< 2 Rois 2 >

1 Comme Yahvé était sur le point d'enlever Élie au ciel par un tourbillon, Élie partit de Gilgal avec Élisée.
Da lokaci ya yi da Ubangiji zai ɗauki Iliya zuwa sama cikin guguwa, Iliya da Elisha kuwa suna kan hanyarsu daga Gilgal.
2 Élie dit à Élisée: « Attends ici, car Yahvé m'a envoyé jusqu'à Béthel. » Élisée dit: « Aussi vrai que Yahvé est vivant et que ton âme est vivante, je ne te quitterai pas. » Ils descendirent donc à Béthel.
Sai Iliya ya ce wa Elisha, “Ka dakata a nan; Ubangiji ya aike ni Betel.” Amma Elisha ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka gangara zuwa Betel.
3 Les fils des prophètes qui étaient à Béthel sortirent vers Élisée et lui dirent: « Sais-tu que Yahvé va enlever aujourd'hui ton maître de dessus toi? » Il a dit: « Oui, je le sais. Tiens-toi tranquille. »
Sai ƙungiyar annabawa a Betel suka fito zuwa wajen Elisha suka ce masa, “Ka san cewa Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga wurinka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma kada ku yi magana game da wannan.”
4 Élie lui dit: « Élisée, attends ici, car l'Éternel m'a envoyé à Jéricho. » Il dit: « Aussi vrai que Yahvé est vivant et que ton âme est vivante, je ne te quitterai pas. » Ils arrivèrent donc à Jéricho.
Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan Elisha; Ubangiji ya aike ni Yeriko.” Sai ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai ma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka sai suka tafi Yeriko.
5 Les fils des prophètes qui étaient à Jéricho s'approchèrent d'Élisée et lui dirent: « Sais-tu que Yahvé va enlever aujourd'hui ton maître de dessus toi? » Il a répondu: « Oui, je le sais. Tiens-toi tranquille. »
Ƙungiyar annabawa a Yeriko suka haura zuwa wajen Elisha suka ce, “Ko ka san Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga gare ka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma ku bar zancen nan tukuna.”
6 Élie lui dit: « Attends ici, car l'Éternel m'a envoyé au Jourdain. » Il dit: « Aussi vrai que Yahvé vit et que ton âme vit, je ne te quitterai pas. » Et ils partirent tous deux.
Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan, Ubangiji ya aike ni Urdun.” Sai Elisha ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka ci gaba da tafiya tare.
7 Cinquante hommes d'entre les fils des prophètes allèrent se placer à distance en face d'eux, et ils se tinrent tous deux au bord du Jourdain.
Mutum hamsin na ƙungiyar annabawa suka je suka tsaya da nisa, suna fuskantar inda Iliya da Elisha suka tsaya a Urdun.
8 Élie prit son manteau, l'enroula, et frappa les eaux; elles se divisèrent ici et là, et ils passèrent tous deux à sec.
Sai Iliya ya tuɓe rigarsa, ya nannaɗe ya bugi ruwan Urdun da shi. Sai ruwan ya dāre gida biyu, suka haye a busasshiyar ƙasa.
9 Lorsqu'ils eurent traversé, Élie dit à Élisée: « Demande ce que je peux faire pour toi, avant que je sois enlevé d'avec toi. » Elisha a dit, « S'il te plaît, qu'une double portion de ton esprit soit sur moi. »
Da suka haye, sai Iliya ya ce wa Elisha, “Faɗi mini, abin da kake so in yi maka kafin a ɗauke ni daga gare ka!” Elisha ya amsa ya ce, “Bari in gāji ninki biyu na ruhunka.”
10 Il dit: « Tu as demandé une chose difficile. Si tu me vois quand on m'enlèvera de toi, il en sera ainsi pour toi; sinon, il n'en sera pas ainsi. »
Iliya ya ce, “Ka nemi abu mai wuya, amma in ka ga lokacin da aka ɗauke ni daga gare ka, zai zama naka, in ba haka ba, ba za ka samu ba ke nan.”
11 Comme ils continuaient à parler, voici qu'un char de feu et des chevaux de feu les séparèrent; et Élie monta au ciel dans un tourbillon.
Yayinda suke tafiya suna magana, sai kwatsam, keken yaƙin wuta da dawakan wuta suka ratse tsakaninsu, sai Iliya ya tafi sama a cikin guguwa.
12 Élisée le vit, et il s'écria: « Mon père, mon père, les chars d'Israël et ses cavaliers! » Il ne le vit plus. Puis il saisit ses propres vêtements et les déchira en deux morceaux.
Da Elisha ya ga haka sai ya yi ihu yana cewa, “Babana! Babana! Kekunan yaƙin da mahayan dawakan Isra’ila!” Elisha kuwa bai sāke ganinsa ba. Sai ya kama tufafinsa ya yayyage.
13 Il prit aussi le manteau d'Élie qui était tombé de lui, et s'en retourna se placer sur la rive du Jourdain.
Sai ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya koma ya tsaya a gaɓar Kogin Urdun.
14 Il prit le manteau d'Élie qui était tombé de lui, frappa les eaux, et dit: « Où est Yahvé, le Dieu d'Élie? » Quand il eut aussi frappé les eaux, elles se séparèrent, et Élisée passa outre.
Sa’an nan Elisha ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya bugi ruwan da shi. Ya ce, “Yanzu ina Ubangiji Allah na Iliya?” Da ya bugi ruwan sai ruwan ya dāre gida biyu, sai ya haye.
15 Lorsque les fils des prophètes qui étaient à Jéricho, en face de lui, le virent, ils dirent: « L'esprit d'Élie repose sur Élisée. » Ils vinrent à sa rencontre et se prosternèrent à terre devant lui.
Ƙungiyar annabawa daga Yeriko, waɗanda suke kallo, suka ce, “Ruhun Iliya yana a kan Elisha.” Sai suka je su tarye shi, suka rusuna har ƙasa a gabansa.
16 Ils lui dirent: « Vois maintenant, il y a avec tes serviteurs cinquante hommes forts. Laisse-les, je te prie, aller chercher ton maître. Peut-être l'Esprit de Yahvé l'a-t-il enlevé et déposé sur quelque montagne ou dans quelque vallée. » Il a dit: « Ne les envoyez pas. »
Suka ce, “Duba, mu bayinka muna da masu ji da ƙarfi hamsin. Bari su je su nemi maigidanka. Wataƙila, Ruhun Ubangiji ya ɗauke shi ya ajiye bisa wani dutse, ko wani kwari.” Elisha ya ce, “A’a, kada ku aike su.”
17 Comme ils le pressaient jusqu'à la honte, il dit: « Envoyez-les. » Ils envoyèrent donc cinquante hommes; ils cherchèrent pendant trois jours, mais ne le trouvèrent pas.
Amma suka matsa masa har ya ji ba ya iya hana su. Saboda haka ya ce, “Ku aike su.” Sai suka aiki mutane hamsin, suka yi ta nema har kwana uku amma ba su same Iliya ba.
18 Ils revinrent vers lui pendant qu'il restait à Jéricho, et il leur dit: « Ne vous ai-je pas dit: « N'y allez pas? »
Da suka dawo wurin Elisha, wanda yake a Yeriko, sai ya ce musu, “Ban ce muku kada ku tafi ba?”
19 Les hommes de la ville dirent à Élisée: « Voici, je vous en prie, la situation de cette ville est agréable, comme le voit mon seigneur; mais l'eau est mauvaise, et le pays est stérile. »
Mutane garin suka ce wa Elisha, “Ranka yă daɗe, duba, garin yana da kyan gani, amma ruwan ba shi da kyau, ƙasar kuma ba ta ba da amfani.”
20 Il dit: « Apportez-moi une jarre neuve, et mettez-y du sel. » On la lui apporta.
Sai ya ce, “Ku kawo mini sabuwar ƙwarya, ku kuma sa gishiri a ciki.” Sai suka kawo masa.
21 Il sortit vers la source des eaux, y jeta du sel, et dit: « L'Éternel dit: 'J'ai guéri ces eaux. Il n'y aura plus de mort ni de désert à partir de là ».
Sai ya tafi maɓulɓular ruwan yana watsa gishirin a ciki, yana cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Na warkar da ruwan nan. Ba zai ƙara jawo mutuwa, ko yă hana ƙasar ba da amfani ba.’”
22 Et les eaux furent guéries jusqu'à ce jour, selon la parole qu'Élisée avait prononcée.
Ruwan ya tsabtacce har yă zuwa yau, bisa ga faɗin Elisha.
23 De là, il monta à Béthel. Comme il montait par le chemin, des jeunes gens sortirent de la ville, se moquèrent de lui et lui dirent: « Monte, chauve! Monte, chauve! »
Daga nan sai Elisha ya tafi Betel. Yayinda yake tafiya a hanya, sai waɗansu matasa suka fito daga cikin gari, suka yi masa dariya suna cewa, “Ka haura, ya kai mai kai marar gashi! Ka haura, kai mai kai marar gashi!”
24 Il regarda derrière lui et les vit, et il les maudit au nom de Yahvé. Deux ourses sortirent alors des bois et déchiquetèrent quarante-deux de ces jeunes gens.
Sai ya juya ya dube su, ya la’anta su da sunan Ubangiji. Sai beyar guda biyu suka fito daga jeji suka hallaka matasa arba’in da biyu daga cikinsu.
25 De là, il se rendit au Carmel et de là, il retourna à Samarie.
Sai ya ci gaba zuwa Dutsen Karmel, daga can kuma ya koma Samariya.

< 2 Rois 2 >