< 1 Samuel 8 >

1 Lorsque Samuel fut âgé, il établit ses fils comme juges sur Israël.
Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
2 Or le nom de son premier-né était Joël, et le nom de son second, Abija. Ils étaient juges à Beersheba.
Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
3 Ses fils ne marchèrent pas dans ses voies, mais se détournèrent vers des gains malhonnêtes, acceptèrent des pots-de-vin et pervertirent la justice.
Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
4 Alors tous les anciens d'Israël se rassemblèrent et vinrent trouver Samuel à Rama.
Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
5 Ils lui dirent: « Voici, tu es vieux, et tes fils ne marchent pas dans tes voies. Maintenant, fais-nous un roi pour nous juger comme toutes les nations. »
Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
6 Mais ce qui déplut à Samuel, c'est qu'ils dirent: « Donne-nous un roi pour nous juger. » Samuel pria Yahvé.
Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
7 Yahvé dit à Samuel: « Écoute la voix du peuple dans tout ce qu'il te dira, car ce n'est pas toi qu'il a rejeté, mais c'est moi qu'il a rejeté comme roi sur lui.
Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
8 Ils ont fait tout ce qu'ils ont fait depuis le jour où je les ai fait monter d'Égypte jusqu'à ce jour, en m'abandonnant et en servant d'autres dieux, et ils te feront de même.
Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
9 Maintenant donc, écoutez leur voix. Cependant, tu protesteras solennellement auprès d'eux, et tu leur indiqueras la voie du roi qui régnera sur eux. »
Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
10 Samuel rapporta toutes les paroles de Yahvé au peuple qui lui demandait un roi.
Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
11 Il dit: « Voici comment agira le roi qui régnera sur vous: il prendra vos fils et les mettra à son service, pour ses chars et pour être ses cavaliers; et ils courront devant ses chars.
Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
12 Il les nommera chefs de milliers et chefs de cinquantaines, et il en chargera de labourer son sol et de moissonner sa récolte, de fabriquer ses instruments de guerre et les instruments de ses chars.
Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
13 Il prendra tes filles pour en faire des parfumeuses, des cuisinières et des boulangères.
Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
14 Il prendra tes champs, tes vignes et tes oliviers, même tes meilleurs, et les donnera à ses serviteurs.
Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
15 Il prendra le dixième de tes semences et de tes vignes, et le donnera à ses officiers et à ses serviteurs.
Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
16 Il prendra tes serviteurs, tes servantes, tes meilleurs jeunes gens et tes ânes, et les affectera à son propre travail.
Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
17 Il prendra le dixième de vos troupeaux, et vous serez ses esclaves.
Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
18 Vous crierez en ce jour-là à cause de votre roi que vous vous serez choisi, et Yahvé ne vous répondra pas en ce jour-là. »
Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
19 Mais le peuple refusa d'écouter la voix de Samuel, et ils dirent: « Non, mais nous aurons un roi sur nous,
Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
20 afin que nous soyons aussi comme toutes les nations, et que notre roi nous juge, qu'il sorte devant nous et qu'il mène nos combats. »
Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
21 Samuel entendit toutes les paroles du peuple, et il les répéta aux oreilles de l'Éternel.
Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
22 Yahvé dit à Samuel: « Écoute leur voix, et fais-leur un roi. » Samuel dit aux hommes d'Israël: « Retournez chacun dans votre ville. »
Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”

< 1 Samuel 8 >