< 2 Chroniques 22 >

1 Les habitants de Jérusalem firent régner à sa place Achazia, son plus jeune fils, car la bande d'hommes qui était venue au camp avec les Arabes avait tué tous les plus âgés. Ainsi régna Achazia, fils de Joram, roi de Juda.
Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Achazia avait quarante-deux ans lorsqu'il devint roi, et il régna un an à Jérusalem. Le nom de sa mère était Athalie, fille d'Omri.
Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
3 Il marchait aussi dans les voies de la maison d'Achab, car sa mère le conseillait dans sa méchanceté.
Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
4 Il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, comme la maison d'Achab, car ils furent ses conseillers après la mort de son père, pour le détruire.
Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
5 Il suivit aussi leurs conseils et alla avec Joram, fils d'Achab, roi d'Israël, à la guerre contre Hazaël, roi de Syrie, à Ramoth Galaad; et les Syriens blessèrent Joram.
Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
6 Il revint se faire guérir à Jizreel des blessures qu'on lui avait faites à Rama, lorsqu'il combattait Hazaël, roi de Syrie. Azaria, fils de Joram, roi de Juda, descendit voir Joram, fils d'Achab, à Jizreel, car il était malade.
saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
7 Or, la destruction d'Achazia fut le fait de Dieu, en ce qu'il alla vers Joram; car, quand il fut arrivé, il sortit avec Joram contre Jéhu, fils de Nimshi, que l'Éternel avait oint pour exterminer la maison d'Achab.
Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
8 Lorsque Jéhu exerçait son jugement sur la maison d'Achab, il trouva les princes de Juda et les fils des frères d'Achazia au service d'Achazia, et il les tua.
Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
9 Il chercha Achazia, et on l'attrapa (il se cachait maintenant à Samarie), on l'amena à Jéhu et on le tua; puis on l'enterra, car on disait: « C'est le fils de Josaphat, qui cherchait Yahvé de tout son cœur. » La maison d'Achazia n'avait plus le pouvoir de détenir le royaume.
Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
10 Et quand Athalie, mère d'Achazia, vit que son fils était mort, elle se leva et fit périr toute la race royale de la maison de Juda.
Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
11 Mais Joschabeath, fille du roi, prit Joas, fils d'Achazia, et le sauva furtivement du milieu des fils du roi qui avaient été tués, et le mit avec sa nourrice dans la chambre à coucher. Et Jéhoshabeath, fille du roi Joram, femme du prêtre Jehojada (car elle était la sœur d'Achazia), le cacha d'Athalie, afin qu'elle ne le tuât pas.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
12 Il resta avec eux, caché dans la maison de Dieu, six ans pendant qu'Athalie régnait sur le pays.
Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.

< 2 Chroniques 22 >