< 2 Chroniques 29 >

1 Ézéchias devint roi à l'âge de vingt-cinq ans, et il régna vingt-neuf ans à Jérusalem. Sa mère s'appelait Abija, fille de Zacharie.
Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
2 Il fit ce qui est droit aux yeux de l'Éternel, selon tout ce qu'avait fait David, son père.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
3 La première année de son règne, au premier mois, il ouvrit les portes de la maison de Yahvé et les répara.
A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
4 Il fit venir les prêtres et les Lévites, les rassembla sur la grande place de l'orient,
Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
5 et leur dit: « Écoutez-moi, Lévites! Maintenant, sanctifiez-vous, sanctifiez la maison de Yahvé, le Dieu de vos pères, et emportez les souillures hors du lieu saint.
ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
6 Car nos pères ont été infidèles, ils ont fait ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, notre Dieu, ils l'ont abandonné, ils ont détourné leur visage de la demeure de l'Éternel et lui ont tourné le dos.
Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
7 Ils ont aussi fermé les portes du portique et éteint les lampes, et ils n'ont pas brûlé de parfums ni offert d'holocaustes dans le sanctuaire du Dieu d'Israël.
Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
8 C'est pourquoi la colère de l'Éternel s'est abattue sur Juda et Jérusalem, et il les a livrés au tumulte, à l'étonnement et au sifflement, comme vous le voyez de vos yeux.
Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
9 Car voici, nos pères sont tombés par l'épée, et nos fils, nos filles et nos femmes sont en captivité à cause de cela.
Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
10 Maintenant, j'ai à cœur de faire alliance avec l'Éternel, le Dieu d'Israël, afin que son ardente colère se détourne de nous.
Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
11 Mes fils, ne soyez pas négligents maintenant, car Yahvé vous a choisis pour vous tenir devant lui, pour le servir, et pour que vous soyez ses serviteurs et que vous brûliez des encens. »
’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
12 Alors les Lévites se levèrent: Mahath, fils d'Amasaï, et Joël, fils d'Azaria, des fils des Kehathites; des fils de Merari, Kish, fils d'Abdi, et Azaria, fils de Jehallelel; des Gershonites, Joach, fils de Zimma, et Eden, fils de Joach;
Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
13 et des fils d'Élizaphan, Shimri et Jeuel; et des fils d'Asaph, Zacharie et Mattania;
Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
14 et des fils d'Héman, Jehuel et Shimei; et des fils de Jeduthun, Shemaiah et Uzziel.
Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
15 Ils rassemblèrent leurs frères, se purifièrent et entrèrent, selon l'ordre du roi, d'après les paroles de l'Éternel, pour purifier la maison de l'Éternel.
Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
16 Les prêtres entrèrent dans l'intérieur de la maison de l'Éternel pour la purifier, et ils firent sortir dans le parvis de la maison de l'Éternel toutes les impuretés qu'ils avaient trouvées dans le temple de l'Éternel. Les Lévites le prirent de là pour le porter jusqu'au torrent de Cédron.
Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
17 Ils commencèrent à sanctifier le premier jour du premier mois, et le huitième jour du mois, ils arrivèrent au portique de l'Éternel. Ils sanctifièrent la maison de l'Éternel en huit jours, et ils achevèrent le seizième jour du premier mois.
Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
18 Puis ils se rendirent auprès du roi Ézéchias dans l'enceinte du palais et dirent: « Nous avons purifié toute la maison de Yahvé, y compris l'autel des holocaustes avec tous ses ustensiles, et la table des pains de proposition avec tous ses ustensiles.
Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
19 De plus, nous avons préparé et sanctifié tous les ustensiles que le roi Achaz a jetés pendant son règne, lorsqu'il était infidèle. Voici qu'ils sont devant l'autel de Yahvé ».
Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
20 Le roi Ézéchias se leva de bonne heure, rassembla les chefs de la ville et monta à la maison de l'Éternel.
Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
21 Ils apportèrent sept taureaux, sept béliers, sept agneaux et sept boucs, en sacrifice pour le péché, pour le royaume, pour le sanctuaire et pour Juda. Il ordonna aux prêtres, fils d'Aaron, de les offrir sur l'autel de Yahvé.
Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
22 Ils égorgèrent les taureaux; les prêtres reçurent le sang et l'arrosèrent sur l'autel. Ils égorgèrent les béliers et en répandirent le sang sur l'autel. Ils égorgèrent aussi les agneaux et en répandirent le sang sur l'autel.
Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
23 Ils firent approcher les boucs pour le sacrifice pour le péché devant le roi et l'assemblée, et ils posèrent leurs mains sur eux.
Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
24 Les prêtres les égorgèrent et firent un sacrifice pour le péché avec leur sang sur l'autel, afin de faire l'expiation pour tout Israël; car le roi avait ordonné que l'holocauste et le sacrifice pour le péché soient faits pour tout Israël.
Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
25 Il plaça les Lévites dans la maison de l'Éternel avec des cymbales, des instruments à cordes et des harpes, selon l'ordre de David, de Gad, le voyant du roi, et de Nathan, le prophète; car l'ordre venait de l'Éternel par ses prophètes.
Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
26 Les Lévites se tenaient avec les instruments de David, et les prêtres avec les trompettes.
Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
27 Ezéchias leur ordonna d'offrir l'holocauste sur l'autel. Lorsque l'holocauste commença, le chant de Yahvé commença également, ainsi que les trompettes et les instruments de David, roi d'Israël.
Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
28 Toute l'assemblée se prosternait, les chanteurs chantaient et les trompettes sonnaient. Tout cela se poursuivit jusqu'à ce que l'holocauste soit achevé.
Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
29 Quand ils eurent fini d'offrir, le roi et tous ceux qui étaient présents avec lui se prosternèrent et se prosternèrent.
Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
30 Le roi Ézéchias et les princes ordonnèrent aux Lévites de chanter des louanges à Yahvé selon les paroles de David et du voyant Asaph. Ils chantèrent des louanges avec allégresse, ils se prosternèrent et se prosternèrent.
Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
31 Ézéchias répondit: « Maintenant, vous vous êtes consacrés à Yahvé. Approchez-vous et apportez des sacrifices et des offrandes de remerciement dans la maison de Yahvé. » L'assemblée apporta des sacrifices et des offrandes de remerciement, et tous ceux qui avaient le cœur bien disposé apportèrent des holocaustes.
Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
32 Le nombre des holocaustes que l'assemblée apporta fut de soixante-dix taureaux, cent béliers et deux cents agneaux. Tout cela servit d'holocauste à l'Éternel.
Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
33 Les choses consacrées étaient six cents têtes de bétail et trois mille moutons.
Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
34 Mais les prêtres étaient trop peu nombreux, de sorte qu'ils ne pouvaient pas écorcher tous les holocaustes. C'est pourquoi leurs frères les Lévites les aidèrent jusqu'à ce que le travail soit terminé et jusqu'à ce que les prêtres se soient sanctifiés, car les Lévites avaient un cœur plus droit pour se sanctifier que les prêtres.
Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
35 Les holocaustes étaient en abondance, avec la graisse des sacrifices de prospérité et les libations pour chaque holocauste. Ainsi, le service de la maison de Yahvé fut mis en ordre.
Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
36 Ézéchias et tout le peuple se réjouirent de ce que Dieu avait préparé pour le peuple, car la chose s'était faite soudainement.
Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.

< 2 Chroniques 29 >