< 2 Rois 4 >

1 Or, une femme d'entre les femmes des fils des prophètes cria à Élisée, en disant: « Ton serviteur, mon mari, est mort. Tu sais que ton serviteur craignait Yahvé. Maintenant le créancier est venu prendre pour lui mes deux enfants pour en faire des esclaves. »
Matar wani daga ƙungiyar annabawa ta yi wa Elisha kuka ta ce, “Mijina, bawanka, ya mutu, ka kuma san yadda ya girmama Ubangiji. Amma ga shi yanzu mai binsa bashi ya zo yă kwashe’ya’yana maza biyu su zama bayinsa.”
2 Élisée lui dit: « Que dois-je faire pour toi? Dis-moi, qu'est-ce que tu as dans la maison? » Elle a dit: « Votre serviteur n'a rien dans la maison, sauf un pot d'huile. »
Elisha ya amsa mata ya ce, “Me kike so in yi miki? Ki faɗa mini, me kike da shi a gidanki?” Sai ta ce, “Baiwarka ba ta da kome a can, sai ɗan tulun man zaitun.”
3 Puis il dit: « Allez emprunter des récipients vides à tous vos voisins. N'empruntez pas seulement quelques récipients.
Elisha ya ce, “Ki je wurin dukan maƙwabtanki, ki nemi tulunan da babu kome a ciki. Kada ki nemo kaɗan kawai.
4 Va, ferme la porte sur toi et sur tes fils, et verse de l'huile dans tous ces récipients, et mets de côté ceux qui sont pleins. »
Sa’an nan ki shiga ciki, ki kulle ƙofar da ke da’ya’yanki kuke ciki. Ku ɗuɗɗura man a dukan tulunan, sa’ad da kowanne ya cika, sai ki ajiye a gefe.”
5 Et elle s'éloigna de lui, et ferma la porte sur elle et sur ses fils. Ils lui apportèrent les récipients, et elle y versa de l'huile.
Ta tashi ta shiga tare da’ya’yanta maza, suka kulle ƙofa.’Ya’yanta suka kawo mata tuluna, ita kuma tana ɗurawa.
6 Lorsque les récipients furent pleins, elle dit à son fils: « Apporte-moi un autre récipient. » Il lui a dit: « Il n'y a pas d'autre récipient. » Puis l'huile a cessé de couler.
Da dukan tulunan suka cika, sai ta ce wa ɗanta, “Kawo mini wani tulu.” Amma ya amsa ya ce, “Ai, ba saura.” Sa’an nan man ya daina zuba.
7 Alors elle vint en parler à l'homme de Dieu. Il dit: « Va, vends l'huile, et paie ta dette; toi et tes fils, vous vivrez du reste. »
Sai ta tafi ta faɗa wa mutumin Allah. Shi kuwa ya ce mata, “Tafi, ki sayar da man, ki biya bashinki. Ki biya bukatanki da na’ya’yanki da sauran da ya rage.”
8 Un jour, Élisée se rendit à Shunem, où se trouvait une femme de bonne réputation, et elle le persuada de manger du pain. Elle le persuada de manger du pain. Et chaque fois qu'il passait par là, il s'y rendait pour manger du pain.
Wata rana Elisha ya tafi Shunem. Akwai wata mai arziki a can wadda ta gayyace shi cin abinci. Sai ya zama duk lokacin da yake wucewa, yakan tsaya a can don cin abinci.
9 Elle dit à son mari: « Voici, je vois que c'est un saint homme de Dieu qui passe sans cesse devant nous.
Ta ce wa mijinta, “Na san cewa wannan mutum da kullum yake zuwa nan mai tsarki ne na Allah.
10 Je t'en prie, faisons une petite chambre sur le toit. Mettons-lui un lit, une table, une chaise et un chandelier. Quand il viendra chez nous, il pourra y rester. »
Bari mu yi ɗan ɗaki a rufin gida mu kuma sa masa gado da tebur da kujera da kuma fitila. Saboda a duk lokacin da ya zo wurinmu, sai yă sauka a can.”
11 Un jour qu'il était arrivé là, il entra dans la chambre et s'y coucha.
Wata rana da Elisha ya zo, sai ya haura ɗakinsa ya kwanta.
12 Il dit à Guéhazi, son serviteur: « Appelle cette Sunamite. » Lorsqu'il l'eut appelée, elle se tint devant lui.
Ya ce wa bawansa Gehazi, “Kira mutuniyar Shunam nan.” Sai ya kira ta, ta zo ta tsaya a gabansa.
13 Il lui dit: « Dis-lui maintenant: « Voici, tu as pris soin de nous avec tous ces soins. Que fera-t-on pour toi? Veux-tu que l'on parle de toi au roi ou au chef de l'armée? ». Elle a répondu: « J'habite parmi les miens. »
Elisha ya ce masa, “Ka ce mata, ‘Kin yi duk wannan ɗawainiya saboda mu. Yanzu, me kike so a yi miki? Kina so mu yi magana a madadinki wa sarki ko babban hafsan mayaƙa?’” Sai ta ce, “A’a, ina da dukan abin da nake bukata a cikin jama’ata.”
14 Il dit: « Que faut-il donc faire pour elle? » Guéhazi répondit: « Très certainement, elle n'a pas de fils, et son mari est âgé. »
Sai Elisha ya tambayi Gehazi ya ce, “Me za mu yi mata?” Sai ya amsa ya ce, “Ba ta da ɗa, ga shi kuma mijinta ya tsufa.”
15 Il dit: « Appelle-la. » Quand il l'eut appelée, elle se tint à la porte.
Sai Elisha ya ce, “Ka kira ta.” Sai ya kira ta, ta zo ta tsaya a bakin ƙofa.
16 Il dit: « L'année prochaine, à la même époque, tu embrasseras un fils. » Elle a dit: « Non, mon seigneur, homme de Dieu, ne mens pas à ta servante. »
Elisha ya ce mata, “War haka baɗi, za ki riƙe ɗa na kanki.” Sai ta ce masa, “A’a, ranka yă daɗe, mutumin Allah, kada ka ruɗi baiwarka!”
17 La femme conçut et enfanta un fils à l'époque où le temps était venu, comme Élisée le lui avait dit.
Amma matan ta yi ciki, a shekara ta biye kuwa a daidai lokacin, sai ta haifi ɗa kamar yadda Elisha ya faɗa mata.
18 Lorsque l'enfant eut grandi, il sortit un jour vers son père, vers les moissonneurs.
Yaron ya yi girma, wata rana sai ya tafi wurin mahaifinsa, wanda yake tare da masu girbi.
19 Il dit à son père: « Ma tête! Ma tête! » Il dit à son serviteur: « Porte-le à sa mère. »
Ba zato sai ya ce wa mahaifinsa, “Wayyo! Kaina yana mini ciwo! Kaina yana mini ciwo!” Sai mahaifinsa ya ce wa bawansa, “Kai shi wurin mahaifiyarsa.”
20 Lorsqu'il l'eut pris et amené à sa mère, il resta assis sur ses genoux jusqu'à midi, puis il mourut.
Bayan bawan ya ɗaga shi ya kai wurin mahaifiyarsa, sai yaron ya zauna a cinyarta har tsakar rana, sa’an nan ya mutu.
21 Elle monta et le déposa sur le lit de l'homme de Dieu, ferma la porte sur lui, et sortit.
Sai ta haura ta shimfiɗa shi a gadon mutumin Allah, ta rufe ƙofar, ta fita.
22 Elle appela son mari et lui dit: « Envoie-moi, je te prie, un des serviteurs et un des ânes, afin que je puisse courir chez l'homme de Dieu et revenir. »
Ta kira mijinta ta ce, “Ina roƙonka ka aika mini da ɗaya daga cikin bayi da kuma jaka, don in yi sauri in je wurin mutumin Allah in dawo.”
23 Il répondit: « Pourquoi voudrais-tu aller le voir aujourd'hui? Ce n'est ni une nouvelle lune ni un sabbat. » Elle a dit: « C'est bon. »
Sai ya ce, “Me zai kai ki wurinsa, ai, yau ba Sabon Wata ba ne ko ranar Asabbaci?” Sai ta ce, “Ba kome.”
24 Puis elle sella un âne et dit à son serviteur: « Conduis, et avance! Ne ralentis pas pour moi, à moins que je ne te le demande. »
Sai ta sa wa jakar sirdi ta ce wa bawanta, “Yi ta kora mini jakar, kada ka sassauta, sai na faɗa maka.”
25 Elle s'en alla, et vint vers l'homme de Dieu sur la montagne du Carmel. Lorsque l'homme de Dieu la vit de loin, il dit à Guéhazi, son serviteur: « Voici la Sunamite.
Ta haka ta kama hanya ta tafi wurin mutumin Allah a Dutsen Karmel. Da ya hange ta daga nesa, sai mutumin Allah ya ce wa bawansa Gehazi, “Duba! Ga mutuniyar Shunam nan can!
26 Cours à sa rencontre et demande-lui: « Est-ce que tu te portes bien? Ton mari se porte-t-il bien? Ton enfant se porte-t-il bien? Elle a répondu: « C'est bien. »
Ka yi gudu ka tarye ta ka tambaye ta, ‘Lafiyarki? Mijinki yana nan lafiya? Yaronki yana nan lafiya?’” Ta amsa ta ce, “Kome lafiya yake.”
27 Lorsqu'elle arriva auprès de l'homme de Dieu sur la colline, elle se saisit de ses pieds. Guéhazi s'approcha pour la repousser; mais l'homme de Dieu dit: « Laisse-la tranquille, car son âme est troublée au-dedans d'elle; et Yahvé me l'a caché et ne me l'a pas dit. »
Da ta isa wurin mutumin Allah a dutsen, sai ta kama ƙafafunsa. Sai Gehazi ya zo don yă ture ta, amma mutumin Allah ya ce, “Ka bar ta! Tana cikin baƙin ciki ƙwarai, amma Ubangiji ya ɓoye mini, bai kuma faɗa mini me ya sa ba.”
28 Alors elle dit: « Est-ce que je t'ai demandé un fils, mon seigneur? N'ai-je pas dit: « Ne me trompe pas »? »
Sai ta tambaya shi ta ce, “Na roƙe ka ɗa ne, ranka yă daɗe? Ba na ce maka, ‘Kada ka sa in fara bege ba’?”
29 Puis il dit à Guéhazi: « Mets ton manteau dans ta ceinture, prends mon bâton dans ta main, et va-t'en. Si tu rencontres quelqu'un, ne le salue pas, et si quelqu'un te salue, ne lui réponds pas. Puis pose mon bâton sur le visage de l'enfant. »
Elisha ya ce wa Gehazi, “Ka yi ɗamara, ka ɗauki sandana ka ruga a guje. Idan ka sadu da wani, kada ka gaishe shi, idan kuma wani ya gaishe ka, kada ka amsa. Ka shimfiɗa sandana a fuskar yaron.”
30 La mère de l'enfant dit: « Aussi vrai que Yahvé est vivant et que ton âme est vivante, je ne te quitterai pas. » Il se leva donc et la suivit.
Amma mahaifiyar yaron ta ce, “Muddin Ubangiji yana raye, kai kuma kana a raye, ba zan bar ka ba.” Saboda haka ya tashi ya bi ta.
31 Guéhazi les précéda et posa le bâton sur le visage de l'enfant; mais il n'y avait ni voix ni ouïe. Il retourna donc à sa rencontre et lui dit: « L'enfant ne s'est pas réveillé. »
Gehazi ya yi gaba, ya shimfiɗa sandan a fuskar yaron, amma babu motsi, babu alamar rai. Saboda haka Gehazi ya koma ya taryi Elisha, ya faɗa masa, “Yaron bai tashi ba.”
32 Lorsqu'Élisée entra dans la maison, voici, l'enfant était mort et couché sur son lit.
Da Elisha ya isa gidan, sai ga gawar yaron kwance a kan gadonsa.
33 Il entra donc, ferma la porte sur eux deux, et pria l'Éternel.
Sai ya shiga, ya rufe ƙofa, daga shi sai yaron, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
34 Il monta et se coucha sur l'enfant, mit sa bouche sur sa bouche, ses yeux sur ses yeux, et ses mains sur ses mains. Il s'étendit sur lui, et la chair de l'enfant se réchauffa.
Sa’an nan ya hau gadon yă kwanta a bisa yaron, ya miƙe a kansa, baki da baki, ido da ido, hannu da hannu. Yayinda ya miƙe kansa a kan yaron, sai jikin yaron ya ɗau ɗumi.
35 Puis il s'en retourna et fit une fois le tour de la maison, puis il monta et s'étendit sur lui. L'enfant éternua sept fois, et l'enfant ouvrit les yeux.
Elisha ya tashi, ya yi ta kai komo a cikin ɗakin. Sa’an nan ya sāke koma kan gadon yă miƙe a kan yaron, sai yaron ya yi atishawa sau bakwai, ya kuma buɗe idanunsa.
36 Il appela Guéhazi, et dit: « Appelle cette Shunamite! » Il l'appela donc. Quand elle fut entrée chez lui, il dit: « Prends ton fils. »
Elisha ya kira Gehazi ya ce, “Kirawo mutuniyar Shunam.” Ya kuwa kira ta. Sa’ad da ta zo, sai Elisha ya ce mata, “Ɗauki ɗanki.”
37 Alors elle entra, se jeta à ses pieds et se prosterna à terre; puis elle prit son fils et sortit.
Sai ta shiga, ta fāɗi a ƙafafunsa ta rusuna har ƙasa. Sa’an nan ta ɗauki ɗanta ta fita.
38 Élisée revint à Gilgal. Il y avait une famine dans le pays; les fils des prophètes étaient assis devant lui, et il dit à son serviteur: « Va chercher la grande marmite, et fais bouillir du ragoût pour les fils des prophètes. »
Sai Elisha ya koma Gilgal, a can kuwa ana yunwa a yankin. Yayinda ƙungiyar annabawa suke tattaunawa da shi, sai ya ce wa Gehazi bawansa, “Ka sa babban tukunya a wuta, ka yi wa mutanen nan fate.”
39 L'un d'eux sortit dans les champs pour cueillir des herbes, et il trouva une vigne sauvage; il en cueillit un genou plein de courges sauvages, et il vint les couper dans la marmite de ragoût, car ils ne les reconnaissaient pas.
Ɗaya daga cikin mutanen ya shiga gona don neman ganyaye, ya kuwa sami kabewar jeji. Ya tsinko’ya’yanta cike da shafin rigarsa. Da ya dawo, sai ya yayyanka su ya zuba a cikin tukunyar faten, ko da yake ba wanda ya san ko mene ne.
40 Ils versèrent donc à manger pour les hommes. Comme ils mangeaient un peu du ragoût, ils s'écrièrent: « Homme de Dieu, il y a de la mort dans le pot! ». Et ils ne purent en manger.
Sai aka zuba wa mutanen faten, amma da suka fara ci, sai suka yi ihu suna cewa, “Ya mutumin Allah, akwai dafi a cikin tukunyan nan!” Suka kuwa kāsa ci.
41 Mais il dit: « Apporte donc de la farine. » Il la jeta dans la marmite; et il dit: « Sers-la au peuple, afin qu'il mange. » Et il n'y avait rien de nuisible dans la marmite.
Elisha ya ce, “Samo mini ɗan gari.” Aka kawo masa ya kuma sa a cikin tukunyan ya ce, “Raba wa mutanen su ci.” Ya kasance kuwa babu wani abin damuwa a tukunyar.
42 Un homme de Baal Shalishah vint et apporta à l'homme de Dieu du pain des prémices: vingt pains d'orge et des épis frais dans son sac. Élisée dit: « Donnez au peuple, pour qu'il mange. »
Sai ga wani mutum ya zo daga Ba’al-Shalisha, ya kawo wa Elisha dunƙulen burodi guda ashirin na sha’ir da aka gasa daga nunan fari na hatsi, tare da kawunan sababbin hatsi. Sai Elisha ya ce, “Ka ba mutanen su ci.”
43 Son serviteur dit: « Quoi, je dois mettre cela devant cent hommes? » Mais il dit: « Donne-le au peuple, qu'il mange, car Yahvé a dit: « Ils mangeront et il en restera ». »
Sai bawansa ya ce, “Yaya zan raba wa mutane ɗari wannan?” Amma Elisha ya amsa ya ce, “Ka raba wa mutane su ci, gama haka Ubangiji ya ce, ‘Za su ci har su bar saura.’”
44 Et il les mit devant eux, et ils mangèrent, et il en resta, selon la parole de Yahvé.
Sa’an nan ya ajiye a gabansu, suka kuwa ci har suka bar saura, bisa ga maganar Ubangiji.

< 2 Rois 4 >