< 2 Chroniques 12 >

1 Lorsque le royaume de Roboam fut établi et qu'il fut puissant, il abandonna la loi de l'Éternel, et tout Israël avec lui.
Bayan mulkin Rehobowam ya kahu kamar sarki ya kuma yi ƙarfi, shi da dukan Isra’ila suka yi biris da dokar Ubangiji.
2 La cinquième année du roi Roboam, Schischak, roi d'Égypte, monta contre Jérusalem, parce qu'ils avaient péché contre l'Éternel,
Domin sun yi rashin biyayya ga Ubangiji, saboda haka Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima a shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam.
3 avec douze cents chars et soixante mille cavaliers. Le peuple qui était venu d'Égypte avec lui était innombrable: les Lubim, les Sukkiim et les Éthiopiens.
Da kekunan yaƙi dubu ɗaya da ɗari biyu da kuma mahayan dawakai dubu haɗe da mayaƙan Libiyawa, Sukkatawa da kuma Kushawa waɗanda suka wuce ƙidaya suka zo tare da shi daga Masar,
4 Il prit les villes fortifiées qui appartenaient à Juda et vint à Jérusalem.
ya ci biranen katanga na Yahuda har zuwa Urushalima.
5 Le prophète Shemahia se rendit auprès de Roboam et des princes de Juda, qui s'étaient rassemblés à Jérusalem à cause de Shishak, et leur dit: « Yahvé dit: Vous m'avez abandonné, je vous laisse aussi entre les mains de Shishak ».
Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’”
6 Alors les princes d'Israël et le roi s'humilièrent, et ils dirent: « Yahvé est juste. »
Shugabannin Isra’ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”
7 Lorsque Yahvé vit qu'ils s'étaient humiliés, la parole de Yahvé parvint à Shemahia, en disant: « Ils se sont humiliés. Je ne les détruirai pas, mais je leur accorderai une certaine délivrance, et ma colère ne sera pas déversée sur Jérusalem par la main de Shishak.
Sa’ad da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai wannan maganar Ubangiji ta zo wa Shemahiya, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.
8 Néanmoins, ils seront ses serviteurs, afin qu'ils connaissent mon service et le service des royaumes des pays. »
Duk da haka za su zama bayinsa, don su san bambanci tsakanin yin mini bauta da kuma yin wa sarakunan sauran ƙasashe bauta.”
9 Shishak, roi d'Égypte, monta contre Jérusalem et enleva les trésors de la maison de Yahvé et les trésors de la maison du roi. Il emporta tout. Il emporta aussi les boucliers d'or que Salomon avait faits.
Da Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima, sai ya kwashi ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan sarki. Ya kwashe kome da kome, har da garkuwoyin zinariyar da Solomon ya yi.
10 Le roi Roboam fit à leur place des boucliers d'airain et les remit entre les mains des chefs des gardes, qui gardaient la porte de la maison du roi.
Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara na mashigin gidan sarki.
11 Chaque fois que le roi entrait dans la maison de Yahvé, la garde venait les porter, puis les ramenait dans la salle des gardes.
Duk sa’ad da sarki ya tafi haikalin Ubangiji, masu tsaron sukan tafi tare da shi, suna riƙe da garkuwoyi, daga baya kuma su mai da su a ɗakin tsaro.
12 Lorsqu'il s'humilia, la colère de Yahvé se détourna de lui, pour ne pas le détruire entièrement. En outre, on trouvait de bonnes choses en Juda.
Gama Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Ubangiji ya bar shi, ba a kuwa hallaka shi ƙaƙaf ba. Tabbatacce an yi’yan abubuwa masu kyau a Yahuda.
13 Et le roi Roboam se fortifia à Jérusalem et régna; car Roboam avait quarante et un ans quand il commença à régner, et il régna dix-sept ans à Jérusalem, la ville que l'Éternel avait choisie parmi toutes les tribus d'Israël pour y mettre son nom. Le nom de sa mère était Naama, l'Ammonite.
Sarki Rehobowam ya kafa kansa daram a Urushalima, ya kuma ci gaba a matsayin sarki. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila wanda zai sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama ce, ita mutuniyar Ammon ce.
14 Il fit ce qui est mal, car il ne mit pas son cœur à chercher l'Éternel.
Ya aikata mugunta domin bai sa zuciyarsa ga neman Ubangiji ba.
15 Or les actes de Roboam, les premiers et les derniers, ne sont-ils pas écrits dans les récits du prophète Shemahia et du voyant Iddo, dans les généalogies? Il y eut continuellement des guerres entre Roboam et Jéroboam.
Game da ayyukan mulkin Rehobowam, daga farko zuwa ƙarshe, ba a rubuce suke a tarihin Shemahiya annabi da Iddo mai gani wanda yake zancen zuriyoyi ba? Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
16 Roboam se coucha avec ses pères et fut enterré dans la ville de David; et Abija, son fils, régna à sa place.
Rehobowam ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Abiya ɗansa kuma ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Chroniques 12 >