< 2 Chroniques 10 >

1 Roboam se rendit à Sichem, car tout Israël était venu à Sichem pour le faire roi.
Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ilawa sun je can don su naɗa shi sarki.
2 Lorsque Jéroboam, fils de Nebath, en eut connaissance (car il était en Égypte, où il avait fui la présence du roi Salomon), il revint d'Égypte.
Da Yerobowam ɗan Nebat ya ji wannan (a lokacin yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon ya tafi), sai ya dawo daga Masar.
3 On l'envoya appeler. Jéroboam et tout Israël vinrent, et ils parlèrent à Roboam en disant:
Saboda haka suka aika a zo da Yerobowam, sai shi da dukan Isra’ila suka je wurin Rehobowam suka ce masa.
4 « Ton père a rendu notre joug pénible. Maintenant, allège le service pénible de ton père et le lourd joug qu'il nous a imposé, et nous te servirons. »
“Mahaifinka ya sa mana kaya masu nauyi a kanmu, amma yanzu ka sauƙaƙa mana aiki mai zafin nan da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
5 Il leur dit: « Revenez me voir après trois jours. » Alors les gens sont partis.
Rehobowam ya amsa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.” Saboda haka mutanen suka watse.
6 Le roi Roboam consulta les vieillards qui s'étaient présentés devant Salomon, son père, de son vivant, en disant: « Quel conseil me donnez-vous sur la manière de répondre à ce peuple? »
Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawan da suka yi wa mahaifinsa Solomon hidima a lokacin da yake da rai, ya tambaye suya ce, “Wace shawara za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
7 Ils lui parlaient ainsi: « Si tu es gentil avec ces gens, si tu leur fais plaisir et si tu leur dis de bonnes paroles, alors ils seront tes serviteurs pour toujours. »
Suka amsa suka ce, “In za ka ji tausayi waɗannan mutane ka kuma gamshe su, ka kuma ba su amsar da ta dace, kullum za su zama bayinka.”
8 Mais il abandonna le conseil des vieillards qu'ils lui avaient donné, et tint conseil avec les jeunes gens qui avaient grandi avec lui, et qui se tenaient devant lui.
Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawa suka ba shi ya kuma nemi shawarar matasan da suka yi girma tare, suke kuma yin masa hidima.
9 Il leur dit: « Quel conseil donnez-vous, pour que nous puissions répondre à ces gens qui m'ont dit: « Allègez le joug que votre père a mis sur nous. »
Ya tambaye su ya ce, “Mece ce shawararku? Yaya zan amsa wa waɗannan mutanen da suke ce mini, ‘Ka sauƙaƙa nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
10 Les jeunes gens qui avaient grandi avec lui lui parlèrent ainsi: « Ainsi tu diras au peuple qui t'a parlé: « Ton père a rendu notre joug pesant, mais allège-le pour nous »; ainsi tu leur diras: « Mon petit doigt est plus gros que la taille de mon père ».
Matasan da suka yi girma tare shi suka amsa, “Faɗa wa mutanen da suke ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sauƙaƙa nauyinmu.’ Ka faɗa musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun mahaifina kauri.
11 Maintenant, alors que mon père vous a chargés d'un lourd joug, je vais ajouter à votre joug. Mon père vous a châtiés avec des fouets, mais moi, je vous châtierai avec des scorpions.'"
Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; zan ma sa mafi nauyi. Mahaifina ya bulale ku da bulala; zan bulale ku da kunamai.’”
12 Jéroboam et tout le peuple se présentèrent à Roboam le troisième jour, comme le roi le leur avait demandé, en disant: « Revenez me voir le troisième jour. »
Bayan kwana uku sai Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam, yadda sarki ya ce, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
13 Le roi leur répondit durement; et le roi Roboam abandonna le conseil des anciens,
Sarki ya amsa musu da kakkausar murya. Ya ƙi shawarar dattawan,
14 et leur parla selon le conseil des jeunes gens, en disant: « Mon père a rendu votre joug pesant, mais j'y ajouterai. Mon père vous a châtiés avec des fouets, mais je vous châtierai avec des scorpions. »
ya kuma bi shawarar matasan ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; zan ma sa mafi nauyi. Mahaifina ya bulale ku da bulala; zan bulale ku da kunamai.”
15 Et le roi n'écouta pas le peuple, car cela venait de Dieu, afin que l'Éternel affermît sa parole, qu'il avait dite par Achija, le Silonite, à Jéroboam, fils de Nebat.
Saboda haka sarki bai saurari mutane ba, gama wannan juyin al’amura daga Allah ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi ga Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya mutumin Shilo.
16 Lorsque tout Israël vit que le roi ne les écoutait pas, le peuple prit la parole et dit au roi: « Quelle part avons-nous en David? Nous n'avons pas d'héritage dans le fils de Jessé! Chacun dans sa tente, Israël! Occupe-toi maintenant de ta propre maison, David. » Et tout Israël s'en alla dans ses tentes.
Sa’ad da Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, suka ce, “Wanda rabo muke da shi a wurin Dawuda, wanda sashe muke da shi daga ɗan Yesse? Kowa yă koma tentinsa, ya Isra’ila! Ka lura da gidanka, ya Dawuda!” Saboda haka dukan Isra’ilawa suka tafi gida.
17 Mais quant aux enfants d'Israël qui habitaient dans les villes de Juda, Roboam régnait sur eux.
Amma game da Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da yin mulki a bisansu.
18 Alors le roi Roboam envoya Hadoram, qui était à la tête des hommes soumis au travail forcé, et les enfants d'Israël le lapidèrent à mort. Le roi Roboam se hâta de monter sur son char, pour s'enfuir à Jérusalem.
Sarki Rehobowam ya aiki Hadoram wanda yake lura da aikin dole, amma Isra’ilawa suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu. Sarki Rehobowam kuwa ya gaggauta ya shiga keken yaƙinsa ya gudu zuwa Urushalima.
19 Ainsi, Israël s'est rebellé contre la maison de David jusqu'à ce jour.
Ta haka Isra’ila ya kasance cikin tawaye a kan gidan Dawuda har yă zuwa wannan rana.

< 2 Chroniques 10 >