< 2 Chroniques 13 >

1 La dix-huitième année du roi Jéroboam, Abija commença à régner sur Juda.
A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
2 Il régna trois ans à Jérusalem. Sa mère s'appelait Micaia, fille d'Uriel, de Guibea. Il y eut une guerre entre Abija et Jéroboam.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
3 Abija se mit en campagne avec une armée de vaillants guerriers, quatre cent mille hommes d'élite, et Jéroboam se rangea en bataille contre lui avec huit cent mille hommes d'élite, qui étaient de vaillants guerriers.
Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
4 Abija se tint debout sur la montagne de Zemaraïm, qui est dans la montagne d'Ephraïm, et dit: « Écoute-moi, Jéroboam et tout Israël!
Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
5 Ne savez-vous pas que Yahvé, le Dieu d'Israël, a donné le royaume d'Israël à David pour toujours, à lui et à ses fils, par une alliance de sel?
Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
6 Mais Jéroboam, fils de Nebat, serviteur de Salomon, fils de David, se leva et se révolta contre son maître.
Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
7 Des hommes sans valeur se rassemblèrent auprès de lui, des méchants qui se fortifièrent contre Roboam, fils de Salomon, alors que Roboam était jeune et avait le cœur tendre, et qu'il ne put leur résister.
sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
8 « Maintenant, vous avez l'intention de résister au royaume de Yahvé entre les mains des fils de David. Vous êtes une grande multitude, et les veaux d'or que Jéroboam vous a faits pour dieux sont avec vous.
“Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
9 N'avez-vous pas chassé les prêtres de Yahvé, les fils d'Aaron et les Lévites, et ne vous êtes-vous pas fait des prêtres selon les coutumes des peuples d'autres pays? Celui qui vient se consacrer avec un jeune taureau et sept béliers peut être prêtre de ceux qui ne sont pas des dieux.
Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
10 « Quant à nous, Yahvé est notre Dieu, et nous ne l'avons pas abandonné. Nous avons des prêtres au service de Yahvé, les fils d'Aaron, et les Lévites à leur service.
“Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
11 Ils brûlent à Yahvé, chaque matin et chaque soir, des holocaustes et des parfums doux. Ils mettent aussi les pains de proposition en ordre sur la table pure, et prennent soin du chandelier d'or avec ses lampes, pour qu'elles brûlent chaque soir; car nous observons les instructions de l'Éternel, notre Dieu, mais vous l'avez abandonné.
Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
12 Voici, Dieu est avec nous à notre tête, et ses prêtres avec les trompettes d'alarme pour sonner l'alarme contre vous. Enfants d'Israël, ne luttez pas contre Yahvé, le Dieu de vos pères, car vous ne réussirez pas. »
Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
13 Mais Jéroboam fit dresser une embuscade derrière eux; ils étaient donc devant Juda, et l'embuscade était derrière eux.
To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
14 Lorsque Juda regarda en arrière, voici, la bataille était devant et derrière eux; ils crièrent à Yahvé, et les prêtres sonnèrent des trompettes.
Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
15 Alors les hommes de Juda poussèrent des cris de guerre. Comme les hommes de Juda criaient, Dieu frappa Jéroboam et tout Israël devant Abija et Juda.
mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
16 Les enfants d'Israël s'enfuirent devant Juda, et Dieu les livra entre leurs mains.
Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
17 Abija et son peuple leur firent subir une grande défaite, et cinq cent mille élus d'Israël tombèrent morts.
Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
18 C'est ainsi que les enfants d'Israël furent soumis en ce temps-là et que les enfants de Juda l'emportèrent, car ils s'en remettaient à Yahvé, le Dieu de leurs pères.
Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
19 Abija poursuivit Jéroboam et lui prit des villes: Béthel et ses villages, Jeshanah et ses villages, et Ephron et ses villages.
Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
20 Jéroboam ne recouvra pas ses forces du temps d'Abija. Yahvé le frappa, et il mourut.
Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
21 Mais Abija devint puissant et prit pour lui quatorze femmes, et il engendra vingt-deux fils et seize filles.
Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
22 Le reste des actes d'Abija, sa conduite et ses paroles sont écrits dans le commentaire du prophète Iddo.
Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.

< 2 Chroniques 13 >