< 2 Chroniques 25 >
1 Amatsia avait vingt-cinq ans lorsqu'il devint roi, et il régna vingt-neuf ans à Jérusalem. Le nom de sa mère était Joaddan, de Jérusalem.
Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
2 Il fit ce qui est droit aux yeux de l'Éternel, mais pas avec un cœur parfait.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
3 Et lorsque la royauté fut établie en sa faveur, il tua ses serviteurs qui avaient tué le roi son père.
Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
4 Mais il ne fit pas mourir leurs enfants, et il agit selon ce qui est écrit dans la loi, dans le livre de Moïse, comme Yahvé l'a ordonné, en disant: « Les pères ne mourront pas pour les enfants, et les enfants ne mourront pas pour les pères; mais chacun mourra pour son propre péché. »
Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
5 Amatsia rassembla Juda et les classa selon les maisons de leurs pères, sous les chefs de milliers et les chefs de centaines, tout Juda et Benjamin. Il les compta depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, et il trouva qu'il y avait trois cent mille hommes d'élite, capables d'aller à la guerre, sachant manier la lance et le bouclier.
Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
6 Il loua aussi cent mille hommes vaillants d'Israël pour cent talents d'argent.
Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
7 Un homme de Dieu vint lui dire: « O roi, ne laisse pas l'armée d'Israël aller avec toi, car Yahvé n'est pas avec Israël, avec tous les enfants d'Ephraïm.
Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
8 Mais si tu veux y aller, agis, et sois fort pour la bataille. Dieu vous renversera devant l'ennemi, car Dieu a le pouvoir de secourir et de renverser. »
Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
9 Amatsia dit à l'homme de Dieu: « Mais que ferons-nous pour les cent talents que j'ai donnés à l'armée d'Israël? » L'homme de Dieu répondit: « Yahvé est capable de te donner beaucoup plus que cela. »
Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
10 Alors Amatsia sépara l'armée qui était venue à lui d'Ephraïm, pour la renvoyer chez elle. C'est pourquoi leur colère s'enflamma contre Juda, et ils retournèrent chez eux avec fureur.
Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
11 Amatsia prit courage, conduisit son peuple et alla dans la vallée du sel; il frappa dix mille hommes des fils de Séir.
Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
12 Les enfants de Juda en emportèrent dix mille vivants, les amenèrent au sommet du rocher et les jetèrent du haut du rocher, de sorte qu'ils furent tous brisés en morceaux.
Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
13 Mais les hommes de l'armée qu'Amatsia avait renvoyés pour ne pas aller avec lui au combat, tombèrent sur les villes de Juda, depuis Samarie jusqu'à Beth Horon, en battirent trois mille et firent un grand pillage.
Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
14 Après qu'Amatsia fut revenu du massacre des Édomites, il fit venir les dieux des fils de Séir et les érigea en dieux, il se prosterna devant eux et leur offrit des parfums.
Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
15 La colère de Yahvé s'enflamma contre Amatsia, et il lui envoya un prophète qui lui dit: « Pourquoi as-tu recherché les dieux de ces peuples qui n'ont pas délivré leur propre peuple de ta main? »
Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
16 Comme il parlait avec lui, le roi lui dit: « T'avons-nous fait un des conseillers du roi? Arrête! Pourquoi devrais-tu être frappé? » Le prophète s'arrêta et dit: « Je sais que Dieu a décidé de te détruire, parce que tu as fait cela et que tu n'as pas écouté mes conseils. »
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
17 Alors Amatsia, roi de Juda, consulta ses conseillers et envoya dire à Joas, fils de Joachaz, fils de Jéhu, roi d'Israël: « Viens! Regardons-nous en face. »
Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
18 Joas, roi d'Israël, envoya dire à Amatsia, roi de Juda: « Le chardon du Liban envoya dire au cèdre du Liban: « Donne ta fille pour femme à mon fils. Alors une bête sauvage qui était au Liban passa et piétina le chardon.
Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
19 Tu te dis que tu as frappé Édom, et ton cœur te pousse à te glorifier. Maintenant, reste chez toi. Pourquoi te mêler à la détresse, pour que tu tombes, toi et Juda avec toi? ».
Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
20 Mais Amatsia ne voulut pas écouter, car c'était Dieu qui voulait les livrer entre les mains de leurs ennemis, parce qu'ils avaient recherché les dieux d'Édom.
Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
21 Joas, roi d'Israël, monta, et lui et Amatsia, roi de Juda, se regardèrent en face à Beth Shemesh, qui appartient à Juda.
Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
22 Juda fut vaincu par Israël, et chacun s'enfuit dans sa tente.
Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
23 Joas, roi d'Israël, prit à Beth Shemesh Amatsia, roi de Juda, fils de Joas, fils de Joachaz, et l'amena à Jérusalem. Il abattit la muraille de Jérusalem depuis la porte d'Ephraïm jusqu'à la porte de l'angle, soit quatre cents coudées.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
24 Il prit tout l'or et l'argent, tous les objets qui se trouvaient dans la maison de Dieu avec Obed-Edom, les trésors de la maison du roi et les otages, et il retourna à Samarie.
Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
25 Amatsia, fils de Joas, roi de Juda, vécut quinze ans après la mort de Joas, fils de Joachaz, roi d'Israël.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
26 Le reste des actes d'Amatsia, les premiers et les derniers, ne sont-ils pas écrits dans le livre des rois de Juda et d'Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 Depuis qu'Amatsia s'est détourné de Yahvé, on a formé une conspiration contre lui à Jérusalem. Il s'enfuit à Lakis, mais ils le poursuivirent à Lakis et l'y tuèrent.
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28 On le fit monter sur des chevaux et on l'enterra avec ses pères dans la ville de Juda.
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.