ses tentes.
Saboda haka Yehoram ya tafi Zayir da dukan kekunan yaƙinsa. Sojojin Edom suka kewaye shi a can, amma da dare sai Yoram ya ɓarke ya gudu, sojojinsa kuma suka watse zuwa gidajensu.
22 Ainsi Édom se révolta de dessous la main de Juda jusqu'à ce jour. En même temps, Libna se révolta.
Har yă zuwa yau, Edom tana yi wa Yahuda tawaye. A lokaci ɗaya ne Libna ma ta yi tawaye.
23 Le reste des actes de Joram, et tout ce qu'il a fait, n'est-ce pas écrit dans le livre des Chroniques des rois de Juda?
Game da waɗansu abubuwan da suka faru a zamanin Yoram, ba suna a rubuce a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?
24 Joram se coucha avec ses pères et fut enterré avec ses pères dans la ville de David; et Achazia, son fils, régna à sa place.
Yoram ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda. Sai Ahaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
25 La douzième année de Joram, fils d'Achab, roi d'Israël, Achazia, fils de Joram, roi de Juda, commença à régner.
A shekara ta goma sha biyu ta Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra’ila, Ahaziya ɗan Yehoram, sarkin Yahuda ya fara mulki.
26 Achazia avait vingt-deux ans lorsqu'il devint roi, et il régna un an à Jérusalem. Le nom de sa mère était Athalie, fille d'Omri, roi d'Israël.
Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ɗaya. Sunan mahaifiyarsa Ataliya, jikanyar Omri, sarkin Isra’ila.
27 Il marcha dans la voie de la maison d'Achab et fit ce qui est mal aux yeux de Yahvé, comme la maison d'Achab, car il était le gendre de la maison d'Achab.
Ya bi gurbin gidan Ahab, ya yi mugunta a gaban Ubangiji yadda gida Ahab ta yi, gama yana da dangantaka ta aure da gidan Ahab.
28 Il alla avec Joram, fils d'Achab, à la guerre contre Hazaël, roi de Syrie, à Ramoth Galaad, et les Syriens blessèrent Joram.
Ahaziya ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab don su yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
29 Le roi Joram revint se faire guérir à Jizreel des blessures que les Syriens lui avaient faites à Rama, lorsqu'il combattait contre Hazaël, roi de Syrie. Achazia, fils de Joram, roi de Juda, descendit voir Joram, fils d'Achab, à Jizreel, car il était malade.
saboda haka Sarki Yoram ya koma zuwa Yezireyel don yă yi jinyar raunin da Arameyawa suka ji masa a Rama a yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sai Ahaziya ɗan Yehoram, sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel yă dubi Yoram ɗan Ahab domin an yi masa rauni.