< 2 Chroniques 35 >

1 Josias célébra la Pâque en l'honneur de Yahvé à Jérusalem. On immolait la Pâque le quatorzième jour du premier mois.
Yosiya ya yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji a Urushalima, aka kuma yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a ranar goma sha huɗu ga wata na farko.
2 Il établit les prêtres dans leurs fonctions et les encouragea dans le service de la maison de l'Éternel.
Ya zaɓi firistoci su yi aikinsu, sai ya ƙarfafa su su yi aikin da kyau a hidimar haikalin Ubangiji.
3 Il dit aux Lévites, qui enseignaient à tout Israël et qui étaient consacrés à Yahvé: « Mettez l'arche sainte dans la maison que Salomon, fils de David, roi d'Israël, a construite. Elle ne sera plus un fardeau pour vos épaules. Maintenant, servez Yahvé, votre Dieu, et son peuple, Israël.
Ya ce wa Lawiyawa waɗanda suke koyar da dukan Isra’ila da kuma waɗanda aka tsarkake wa Ubangiji. “Ku sa akwatin alkawari mai tsarki a cikin haikalin da Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila ya gina. Ba za a riƙa ɗaukansa a kafaɗa ba. Yanzu ku bauta wa Ubangiji Allahnku da kuma mutanensa Isra’ila.
4 Préparez-vous selon les maisons de vos pères, selon vos divisions, selon l'écriture de David, roi d'Israël, et selon l'écriture de Salomon, son fils.
Ku shirya kanku iyali-iyali a sassanku, bisa ga umarnan da Dawuda sarkin Isra’ila da kuma ɗansa Solomon suka rubuta.
5 Tenez-vous dans le lieu saint selon les divisions des maisons paternelles de vos frères, les enfants du peuple, et qu'il y ait pour chacun une portion de maison paternelle des Lévites.
“Ku tsaya a tsattsarkan wuri, bisa ga ƙungiyoyin gidajen kakannin’yan’uwanku, waɗanda su ba firistoci ba ne. Kowanne ya sami kashi daga cikin gidan Lawiyawa.
6 Immolez l'agneau de Pâques, sanctifiez-vous et préparez pour vos frères, afin de faire selon la parole de Yahvé par Moïse. »
Ku yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku kuma shirya raguna domin’yan’uwanku, kuna yin abin da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.”
7 Josias donna aux enfants du peuple, du troupeau, des agneaux et des chevreaux, tous pour les offrandes de la Pâque, à tous ceux qui étaient présents, au nombre de trente mille, et trois mille taureaux. Ces biens appartenaient au roi.
Yosiya ya tanada wa dukan mutanen da ba firistoci ba ne waɗanda suke a wurin, tumaki da awaki dubu talatin don a yanka saboda hadayun Bikin Ƙetarewa, ya kuma ba su shanu dubu uku. Dukan dabbobin kuwa daga garken sarki ne.
8 Ses princes firent une offrande volontaire au peuple, aux prêtres et aux lévites. Hilkija, Zacharie et Jehiel, chefs de la maison de Dieu, donnèrent aux sacrificateurs, pour les offrandes de la Pâque, deux mille six cents petits animaux et trois cents têtes de bétail.
Fadawansa su ma suka ba da taimako da yardar rai ga mutane da kuma firistoci da Lawiyawa. Hilkiya, Zakariya da Yehiyel masu aiki a haikalin Allah, suka ba firistoci hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyu da ɗari shida da kuma shanu ɗari uku.
9 Conania, Shemahia et Nethanel, ses frères, Haschabia, Jeiel et Jozabad, les chefs des Lévites, donnèrent aux Lévites, pour les offrandes de la Pâque, cinq mille petits animaux et cinq cents têtes de bétail.
Haka kuma Konaniya tare da Shemahiya da Netanel, ɗan’uwansa, da Hashabiya, Yehiyel da Yozabad, shugabannin Lawiyawa, suka tanadar da hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyar da kuma bijimai ɗari biyar domin Lawiyawa.
10 Le service fut donc préparé; les prêtres se tinrent à leur place, et les Lévites selon leurs divisions, conformément à l'ordre du roi.
Sa’ad da aka shirya kome don Bikin Ƙetarewar, sai Firistoci tare da Lawiyawa suka tsaya wurin tsayawarsu bisa ga umarnin sarki.
11 Ils égorgèrent les agneaux de la Pâque; les prêtres aspergèrent le sang qu'ils reçurent de leurs mains, et les Lévites les dépouillèrent.
Aka yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, firistoci kuma suka yayyafa jinin da aka ba su, yayinda Lawiyawa suna fiɗan dabbobi.
12 Ils enlevèrent les holocaustes pour les donner selon les divisions des maisons paternelles des enfants du peuple, afin de les offrir à l'Éternel, comme il est écrit dans le livre de Moïse. Ils firent de même avec le bétail.
Suka keɓe hadayun ƙonawa don su ba da su ga ƙungiyoyin iyalan mutane don su miƙa ga Ubangiji, yadda yake a rubuce a Littafin Musa. Suka yi haka da shanun.
13 Ils faisaient rôtir la Pâque au feu, selon l'ordonnance. Ils firent bouillir les offrandes saintes dans des marmites, des chaudrons et des casseroles, et les portèrent rapidement à tous les enfants du peuple.
Suka gasa dabbobin Bikin Ƙetarewa a bisa wuta yadda aka tsara, suka dafa hadayu masu tsarki a tukwane, da manyan tukwane, da kuma kwanoni, suka raba su nan da nan ga dukan mutane.
14 Ensuite, ils se préparèrent pour eux-mêmes et pour les prêtres, car les prêtres, fils d'Aaron, étaient occupés à offrir les holocaustes et la graisse jusqu'à la nuit. Les Lévites se préparèrent donc pour eux-mêmes et pour les prêtres, fils d'Aaron.
Bayan wannan, suka shirya wa kansu da kuma wa firistoci, saboda firistoci, zuriyar Haruna, suna miƙa hadayun ƙonawa da sashen kitse daga safe har dare. Saboda haka Lawiyawa suka shirya wa kansu da kuma wa firistocin daga zuriyar Haruna.
15 Les chantres, fils d'Asaph, étaient à leur place, selon l'ordre de David, Asaph, Héman et Jeduthun, voyant du roi; et les portiers étaient à chaque porte. Ils n'avaient pas besoin de quitter leur service, car leurs frères les Lévites les préparaient.
Mawaƙa zuriyar Asaf, suna a wuraren da Dawuda, Asaf, Heman da Yedutun mai duba na sarki suka tsara. Bai zama lalle matsaran ƙofofi a kowace ƙofa su bar wuraren aikinsu ba, domin’yan’uwansu Lawiyawa sun yi shiri dominsu.
16 Ainsi, tout le service de l'Éternel fut préparé le même jour, pour célébrer la Pâque et pour offrir des holocaustes sur l'autel de l'Éternel, selon l'ordre du roi Josias.
Ta haka fa aka yi dukan hidimar Ubangiji a wannan rana, domin su kiyaye Bikin Ƙetarewa, domin kuma su miƙa hadayu na ƙonawa a bisa bagaden Ubangiji, yadda sarki Yosiya ya umarta.
17 Les enfants d'Israël qui étaient présents célébrèrent la Pâque en ce temps-là, et la fête des pains sans levain pendant sept jours.
Isra’ilawan da suka kasance a can suka yi Bikin Ƙetarewa a wannan rana, suka kuma kiyaye Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai.
18 Il n'y a pas eu de Pâque comme celle-là en Israël depuis les jours du prophète Samuel, et aucun des rois d'Israël n'a célébré une Pâque comme celle que Josias a célébrée, avec les prêtres, les lévites, tout Juda et Israël présents, et les habitants de Jérusalem.
Ba a taɓa yin Bikin Ƙetarewa haka ba tun zamanin annabi Sama’ila; kuma babu sarkin Isra’ilan da ya taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa kamar yadda Yosiya ya yi, tare da firistoci, Lawiyawa da kuma dukan Yahuda da Isra’ila, waɗanda suke can tare da mutanen Urushalima.
19 Cette Pâque fut célébrée la dix-huitième année du règne de Josias.
An yi wannan Bikin Ƙetarewa a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya.
20 Après tout cela, comme Josias avait préparé le temple, Neco, roi d'Égypte, monta pour combattre Carchemish au bord de l'Euphrate, et Josias sortit à sa rencontre.
Bayan wannan duka, sa’ad da Yosiya ya shirya haikali, Neko sarkin Masar ya haura don yă yi yaƙi a Karkemish a Yuferites, sai Yosiya ya fita don yă fafata da shi a yaƙi.
21 Mais il lui envoya des ambassadeurs, en disant: « Qu'ai-je à faire avec toi, roi de Juda? Je ne viens pas aujourd'hui contre toi, mais contre la maison avec laquelle je suis en guerre. Dieu m'a ordonné de me hâter. Prends garde que ce soit Dieu qui soit avec moi, afin qu'il ne te détruise pas. »
Amma Neko ya aiki’yan saƙo ga Yosiya, yana cewa, “Me ya gama ni da kai, ya Sarkin Yahuda? Ban zo in yi yaƙi da kai ba. Na zo ne in yi yaƙi da gidan da yake gāba da ni! Ka ƙyale ni! Allah ne ya riga ya faɗa mini in hanzarta. Kada ka yi gāba da Allah, wanda yake tare da ni, don kada yă hallaka ka.”
22 Cependant Josias ne voulut pas détourner son visage de lui, mais il se déguisa pour pouvoir combattre avec lui, et il n'écouta pas les paroles de Neco venant de la bouche de Dieu, et il vint combattre dans la vallée de Megiddo.
Yosiya fa, bai juya daga gare shi ba, amma ya ɓad da kama don yă yi yaƙin. Bai saurari abin da Neko ya faɗa bisa ga umarnin Allah ba, amma ya tafi ya yaƙe shi a filin Megiddo.
23 Les archers tirèrent sur le roi Josias, et le roi dit à ses serviteurs: « Emmenez-moi, car je suis gravement blessé! ».
Maharba suka harbi Yosiya, sai ya ce wa hafsoshinsa, “Ku ɗauke ni ku fita da ni daga nan; gama an yi mini mummunan rauni.”
24 Ses serviteurs le firent descendre du char, le mirent dans le second char qu'il avait, et l'emmenèrent à Jérusalem. Il mourut, et fut enterré dans les tombeaux de ses pères. Tout Juda et Jérusalem portèrent le deuil de Josias.
Saboda haka suka ɗauke shi a keken yaƙin, suka fitar da shi, suka sa shi a wata keken yaƙin da yake da shi, suka kawo shi Urushalima, inda ya mutu. Aka binne shi a makabartar kakanninsa, sai dukan Yahuda da Urushalima suka yi makoki dominsa.
25 Jérémie fit des lamentations sur Josias, et tous les chanteurs et toutes les chanteuses ont parlé de Josias dans leurs lamentations jusqu'à ce jour, et ils en ont fait une ordonnance en Israël. Voici, elles sont écrites dans les lamentations.
Annabin Irmiya ya tsara waƙoƙin makoki domin Yosiya, wanda har wa yau mawaƙa maza da mata suke rera game da Yosiya. Suka sa waɗannan su zama al’ada a Isra’ila, suna kuma a rubuce cikin Littafin Makoki.
26 Maintenant, le reste des actes de Josias et ses bonnes actions, selon ce qui est écrit dans la loi de l'Éternel,
Sauran ayyukan mulkin Yosiya da kuma kyawawan abubuwan da ya yi, bisa ga abin da aka rubuta a Dokar Ubangiji,
27 et ses actes, les premiers et les derniers, voici, ils sont écrits dans le livre des rois d'Israël et de Juda.
dukan ayyukan, daga farko har zuwa ƙarshe, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda.

< 2 Chroniques 35 >