< 2 Chroniques 32 >
1 Après ces choses et cette fidélité, Sennachérib, roi d'Assyrie, arriva, entra en Juda, campa contre les villes fortifiées et eut l'intention de les gagner pour lui.
Bayan dukan abin da Hezekiya ya yi cikin aminci, sai Sennakerib sarkin Assuriya ya zo ya yaƙi Yahuda. Ya yi kwanto wa biranen katanga, yana zato zai ci su da yaƙi wa kansa.
2 Lorsqu'Ézéchias vit que Sennachérib était venu et qu'il projetait de combattre Jérusalem,
Sa’ad da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo yana kuma niyya yă yaƙi Urushalima,
3 il consulta ses princes et ses hommes forts pour arrêter les eaux des sources qui étaient à l'extérieur de la ville, et ils l'aidèrent.
sai ya yi shawara da fadawansa da hafsoshin mayaƙansa cewa su datse ruwa daga maɓulɓulan ruwan da yake waje da birnin, suka kuwa taimake shi.
4 Alors beaucoup de gens se rassemblèrent et ils arrêtèrent toutes les sources et le ruisseau qui coulait au milieu du pays, en disant: « Pourquoi les rois d'Assyrie viendraient-ils et trouveraient-ils de l'eau en abondance? »
Sai babban taro suka haɗu suka datse dukan maɓulɓulai da rafuffukan da suke gudu cikin ƙasar. Suka ce “Me zai sa sarakunan Assuriya su zo su sami ruwa barkatai?”
5 Il prit courage, rebâtit toute la muraille abattue, l'éleva jusqu'aux tours, avec l'autre muraille en dehors, et renforça Millo dans la ville de David; il fabriqua des armes et des boucliers en abondance.
Sai suka yi aiki tuƙuru suna gyaran dukan sassan katangar da suka fāɗi, suna kuma gina hasumiya a kai. Ya gina wata katanga a waje da wannan, ya kuma ƙara ƙarfin madogaran gini na Birnin Dawuda. Ya yi makamai masu yawa da kuma garkuwoyi.
6 Il plaça des chefs de guerre à la tête du peuple, les rassembla auprès de lui sur la grande place à la porte de la ville, et leur adressa des paroles d'encouragement en disant:
Ya naɗa manyan hafsoshi a kan mutane, ya tattara su a gabansa a fili a ƙofar birni, ya kuma ƙarfafa su da waɗannan kalmomi.
7 « Soyez forts et courageux. Ne craignez pas et ne soyez pas effrayés à cause du roi d'Assyrie et de toute la multitude qui est avec lui, car il y a plus grand que lui avec nous.
“Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Assuriya, da mayaƙan nan masu yawa da suke tare da shi, gama shi wanda yake tare da mu, ya fi wanda yake tare da su.
8 Il a avec lui un bras de chair, mais Yahvé notre Dieu est avec nous pour nous secourir et mener nos combats. » Le peuple se reposa sur les paroles d'Ézéchias, roi de Juda.
Mayaƙa na jiki ne kawai suke tare da shi, amma Ubangiji Allahnmu ne yake tare da mu, zai kuwa taimake mu yă kuma yi yaƙinmu.” Mutane kuwa suka amince da maganar Hezekiya, Sarkin Yahuda.
9 Après cela, Sennacherib, roi d'Assyrie, envoya ses serviteurs à Jérusalem (il était en train d'attaquer Lachish, et toutes ses forces étaient avec lui), à Ézéchias, roi de Juda, et à tous les Judéens qui étaient à Jérusalem, en disant:
Daga baya, sa’ad da Sennakerib sarkin Assuriya da dukan mayaƙansa suke kwanto wa Lakish, sai ya aiki hafsoshinsa da wannan saƙo wa Hezekiya sarkin Yahuda da kuma wa dukan mutanen Yahuda waɗanda suke can cewa,
10 Sennacherib, roi d'Assyrie, dit: « En qui vous confiez-vous, puisque vous restez assiégés à Jérusalem?
“Ga abin da Sennakerib sarkin Assuriya ya ce ga me kake dogara, har da ka dāge cikin Urushalima da aka yi mata kwanto?
11 Ézéchias ne vous persuade-t-il pas de vous livrer à la mort par la famine et par la soif, en disant: « Yahvé notre Dieu nous délivrera de la main du roi d'Assyrie? »
Ai, Hezekiya, ruɗinku yake yi, don yă sa ku mutu da yunwa da ƙishirwa sa’ad da yake ce muku, ‘Ubangiji Allahnmu zai cece mu daga hannun sarkin Assuriya.’
12 Le même Ézéchias n'a-t-il pas enlevé ses hauts lieux et ses autels, et n'a-t-il pas donné cet ordre à Juda et à Jérusalem: « Vous vous prosternerez devant un seul autel, et vous y brûlerez des parfums? »
Hezekiya kansa bai rushe waɗannan masujadan kan tudu da bagadai, yana ce wa Yahuda da Urushalima, ‘Dole ku yi sujada a gaban bagade guda ku kuma ƙone hadayu a kansa ba’?
13 Ne savez-vous pas ce que moi et mes pères avons fait à tous les peuples du pays? Les dieux des nations de ces pays étaient-ils en mesure de délivrer leur pays de ma main?
“Ba ku san abin da ni da kuma kakannina suka yi wa dukan mutanen sauran ƙasashe ba? Allolin ƙasashen nan sun taɓa iya ceton ƙasarsu daga hannuna ne?
14 Qui, parmi tous les dieux de ces nations que mes pères ont dévastées, pouvait délivrer son peuple de ma main, pour que ton Dieu puisse te délivrer de ma main?
Wanne a cikin dukan allolin waɗannan ƙasashe da kakannina suka hallaka ya taɓa iya ceton mutanensa daga gare ni? To, yaya Allahnku zai iya cetonku daga hannuna?
15 Maintenant, ne vous laissez pas tromper par Ezéchias et ne vous persuadez pas de cette manière. Ne le croyez pas, car aucun dieu d'aucune nation ni d'aucun royaume n'a pu délivrer son peuple de ma main et de la main de mes pères. A combien moins forte raison votre Dieu vous délivrera-t-il de ma main? »
Yanzu fa, kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku yă kuma ɓad da ku haka. Kada ku gaskata shi, gama babu allahn wata ƙasa ko masarautar da ya taɓa iya ceton mutanensa daga hannuna ko kuwa hannun kakannina. Balle har Allahnku yă cece ku daga hannuna!”
16 Ses serviteurs parlèrent encore contre l'Éternel Dieu et contre son serviteur Ézéchias.
Hafsoshin Sennakerib suka ci gaba da maganar banza wa Ubangiji Allah da kuma a kan bawansa Hezekiya.
17 Il écrivit aussi des lettres insultant Yahvé, le Dieu d'Israël, et parlant contre lui, disant: « Comme les dieux des nations du pays, qui n'ont pas délivré leur peuple de ma main, ainsi le Dieu d'Ézéchias ne délivrera pas son peuple de ma main. »
Sarki ya kuma rubuta wasiƙu yana zagin Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana faɗin wannan a kansa, “Kamar yadda sauran allolin mutanen sauran ƙasashe ba su iya kuɓutar da mutane daga hannuna ba, haka Allahn Hezekiya ba zai kuɓutar da mutanensa daga hannuna ba.”
18 Ils appelèrent d'une voix forte, dans la langue des Juifs, les habitants de Jérusalem qui étaient sur la muraille, pour les effrayer et les troubler, afin de prendre la ville.
Sa’an nan suka yi magana da ƙarfi cikin Yahudanci wa mutanen Urushalima waɗanda suke kan katanga, don su firgita su, su kuma sa su ji tsoro don su iya cin birnin.
19 Ils parlaient du Dieu de Jérusalem comme des dieux des peuples de la terre, qui sont l'œuvre de mains d'hommes.
Suka yi magana game da Allah na Urushalima yadda suka yi game da allolin sauran mutanen duniya, aikin hannuwan mutane.
20 Le roi Ézéchias et le prophète Ésaïe, fils d'Amoz, prièrent à cause de cela et crièrent au ciel.
Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz suka yi kuka cikin addu’a ga sama game da wannan.
21 Yahvé envoya un ange qui extermina tous les vaillants hommes, les chefs et les capitaines dans le camp du roi d'Assyrie. Celui-ci s'en retourna, honteux de son visage, dans son pays. Comme il était entré dans la maison de son dieu, ceux qui étaient sortis de son propre corps l'y tuèrent par l'épée.
Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.
22 Ainsi Yahvé sauva Ézéchias et les habitants de Jérusalem de la main de Sennacherib, roi d'Assyrie, et de la main de tous les autres, et il les guida de tous côtés.
Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mutanen Urushalima daga hannun Sennakerib sarkin Assuriya da kuma daga hannun dukan sauran. Ya magance su a kowane gefe.
23 Beaucoup apportèrent des présents à Yahvé à Jérusalem et des objets précieux à Ézéchias, roi de Juda, de sorte qu'il fut désormais exalté aux yeux de toutes les nations.
Yawanci mutane suka kawo hadayun ƙonawa zuwa Urushalima wa Ubangiji da kuma kyautai masu daraja wa Hezekiya sarkin Yahuda. Daga lokacin zuwa gaba dukan ƙasashe suka girmama shi.
24 En ces jours-là, Ézéchias était en phase terminale, et il pria Yahvé; celui-ci lui parla et lui donna un signe.
A kwanakin nan Hezekiya ya yi ciwo, ya yi kusan mutuwa. Sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wanda ya amsa masa ya kuma ba shi alama.
25 Mais Ézéchias ne rendit pas le bienfait qui lui avait été fait, parce que son cœur s'élevait. C'est pourquoi il y eut de la colère sur lui, sur Juda et sur Jérusalem.
Amma zuciyar Hezekiya ta yi girman kai, bai kuwa yi amfani da alherin da aka nuna masa ba, saboda haka fushin Ubangiji ya sauko a kansa da kuma a kan Yahuda da Urushalima.
26 Cependant, Ézéchias s'humilia à cause de l'orgueil de son cœur, lui et les habitants de Jérusalem, de sorte que la colère de Yahvé ne s'abattit pas sur eux du temps d'Ézéchias.
Sai Hezekiya ya tuba daga girma kan zuciyarsa, haka ma mutanen Urushalima; saboda haka fushin Ubangiji bai zo a kansu a kwanakin Hezekiya ba.
27 Ézéchias eut des richesses et des honneurs immenses. Il se pourvut de trésors pour l'argent, pour l'or, pour les pierres précieuses, pour les aromates, pour les boucliers, et pour toutes sortes de vases précieux;
Hezekiya mai arziki da girma ne ƙwarai, ya kuma yi baitulmali domin azurfa da zinariyarsa da kuma domin duwatsu masu daraja, kayan yaji, garkuwoyi da kuma domin dukan kayayyaki masu daraja nasa.
28 il se pourvut aussi de magasins pour la production du blé, du vin nouveau et de l'huile, et d'étables pour toutes sortes de bêtes, et de troupeaux en plis.
Ya kuma yi gine-gine domin ajiyar hatsi, sabon ruwa inabi da mai; ya kuma yi wuraren ajiyar kowane irin shanu dabam-dabam, da kuma turke domin tumaki.
29 Il se procura aussi des villes, et des biens en abondance pour le bétail et les troupeaux, car Dieu lui avait donné des biens en abondance.
Ya gina ƙauyuka ya kuma samo shanu da garkuna masu yawa, gama Allah ya ba shi arziki mai yawa sosai.
30 Ce même Ézéchias arrêta aussi la source supérieure des eaux du Gihon, et les fit descendre directement à l'ouest de la ville de David. Ézéchias prospéra dans toutes ses œuvres.
Hezekiya ne ya datse ruwan bisa na maɓulɓular Gihon, ya sa ruwan ya gangara zuwa gefe yamma na Birnin Dawuda. Ya yi nasara a kome da ya yi.
31 Cependant, à propos des ambassadeurs des princes de Babylone, qui l'envoyèrent s'enquérir du prodige qui se faisait dans le pays, Dieu le laissa pour l'éprouver, afin qu'il sache tout ce qui était dans son cœur.
Amma da masu mulkin Babilon suka aika da jakadu su tambaye shi game alamar da ta faru a ƙasar, Allah ya rabu da shi don yă gwada shi don yă kuma san kome da yake cikin zuciyarsa.
32 Le reste des actes d'Ézéchias et ses bonnes actions, voici, ils sont écrits dans la vision du prophète Ésaïe, fils d'Amoz, dans le livre des rois de Juda et d'Israël.
Sauran ayyukan mulkin Hezekiya da kuma kyawawa ayyukansa, suna a rubuce a cikin wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz, a cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
33 Ézéchias se coucha avec ses pères, et on l'enterra dans la montée des tombeaux des fils de David. Tout Juda et les habitants de Jérusalem l'honorèrent à sa mort. Manassé, son fils, régna à sa place.
Hezekiya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a kan tudu inda makabartan zuriyar Dawuda suke. Dukan Yahuda da kuma mutanen Urushalima suka girmama shi sa’ad da ya mutu. Sai Manasse ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.